Tsoffin Ma’aikatan Hukumar Leken Asiri HKI Mosad Sun Shiga Cikin Masu Kiran A Kawo Karshen Yaki Da Gaza
Published: 14th, April 2025 GMT
A daidai lokacin da ake ci gaba da takaddama a HKI dangane da wasikar da wasu sojojin sama su ka rubuta na sukar yakin Gaza, wasu tsoffin ma’aikatar hukumar leken asiri ta “Mosad” sun bi sawunhu.
Kafafen watsa labarum HKI sun ambaci cewa, fiye da tsoffin jami’an leken asirin kungiyar MOSAD 200 ne su ka rattaba hannu akan wata takarda suna nuna goyon bayansu da sojan sama da su ka yi kira a kawo karshen yakin Gaza.
Kwanaki kadan da su ka gabata, tashar talabijin din Channel 13; ta watsa labarin da yake cewa; Wasu ma’aikatar rundunar leken asiri ta soja sun shiga cikin masu kira da a kawo karshen yakin na Gaza da kuma dawo da fursunoni daga can.
An kuma samu irin wannan halayyar ta yin kira a kawo karshen yakin a tsakanin likitocin soja su 100 sai kuma malaman jami’a su ma daruruwa.
Kiraye-kirayen da sojojii suke yi a HKI da na kwo karshen yakin Gaza da mayar da fursunonin yaki, ya bude wata sabuwar takaddama a tsakanin ‘yan siyasa.
Wasikar ta bude jayayya a tsakanin ‘yan sahayoniya akan cewa, Netanyahu yana ci gaba da yin yaki ne saboda maslahar kashin kansa.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: karshen yakin
এছাড়াও পড়ুন:
Syria: Sojojin “Isra’ila” Sun Kutsa Cikin Yankin Qunaidhara
Motocin sojan Haramtacciyyar Kasar Isra’ila 10 sun kutsa cikin yankin Qunaidhara na kasar Syria, da safiyar yau Asabar, tare da kafa wasu wuraren bincike akan hanya.
Kungiyar kare hakkin bil’adama na kasar Syria “Mirsad” ya ce, sojojin mmayar sun rika kutsawa cikin gidajen mutane a yankin suna bincike, sai dai babu bayani akan ko sun kama mutanen da su ka shiga cikin gidajensu.
Kungiyar kare hakkin bil’adaman ta kasar Syria ta kuma amabci yadda sojojin mamayar su ka gabatar da mutanen yankin taimakon kayan agaji,amma su ka ki karba.
A jiya Juma’a ma dai sojojin mamayar “Isra’ila” sun kutsa cikin garuruwa da dama da suke a yankin da ake kira na tsagaita wutar yakin karshe tsakanin ‘yan sahayoniyar da Syria a 1976.
Motocin soja guda 4 ne su ka shiga cikin kauyukan Biriqah, da Bi’irul-Ajam, da suke a kusa da Qunaidhara ta tsakiya. Daga can kuma su ka nausa zuwa Qunaidarah ta kudu.
Haramtacciyar Kasar Isra’ila dai tana yin kutse a cikin kasar Syria a duk lokacin da ta ga dama, duk da cewa gwamnatin Damascuss mai ci ba ta gaba da ita.
Bugu da kari, sojojin Haramtacciyar Kasar Isra’ila sun rusa mafi yawancin makaman Syria, na sama, kasa da kuma na ruwa, bayan kifar da gwamantin Basshar Asad a shekarar da ta gabata.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kalibaf: Iran Da Habasha Suna Bunkasa Alakokin Siyasa Da Tattalin Arziki December 13, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 171 December 13, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 170 December 13, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 169 December 13, 2025 Isra’ila Ta Kai Hari A Kudancin Labanon A Ci Gaba Da Keta Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta December 13, 2025 Ziyarar Da Shugaban Rasha Ya Kai Indiya Ta Kara Karfafa Dangantakar Mosko Da Delhi December 13, 2025 Amurka Ta Sanya Sabbin Takunkumi A Bangaren Manfetur Na Venuzuela December 13, 2025 Hamas Ta Ce Ci Gaba Da Kai Hare-Haren Isra’ila Ya Nuna Gazawar Tsarin Duniya Na Dakatar Da Ita. December 13, 2025 Matatar Mai ta Dangote Ta Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 699 December 13, 2025 Iran da Rasha sun jaddada aiwatar da yarjejeniyar hadin gwiwa a tsakaninsu December 13, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci