Hamas ta ce a shirye take ta sako dukkan fursunonin Isra’ila da suka rage, domin musanya fursunoni”
Published: 14th, April 2025 GMT
Wani babban jami’in Hamas ya ce kungiyar a shirye take ta sako dukkan fursunonin Isra’ila da suka rage a zirin Gaza da aka yi wa kawanya, domin musanya abin da ya bayyana da ” fursunoni” da kuma tabbatar da kawo karshen yakin kisan kare dangi da ake ci gaba da yi.
Kamfanin dillancin labaran AFP ya nakalto Taher al-Nunu na cewa: “A shirye muke mu sako dukkan ‘yan Isra’ila da ake tsare da su a yarjejeniyar musayar fursunoni, da kawo karshen yakin, da janyewar sojojin Isra’ila daga zirin Gaza da shigar da kayan agajin jin kai.
A halin yanzu Hamas na tattaunawa a birnin Alkahira tare da masu shiga tsakani na Masar da Qatar.
Saidai, duk da haka, jami’in na Hamas ya caccaki Isra’ila saboda hana ci gaban da aka samu wajen tsagaita wuta.
A wani labarin kuma Akwai rahotannin da ke cewa Washington za ta yi matsin lamba kan gwamnatin Tel Aviv ta amince da wata sabuwar shawara kan tsagaita wuta a Gaza.
A ranar 18 ga watan Maris ne sojojin kasar Isra’ila suka kaddamar da wani harin ba-zata a zirin Gaza, inda suka kashe daruruwan mutane, tare da jikkata wasu da dama, tare da wargaza yarjejeniyar tsagaita bude wuta da kungiyar Hamas ta Falasdinu, da yarjejeniyar musayar fursunoni.
A cewar ma’aikatar lafiya a Gaza, akalla Falasdinawa 50,983 aka kashe, akasari mata da kananan yara, tun daga ranar 7 ga Oktoba, 2023.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Isra ila da
এছাড়াও পড়ুন:
Rashin wutar lantarki ya durƙusar da kasuwanci a Arewa Maso Gabas
Rashin wutar lantarki a Arewa maso Gabashin Najeriya ya tilasta wa jama’a da ’yan kasuwa zaman ɗari-ɗari da asarar dukiya, sakamakon aikin da Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Ƙasa (TCN), ke yi na aikin sabbin turakun wutar lantarki.
Rashin wutar, wanda ya fara daga ranar 10 zuwa 14 ga watan Yuni, ya shafi layin wutar lantarki na Jos–Bauchi–Gombe mai ƙarfin 132kV.
An kashe mutum 41 cikin mako ɗaya a Filato Hajjin 2025: Jihohi 11 sun kashe N6.2bn wajen tallafa wa AlhazaiA Jihar Adamawa, musamman a birnin Yola, jama’a na cikin matsanancin hali.
Hajiya Aisha Babangida daga Jimeta, ta ce rashin wutar ya tilasta masa soye dukkanin naman ragon sallarta domin babu wutar da za ta ajiye shi a firinji.
“Na fi son dafawa, amma dole na soya gaba ɗaya. Wannan matsala ta wuta ta zo ne a lokacin da ake buƙatar wutar,” in ji ta.
Kasuwanci da harkokin yau da kullum sun tsaya cak a wurare da dama.
Adamu Abubakar, mai sayar da lemun kwalba a kasuwar Jimeta, ya koka da cewa rashin sanyin ruwa ya rage masa yawan kwastomomi.
“Mutane na so ruwan sanyi, amma ba zan iya samun mai sanyi ba. Ina amfani da ƙanƙara ne yanzu don na ci gaba da kasuwancina,” in ji shi.
Muhammad Zaharaddeen, wani barber mai shagon aski a Bauchi, ya ce kasuwancinsa ya durƙushe sakamakon rashin wutar lantarki.
“Shagona na buƙatar wutar lantarki sosai. Ko da na kunna janareta, farashin mai ya tashi fiye da yadda mutane ke biya a baya,” in ji shi.
“Da ba don wani ɗan kasuwanci da nake yi a gefe ba, da ko abinci ba zan iya siya ba.”
A Jalingo, babban birnin Jihar Taraba, asibitoci da ƙananan ‘yan kasuwa na kokawa kan hauhawar kuɗin aiki.
Asibitin Federal Medical Centre ya koma amfani da janareta, wanda hakan ke sa wa ana biyan maƙudan kuɗaɗe wajen zuba man fetur.
“An daɗe da yanke wutarmu, yanzu da aka dawo mana da ita, sai kuma ga wannan matsalar. Duk manyan na’urorinmu suna amfani ne da dizal,” in ji Dokta Aisha Adamu Sani, daraktar asibitin.
Masu niƙa, masu walda da masu ɗinki a Jalingo sun dakatar da aiki.
Mallam Haruna Garba, wanda ke da injin niƙa, ya ce ya rufe shagonsa gaba ɗaya.
“Ba zan iya niƙa babu wutar lantarki ba. Man fetur ya yi tsada sosai. Na rufe kasuwancina na ɗan lokaci,” in ji shi.
A Damaturu, babban birnin Jihar Yobe, al’umma na fama da ƙarancin ruwa da hauhawar farashin ruwan sanyi da kayan masarufi.
Musa Adamu, mai sayar da lemu, ya ce: “Babu wuta, babu sanyi. Dole na ɗan kara farashi, amma ya kamata jama’a su fahimtci rayuwar da ake ciki,” in ji shi.
Masu ƙananan sana’o’i irin su Yusuf Bukar, wani masassaƙa a Damaturu, na kashe dubban Naira kullum wajen siyan mai domin kammala ayyukansu.
“Idan wannan hali ya ci gaba, zan rasa kwastomomina. Na kashe Naira 10,000 a jiya kacal a kan mai,” in ji shi cikin baƙin ciki.
TCN ta bayyana cewa katse wutar na da matuƙar muhimmanci domin kammala gina sabbin turakun wuta masu ƙarfin 330kV domin inganta tsarin samar da wutar a yankin.
Kakakin TCN, Ndidi Mbah, ta ce turakun za su zama mafita daga yawan katsewar wuta a gaba.
“Da zarar an kammala aikin, za a iya amfani da layin Bauchi da Gombe. Jos ma za ta iya riƙa kai wa Bauchi wuta kai-tsaye,” in ji ta.
Sai dai masana sun ɗora alhakin matsalar kan rashin wata hanya da za ake samar wa Arewa maso Gabas wuta.
Wani tsohon ma’aikacin TCN da ya nemi a sakaya sunansa ya ce: “Idan layin Jos-Bauchi-Gombe ya faɗi, kowa zai tsunduma cikin duhu. Ya kamata a ce an gina wata hanya ta biyu tun da daɗewa.”
Wannan ba shi ne karon farko da yankin ke faɗawa cikin duhu ba.
A baya, wasu da ba a san ko su waye ba sun lalata turakun wuta da bam, wanda ya sa aka ɗauke wuta gaba ɗaya a Arewa maso Gabas.
Sai dai wannan katsewar wutar wata hujja ce ta gaggawar sake fasalin tsarin wutar lantarki a yankin.