Tsoffin Ma’aikatan Hukumar Leken Asiri HKI Mosad Sun Shiga Cikin Masu Kiran A Kawo Karshen Yaki Da Gaza
Published: 14th, April 2025 GMT
A daidai lokacin da ake ci gaba da takaddama a HKI dangane da wasikar da wasu sojojin sama su ka rubuta na sukar yakin Gaza, wasu tsoffin ma’aikatar hukumar leken asiri ta “Mosad” sun bi sawunhu.
Kafafen watsa labarum HKI sun ambaci cewa, fiye da tsoffin jami’an leken asirin kungiyar MOSAD 200 ne su ka rattaba hannu akan wata takarda suna nuna goyon bayansu da sojan sama da su ka yi kira a kawo karshen yakin Gaza.
Kwanaki kadan da su ka gabata, tashar talabijin din Channel 13; ta watsa labarin da yake cewa; Wasu ma’aikatar rundunar leken asiri ta soja sun shiga cikin masu kira da a kawo karshen yakin na Gaza da kuma dawo da fursunoni daga can.
An kuma samu irin wannan halayyar ta yin kira a kawo karshen yakin a tsakanin likitocin soja su 100 sai kuma malaman jami’a su ma daruruwa.
Kiraye-kirayen da sojojii suke yi a HKI da na kwo karshen yakin Gaza da mayar da fursunonin yaki, ya bude wata sabuwar takaddama a tsakanin ‘yan siyasa.
Wasikar ta bude jayayya a tsakanin ‘yan sahayoniya akan cewa, Netanyahu yana ci gaba da yin yaki ne saboda maslahar kashin kansa.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: karshen yakin
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnan Zamfara Ya Raba Buhunan Taki 59,205 Ga Manoman Jihar
Sanarwar ta ƙara da cewa, sauran kayayyakin da aka raba sun haɗa da irin shinkafa kilogiram 34,800, irin masara kilogiram 80,000, da lita 23,740 na maganin ciyawa, lita 11,735 na maganin kwari, da buhunan sinadarai na gyaran iri 23,470.
A yayin jawabin maddamarwar, Gwamna Lawal ya bayyana cewa rabon takin zamani kyauta na nuni da yadda gwamnatinsa ke ƙoƙarin kawo sauyi a jihar Zamfara ta hanyar noma mai ɗorewa da bunƙasa karkara.
Ya ce, “Aikin noma shi ne ginshiƙin tattalin arzikin jiharmu, ba sashe kaɗai ba ne, amma asalin al’ummarmu ne.
“Gwamnatinmu ta rungumi taken ‘noma abin alfaharinmu ne’. Noma na nuna ainihin ko su wane ne mu da kuma abin da ya kamata mu ba da fifiko a matsayinmu na al’umma, sama da kashi 85 na al’ummarmu sun dogara ne kan noma don rayuwa. Haƙƙin ne a kan mu, kuma haƙiƙa ya zama wajibi mu ba su goyon baya da ƙarfafa su.
“Wannan gwamnatin tana kallon noma a matsayin dabarar samar da abinci, samar da ayyukan yi, rage fatara, da bunƙasar tattalin arzikin ƙasa baki ɗaya, shi ya sa muke aiwatar da shirin kawo sauyi a fannin noma, wanda ya dace da buƙatun al’ummominmu da kuma yin daidai da manufar ci gaba mai ɗorewa ta 2, wanda ke neman kawo ƙarshen yunwa, inganta abinci mai gina jiki, da bunƙasa noma mai ɗorewa.
“Duk da ƙalubalen sauyin yanayi da kuma ƙarshen lokacin damina na 2025, mun ci gaba da mai da hankali sosai, gwamnatinmu tana tallafa wa manoma da kayan aikin da ake buƙata don bunƙasa noma da samun kuɗin shiga, muna saka hannun jari a fannin samar da iri, takin zamani, fasaha, da jarin bil’adama don samun tasiri na dogon lokaci.
“Manufarmu ta haɗa da ƙarfafa mata, matasa, da kuma ɗaiɗaikun mutane masu buƙatu na musamman a matsayin wakilai na kawo sauyi, ba wai mahalarta kaɗai ba. Mun bullo da ingantaccen tsarin rabo cikin gaskiya don tabbatar da cewa tallafin ya isa ga manoman da suka dace a daidai lokacin da ya dace.
“Mun gane cewa manoma na fuskantar matsaloli kamar rashin damar samun kayan aiki, kuɗaɗe, rashin tabbas na kasuwa, asarar bayan girbi, da kuma tasirin sauyin yanayi. Amma muna tunkarar waɗannan batutuwa.
“Ta hanyar shiga tsakani, muna gina tsarin da zai taimaka wa manomanmu daga shuka har zuwa bayan girbi. Muna haɓaka noma da injinan zamani.
“Bari na dan ɗauki lokaci in yi magana kai tsaye ga waɗanda suka ci gajiyar shirin na bana. Waɗannan kayayyakin ba na sayarwa be ne. Ba kayayyakin da za a yi ciniki da su ba ne domin a samu ci gaba cikin gaggawa. Kayan aiki ne na samar da ci gaba, zuba jari a nan gaba da kuma makomar Zamfara. Ku yi amfani da su cikin hikima, ku yi amfani da su cikin gaskiya, ku bar su su zama ginshiƙi na ƙaruwar girbi da inganta rayuwa.
“Baƙin alfarma, ’yan uwa maza da mata, yanzu ya zama abin alfaharina na ƙaddamar da shirin Rarraba Kayayyakin Aikin Noma na 2025 a hukumance, wanda zai amfani ƙananan manoma 59,205 a faɗin jihar mu.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp