Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-07-11@07:42:11 GMT

Cutar Sankarau Ta Kashe Mutane 56 A Kebbi

Published: 20th, March 2025 GMT

Cutar Sankarau Ta Kashe Mutane 56 A Kebbi

Gwamnatin jihar Kebbi, ta tabbatar da mutuwar mutane 56 a sakamakon barkewar cutar sankarau a jihar inda 25 a Gwandu, 16 a Jega, 14 kuma suka mutu a kananan hukumomin Aliero na jihar.

 

Da yake zantawa da manema labarai, babban sakatare a ma’aikatar lafiya ta jihar, Dakta Nuhu Koko, ya ce an samu jimillar mutane 653 da ake zargin sun kamu da cutar a kananan hukumomi biyar da suka hada da Aliero, Jega, Gwandu, Birnin Kebbi da Bunza.

 

A cewarsa, samfurorin da aka aiko da kuma tabbatarwa daga cibiyar bincike, yanzu jihar ta san yadda take magance cututtukan sankarau.

 

Ya kara da cewa, an aika samfurori 17 zuwa dakin gwaje-gwaje na kasa da kasa da ke Abuja domin tabbatar da su, 5 daga cikinsu sun dawo ba tare da wata matsala ba,5 kuma ba sun tabbatar da cutar ce yayin da Aliero aka samu bullar cutar guda 3, Gwandu 1 da Jega 1.

 

Dokta Koko ya ce, dukkan majinyatan guda biyar da suka kamu da cutar an yi musu magani kuma an sallame su, yayin da ake jiran sakamakon gwaji guda 7 a NRL Abuja.

 

Babban Sakatare, ya bayyana cewa, an samu allurai 3,000 na rigakafin CSM daga ma’aikatar lafiya da jin dadin jama’a ta tarayya kuma an rarraba su a fadin kananan hukumomi 3 masu fama da wannan cutar.

 

Ya bayyana cewa, an samar da cibiyoyin keɓewa tare da haɗin gwiwar MS a Gwandu, Jega da Aliero tare da katifu, magunguna da sauran kayan masarufi da aka samar wa ƙananan hukumomin da abin ya shafa.

 

COV/Abdullahi Tukur

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Sankarau

এছাড়াও পড়ুন:

Zagaye na 5 A Tattaunawar Gaza da HKI  Ya tashi ba tare da Sun Dai-daita ba A Doha

Tattaunawa na baya-bayan nan tsakakin HKI da Hamas ya tashi ba tare da wani ci gaba ba a birnin Doha na kasar Qatar. Idan an cimma wannan yarjeniyar dai ana saran musayan fursinoni 10 na HKI sannan za’a saki wasu da dama dake hannun HKI,

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa rashin nasarar wannan taron ya sanya makomar yaki a Gaza cikin rudu don yanzun kuma ba’a san abinda zai faru ba. Kuma bamu san manufar HKI ba a wannan yakin.

Wani jami’in Falasdinawa ya fadawa tashar talabijin ta Al-Sharq kan cewa da alamun tawagar yahudawan sunzo ba taren da niyyar cimma wani Abu ba, tunda duk abunda aka  tambayesu sai suce sai sun tambayi tel-Aviv, wanda ya nuna basu zo don cimma wata yarjeniya ba.

Don haka jami’in ya zargi HKI da wargaza tattaunawar. Mai yuwa kuma suna kan shirin na korar Falasdinawa daga Gaza gaba daya,

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Kasar Iran Yace Huldar kasar Iran Da IAEA Zai Ci Gaba Ne Idan Ta Daina Fuska Biyu
  • An kashe mutum ɗaya da ƙona gidaje sama da 100 a Taraba
  • Zagaye na 5 A Tattaunawar Gaza da HKI  Ya tashi ba tare da Sun Dai-daita ba A Doha
  • ’Yan ƙabilar Ibo ne suka fi aikata laifi a Jihar Anambra ba Fulani ba — Gwamna Soludo
  • Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 13 A Neja
  • Na Biya Bashin Garatutin Naira Biliyan 13.6 Da ’Yan Fanshon Zamfara Ke Bi Tun 2011 – Gwamna Lawal
  • Iran Ta Tabbatar Da Cewa Tana Iya Yakar Amurka Da HKI A Lokaci Guda
  • HKI Ta Kashe Falasdianwa 6 A Gaza, Kuma Tsoffin Fursinoni
  • An ceto mutum 6 daga hannun masu garkuwa a Kebbi
  • ‘ADC za ta mayar da APC jam’iyyar adawa a 2027’