A daidai lokacin da ake ci gaba da takaddama a HKI dangane da wasikar da wasu sojojin sama su ka rubuta na sukar yakin Gaza, wasu tsoffin ma’aikatar hukumar leken asiri ta “Mosad” sun bi sawunhu.

Kafafen watsa labarum HKI sun ambaci cewa, fiye da tsoffin jami’an leken asirin kungiyar MOSAD 200 ne su ka rattaba hannu akan wata takarda suna nuna goyon bayansu da sojan sama da su ka yi kira a kawo karshen yakin Gaza.

Kwanaki kadan da su ka gabata, tashar talabijin din Channel 13; ta watsa labarin da yake cewa; Wasu ma’aikatar rundunar leken asiri ta soja sun shiga cikin masu kira da a kawo karshen yakin na Gaza da kuma dawo da fursunoni daga can.

An kuma samu irin wannan halayyar ta yin kira a kawo karshen yakin a tsakanin likitocin soja su 100 sai kuma malaman jami’a su ma daruruwa.

Kiraye-kirayen da sojojii suke yi a HKI da na kwo karshen yakin Gaza da mayar da fursunonin yaki, ya bude wata sabuwar takaddama a tsakanin ‘yan  siyasa.

Wasikar ta bude jayayya a tsakanin ‘yan sahayoniya akan cewa, Netanyahu yana ci gaba da yin yaki ne saboda maslahar kashin kansa.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: karshen yakin

এছাড়াও পড়ুন:

Yara masara zuwa makaranta barazana ne ga kasa — Shettima

Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima ya ce yawan yara marasa zuwa makaranta a Najeriya a barazana ce da ke buƙatar haɗin gwiwa daga dukkan matakan gwamnati da masu ruwa da tsaki.

Shettima ya yi wannan bayani a taron Zauren Ilimin Najeriya na 2025 da aka gudanar a Abuja, wanda Kungiyar Gwamnonin Najeriya tare da Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya da abokan hulɗa suka shirya.

Ya ce matsalar ilimi ba za ta iya warwarewa da ƙoƙarin gwamnati kaɗai ba, yana mai jaddada cewa: “Yawan yaran da ba sa zuwa makaranta bukatar gaggawa ce ta ƙasa da ke buƙatar haɗin kai tsakanin Gwamnatin Tarayya, jihohi, kananan hukumomi da al’umma.”

Shettima, wanda mai ba shi shawara na musamman Aliyu Modibbo Umar ya wakilta, ya ce dole malamai su samu horo mai kyau, kulawa da kuma kima a matsayinsu na ƙwararru domin a samu ingantaccen ilimi.

An dakatar da Shugaban Karamar Hukumar Lafia NAJERIYA A YAU: Yadda Abincin Da Mutane Ke Ci Ke Zamewa Guba

Ya kuma yi kira da a faɗaɗa ilimin sana’o’i da fasaha domin matasa su samu ƙwarewar da za ta taimaka musu a kasuwa. Ya ce hakan na buƙatar kuɗi masu dorewa da aka tsara yadda ya kamata.

Mataimakin Shugaban Kasa ya bayyana cewa duk da ƙarin kuɗin da gwamnati ta ware wa ilimi daga Naira tiriliyan 1.54 a 2023 zuwa Naira tiriliyan 3.52 a 2025, gibin kuɗi ya yi yawa fiye da abin da gwamnati za ta iya ɗauka ita kaɗai.

Ya ambaci ƙarin kuɗin da aka ware wa hukumar TETFUND, UBEC da asusun tallafin ilimi na NELFUND, ciki har da Naira biliyan 86.3 da aka raba wa ɗaliban jami’a sama da 450,000 a ƙarƙashin tsarin lamunin ɗalibai.

Sai dai ya jaddada cewa gina tsarin ilimi mai ɗorewa na buƙatar haɗin gwiwa daga kamfanoni masu zaman kansu, shugabannin masana’antu, ƙungiyoyin tsoffin ɗalibai, masu bayar da tallafi da al’umma.

Shettima ya ce: “Dole mu wuce tsarin gwamnati kaɗai wajen bayar da kuɗi, mu rungumi haɗin gwiwa da zai tallafa wa dakunan gwaje-gwaje, cibiyoyin bincike, cibiyoyin sana’o’i, ƙungiyoyin kirkire-kirkire da asusun tallafi.”

Ya kuma bukaci kananan hukumomi da masarautu su ɗauki nauyin gine-ginen makarantu, gyara, tsaro da kuma kulawa da malamai.

Shettima ya yi kira ga duk masu ruwa da tsaki a taron da su jajirce wajen samar da kuɗin ilimi mai dorewa, yana mai cewa haɗin kai ne kaɗai zai iya sauya tsarin ilimi a Najeriya tare da shirya matasa domin fuskantar duniyar zamani.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Annabi SAW Ya Zarce Duk Sauran Annabawa Yawan Mu’uzijoji
  • Nazarin CGTN: Fahimtar Matsayin Sin Cikin Yanayin Tattalin Arzikin Duniya Na Da Muhimmanci
  • Hamas : Isra’ila ta gaza cika alkawarin da ta dauka kan yarjejeniyar tsagaita wuta
  • Amurka ta matsa lamba a kan kotun ICC don janye bincike kan yakin  Gaza da Afghanistan: Reuters
  • Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Sha Alwashin Wadata Al’ummarsa da Tsaftataccen Ruwan Sha
  • Hukumar Karɓar Ƙorafe-ƙorafe ta Jigawa Ta Nemi Kotuna Su Daina Jan Kafa Wajen Aiwatar da Shari’a
  • Iran Ta yi Tir Da Kisan Karen Dangin Isra’ila A Gaza A Ranar Yaki Da Kisan Kiyashi Ta MDD
  • DAGA LARABA: Ko Ziyarar Tawagar Amurka Za Ta Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Najeriya?
  • Saurayi ya kashe budurwarsa sannan ya soya qwaqwalwarta 
  • Yara masara zuwa makaranta barazana ne ga kasa — Shettima