Aminiya:
2025-11-02@21:10:39 GMT

HOTUNA: Abba da Gwamnan Edo sun ziyarci iyalan mafarautan da aka kashe a Edo

Published: 1st, April 2025 GMT

Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf da takwaransa na Jihar Edo Monday Okpebholo, sun ziyarci garin Torankawa da ke Kano domin jajanta wa iyalai da yan uwan mafarautan nan guda 16 da aka kashe a Jihar Edo.

Gwamnonin biyu sun ziyarci garin ne da manufar tabbatar wa da iyalan waɗanda lamarin ya shafa cewa lallai gwamnatin jihar Edo za ta hukunta waɗanda suka yi wannan aika-aika sannan kuma gwamnatin za ta biya su diyya.

Ta zuba wa abokan aikinta guba bayan taƙaddama kan ƙarin matsayi Mene ne matsayin azumin Sitta Shawwal a Mazhabar Malikiyya

“Wannan ziyara ba kawai ta jaje da ta’aziyya ba ce, a’a ta nuna tabbacin ƙoƙarin samar da adalci.

“Iyalan waɗannan mamata na buƙatar abin da ya fi kalaman baka — suna buƙatar aiwatar da duk abin da aka faɗa za a yi musu.

“Ba za mu zauna ba har sai mun ga an kama waɗanda suka yi wannan aika-aika, sai an yi holinsu a bainar jama’a sannan a hukunta su,” in ji Abba Kabir.

A nasa ɓangaren gwamnan jihar ta Edo, Monday Okpebholo ya miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan inda ya ba su tabbacin cewa gwamnatinsa za ta yi adalci ba daɗewa ba.

Aminiya ta ruwaito cewa, Abba ya buƙaci Sanata Okpebholo da ya tabbatar da biyan diyyar mafarauta da aka kashe a jiharsa ta Edo a hanyarsu ta komawa gida domin bukuwan Sallah.

Abba ya bayyana haka ne a lokacin da Gwamna Monday ya jagoranci tawagar gwamnatinsa zuwa Kano domin jajanta wa gwamnati da al’ummar jihar bisa abin da ya faru na kisan matafiyan a makon jiya.

A jawabinsa, gwamna Abba ya yaba da ƙoƙarin takwaran nasa bisa matakan da ya ɗauka, inda ya ce a nasu ɓangaren sun ɗauki matakan da suka dace domin hana ramuwar gayya, “domin mutanen Kano masu son zaman lafiya ne da maraba da baƙi .

“Yawancin waɗanda aka kashe ɗin ’yan Kano ne. An tare su ne a jiharka a hanyarsu ta dawowa daga Fatakwal, aka gana musu azaba, sannan aka ƙone wasu daga cikinsu.”

Gwamna ya kuma yaba da ƙoƙarin gwamnatin Edo wajen ganin an ɗauko gawarwakin tare da binne su kamar addini ya tsara, da kuma kama wasu daga cikin waɗanda ake zargi.

Sai dai gwamna Abba Kabir Yusuf ya ce yana da buƙatu biyu da yake so gwamnan ya yi ƙoƙarin ganin an cika su.

A cewasa, “muna so a gabatar da waɗanda ake zargi a gaban menama labarai domin duniya ta gansu kowa ya ga fuskokinsu. Wannan zai taimaka wajen kwantar da hankalin iyalan waɗanda aka kashe,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa Gwamnan na Edo ya faɗa cewa masa za a tabbatar da hukunci, “kuma ina da tabbacin gwamna zai cika wannan alƙawarin.”

Ya ce, “abu na biyu shi ne muna so a tabbatar da biyan diyyar waɗanda aka kashe ɗin ga iyalansu. Na san kai mutum ne mai nagarta da cika magana, kamar yadda ka ce za a biya diyya, muna so a biya diyyar cikakkiya, kuma a cikin lokaci.”

Tun da farko, gwamna Monday Okpebholo ya bayyana takaicinsa kan yadda lamarin ya faru, inda ya ce tuni an kama mutum 14 da ake zargi suna da hannu a lamarin kuma za su tabbatar da sun fuskanci hukunci.

Bayan wannan ganawar ce da ta gudana a Fadar Gwamnatin Kano, Gwamna Abba ya jagoranci Gwamna Okpebholo zuwa garin Torankawa da ke Karamar Hukumar Bunkure, domin jajanta wa iyalan waɗanda aka kashe.

Okpebholo ya shaida wa iyalan cewa ba zai yi ƙasa a gwiwa ba har sai an tabbatar da adalci.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Kano Monday Okpebholo waɗanda aka kashe tabbatar da

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda

Daga Usman Muhammad Zaria

 

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta yi kira ga mazauna jihar Jigawa da su kasance masu bin doka da oda, tare da yin aiki kafada da kafada da rundunar ‘yan sanda domin tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali a fadin jihar.

Kwamishinan ‘Yan Sanda na jihar Jigawa, CP Dahiru Muhammad, ne ya bayyana haka lokacin da ya karɓi sabbin motoci 10 kirar Toyota Hilux da Gwamna Umar Namadi ya bai wa rundunar a Dutse, babban birnin jihar.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, SP Lawan Shiisu Adam, ya fitar, CP Dahiru Muhammad ya yaba da jajircewar Gwamna Umar Namadi wajen tallafa wa hukumomin tsaro domin sauke nauyin da ke kansu a jihar.

Ya bayyana cewa, wannan gudummawa ta nuna cikakken kudirin gwamnatin Gwamna Namadi na ƙara inganta harkokin tsaro da kuma tallafawa Rundunar ‘Yan Sanda ta Najeriya wajen aiwatar da aikinta na kare rayuka da dukiyoyin jama’a a fadin jihar.

Kwamishinan ya nuna cewa, waɗannan sabbin motoci 10 za su taimaka matuƙa wajen rage lokacin da ake ɗauka kafin amsa kiran gaggawa, tare da ƙara inganta aikin rundunar a fadin jihar.

Ya ƙara da cewa, za a yi amfani da motocin yadda ya kamata, tare da kula da su don tabbatar da ingantaccen  tsaro.

CP Dahiru Muhammad ya kuma sake jaddada aniyar rundunar wajen ci gaba da tabbatar da zaman lafiya, doka da oda, tare da ƙarfafa haɗin gwiwa da sauran hukumomin tsaro da masu ruwa da tsaki.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
  • Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar
  • An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m
  • Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aure