Tsoffin Ma’aikatan Hukumar Leken Asiri HKI Mosad Sun Shiga Cikin Masu Kiran A Kawo Karshen Yaki Da Gaza
Published: 14th, April 2025 GMT
A daidai lokacin da ake ci gaba da takaddama a HKI dangane da wasikar da wasu sojojin sama su ka rubuta na sukar yakin Gaza, wasu tsoffin ma’aikatar hukumar leken asiri ta “Mosad” sun bi sawunhu.
Kafafen watsa labarum HKI sun ambaci cewa, fiye da tsoffin jami’an leken asirin kungiyar MOSAD 200 ne su ka rattaba hannu akan wata takarda suna nuna goyon bayansu da sojan sama da su ka yi kira a kawo karshen yakin Gaza.
Kwanaki kadan da su ka gabata, tashar talabijin din Channel 13; ta watsa labarin da yake cewa; Wasu ma’aikatar rundunar leken asiri ta soja sun shiga cikin masu kira da a kawo karshen yakin na Gaza da kuma dawo da fursunoni daga can.
An kuma samu irin wannan halayyar ta yin kira a kawo karshen yakin a tsakanin likitocin soja su 100 sai kuma malaman jami’a su ma daruruwa.
Kiraye-kirayen da sojojii suke yi a HKI da na kwo karshen yakin Gaza da mayar da fursunonin yaki, ya bude wata sabuwar takaddama a tsakanin ‘yan siyasa.
Wasikar ta bude jayayya a tsakanin ‘yan sahayoniya akan cewa, Netanyahu yana ci gaba da yin yaki ne saboda maslahar kashin kansa.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: karshen yakin
এছাড়াও পড়ুন:
IRGC: Makaman Iran Sun Fada Kan Matatan Man Haifa Har Sau Biyu A Yakin Kwanaki 12
Dakarun kare juyin juya halin musulunci na kasar Iran ya bayyana cewa makamai masu linzamu na dakarun sun fada kan matatar man fetur na Haifa a HKI har sau biyu a yakin kwanaki 12 da ta fafata da Iran a cikin watan Yunin wannan shekara.
Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Burgediya Janar Ali Mohammad Naeini kakakin dakarun ya na fadar haka a jiya Lahadi a wani taro, ya kuma kara da cewa makaman har’ila yau sun kashe jami’an hukumar leken asirin HKI MOSAD har 36 a wani hari kan ginin hukumar a cikin yakin.
Naeini, ya kara da cewa HKI ta yi kuskuren lissafi a lokacinda ta farwa kasar Iran da yaki a cikin watan Yunin da ya gabata, tare da tsammanin cewa JMI ba zata iya maida martani ba, saboda rauni, don an kashe manya-manyan kwamandojin sojojin kasar sannan ba zata iya amfani da makamanta na kare dangi ba.
A ranar 13 ga watan Yuni na wannan shekara ne HKI tare da Amurka suka farwa kasar Iran da yaki, da nufin kifar da gwamnatin kasar da kuma kawo karshen shirinta na makamashin nukliya kwata-kwata. Saboda haka ne jiragen yakin Amurka samfurin B2 suka kai hare-hare kan cibiyoyin makamashin Nukliya na kasar dake Fordo, Natanz da kuma Esfahan.
Naeni ya cewa Iran ta cilla makamai masu linzami har 14 kan sansanin sojojin Amurka mafi girma na Al-Udaid da ke kasar Qatar, sannan yace bisa lissafin Amurkawa kan su sun kashe dalar Amurka miliyon 111 wajen bibiyan inda makaman iran zasu fada.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Najeriya: Gwamnatin Tarayya Ta Bada Sanarwan Kubutar Da Yan Makaranta 100 Da Aka Sace December 8, 2025 Iraki Ta Musanta Cewa Ta Tushe Asusun Hizbullah Da Ansarallah December 8, 2025 Sabon Fada Ya Barke A Tsakanin Thailand Da Cambodia December 8, 2025 Iran Ta Yi Allawadai Da Kisan Fararen Hula A Kasar Sudan December 8, 2025 Macron Na Faransa Ya Yi Wa Najeriya Alkawalin Taimakawa Akan Matsalolin Tsaro December 8, 2025 Rasha Ta Yi Maraba Da Cire Sunanta A Matsayin ” Barazanar Da Amurka Teke Fuskanta December 8, 2025 Majid Majidi Na Iran Ya Sami Kyauyar Girmamawa Daga Cibiyar Fina-finai Na “Eurasia Dake Kasar Rasha December 8, 2025 Benin : Har yanzu Shugaba Patrice Talon ne a kan mulkin_fadar shugaban kasa December 7, 2025 Dole ne Amurka ta amince da ‘yancin Iran na samar da makamashin nukiliya cikin lumana (Araghchi) December 7, 2025 Hamas : ‘’Babu batun kwance damarar makamai matuƙar Isra’ila ta ci gaba da mamaya’’ December 7, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci