Wani babban jami’in Hamas ya ce kungiyar a shirye take ta sako dukkan fursunonin Isra’ila da suka rage a zirin Gaza da aka yi wa kawanya, domin musanya abin da ya bayyana da ” fursunoni” da kuma tabbatar da kawo karshen yakin kisan kare dangi da ake ci gaba da yi.

Kamfanin dillancin labaran AFP ya nakalto Taher al-Nunu na cewa: “A shirye muke mu sako dukkan ‘yan Isra’ila da ake tsare da su a yarjejeniyar musayar fursunoni, da kawo karshen yakin, da janyewar sojojin Isra’ila daga zirin Gaza da shigar da kayan agajin jin kai.

A halin yanzu Hamas na tattaunawa a birnin Alkahira tare da masu shiga tsakani na Masar da Qatar.

Saidai, duk da haka, jami’in na Hamas ya caccaki Isra’ila saboda hana ci gaban da aka samu wajen tsagaita wuta.

A wani labarin kuma Akwai rahotannin da ke cewa Washington za ta yi matsin lamba kan gwamnatin Tel Aviv ta amince da wata sabuwar shawara kan tsagaita wuta a Gaza.

A ranar 18 ga watan Maris ne sojojin kasar Isra’ila suka kaddamar da wani harin ba-zata a zirin Gaza, inda suka kashe daruruwan mutane, tare da jikkata wasu da dama, tare da wargaza yarjejeniyar tsagaita bude wuta da kungiyar Hamas ta Falasdinu, da yarjejeniyar musayar fursunoni.

A cewar ma’aikatar lafiya a Gaza, akalla Falasdinawa 50,983 aka kashe, akasari mata da kananan yara, tun daga ranar 7 ga Oktoba, 2023.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Isra ila da

এছাড়াও পড়ুন:

Taron Ashura Ya Zama Lamari Mafi Girma Da Cinkoson Jama’a, Inda Masu Ziyara Daga Sassan Duniya Suka Isa Karbala

Gangamin Ashura ya zama lamarin mafi girma da cunkoson jama’a inda tattakiin Tuwairij yake gudana tare da faɗaɗa da ba a taɓa ganin irinsa ba

Tattakin Tuwairij na bana zuwa birnin Karbala na fuskantar hallara da cunkoson jama’a da ba a taba ganin irinsa ba, inda dimbin masu ziyara  daga sassan duniya ke tururuwa zuwa hubbaren Imam Husaini da kuma titunan da ke kewaye.

Mai ba da shawara ga babban sakataren cibiyar Hubbaren Imam Husain {a.s} Fadel Oz a cikin wata sanarwa da ya aikewa kafafen watsa labarai ya bayyana cewa: “A shirye-shiryen wannan juyayi, babban Sakatariyar Haramin Imam Husain (a.s) da haramin Abbas sun samar da dukkan sharuddan da suka dace don kula da masu ziyara da kuma tabbatar da jin dadinsu.

Ya kara da cewa, “Yankin da aka kebe domin gudanar da juyayin Ashura  ya samu gagarumin ci gabata hanyar fadada shi, domin a shekarun da suka gabata ana ci gaba da gudanar da ayyukan da suka yi na mallakar wuraren da ke kewaye da fadada titunan da ke zuwa gare su da nufin daukar saukaka wa masu halartar taron.

Oz ya ci gaba da cewa “Hukumar ayyuka, ‘yan sanda, sassan jami’ai, da kuma cibiyoyin gwamnati sun kuma taka rawar gani wajen hada kai don tabbatar da gudanar da juyayin Ashura cikin kwanciyar hankali da lumana.”

Ya bayyana cewa, “wannan hadin gwiwa yana nuna irin kishin da hukumomin da abin ya shafa suke da shi wajen tabbatar da nasarar gudanar da juyayin Ashura a cikin yanayi na musamman na ruhi,” yana mai jaddada cewa “wadannan fadadawa da shirye-shirye suna tafiya tare da ci gaba da karuwar masu ziyara da kuma tabbatar da samun kwarewa da kwanciyar hankali a wannan babban taron addini.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka Tana Fatan HKI da Hamas Su Tsaida Budewa Juna Wuta Na Kwanaki 60 A Karshen Wannan makon
  • ‘Yan Gwagwarmayar Falasdinu Sun Halaka Sojojin Mamaya Biyar Tare Da Jikkata Wasu Goma Na Daban
  • Kakakin Rundunar Izzuddeen Qassam ya Bayyana Yadda Suka Yi Kofar Rago Ga Sojojin Mamayar Isra’ila
  • Falasdinawa 13 Ne Suka Yi Shahada Wasu Da Dama Suka Jikkata A Hare-Haren Sojojin Mamayar Isra’ila A Gaza
  • TCN Ta Wayar Da Kan Al’ummomin Kaduna Kan Illar Lalata Kayan Wuta Da Gini Karkashen Babbar Wayar Wuta 
  • Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%
  • Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Manya Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%
  • Jami’an Leken Asirin “Shabak” Na Isra’ila Sun Kama Nasir Lahham Na Tashar Talabijin din Almayadin
  • Fursunoni 58 Na Rubuta Jarabawar NECO A Kano
  • Taron Ashura Ya Zama Lamari Mafi Girma Da Cinkoson Jama’a, Inda Masu Ziyara Daga Sassan Duniya Suka Isa Karbala