Gwamna Edo Okpebholor Ya Jajantawa Iyalan Wadanda Aka Kashe
Published: 1st, April 2025 GMT
Game da aka yi wa mafarauta 16 a Udune Efandion, karamar hukumar Uromi ta jihar Edo, gwamna Monday Okpebholo ya yi kakkausar suka ga wannan aika-aika na rashin hankali, yana mai bayyana hakan a matsayin “wani abu da kuma muguwar dabi’a.
Okpebholo, tare da Gwamna Abdullahi Yusuf na Jihar Kano, sun yi addu’a ga rayukan wadanda abin ya shafa a kauyen Bunkure na jihar Kano inda wadanda abin ya shafa suka fita tare da kuma da bada tabbacin ga iyalan wadanda abin ya shafa cewa za a gurfanar da masu laifin gaban kuliya.
Allah wadai da gwamnan ya biyo bayan harin da wasu gungun ’yan bindiga suka kai wa mafarautan, wadanda aka yi kuskuren cewa masu garkuwa da mutane ne, wanda ya yi sanadin kashe mutane 16.
Lamarin dai ya janyo cece-ku-ce, inda shugaba Bola Tinubu ya bayar da umarnin a farauto wadanda suka aikata wannan aika-aika tare da umurtar jami’an tsaro da su gudanar da bincike cikin gaggawa.
Okpebholo ya bada tabbacin cewa gwamnatin sa za ta dauki dukkan matakan da suka dace domin ganin an kamo duk wanda ke da hannu a harin tare da gurfanar da shi gaban kuliya. Ya zuwa yanzu dai an kama mutane 14 da ake zargi da hannu a lamarin.
Gwamnan ya kuma yabawa al’ummar jihar Kano da ma daukacin yankin Arewa kan rashin daukar doka a hannunsu da sunan harin ramuwar gayya.
Ya sanar da cewa, ana shirin bayar da diyya ga duk wadanda lamarin ya shafa.
Gwamna Yusuf wanda ya karbi bakuncin Okpebolo a Kano, ya yi alkawarin bayar da tallafin kudi da kayan abinci ga iyalan mafarauta da aka kashe a Uromi, jihar Edo.
Ya kuma yi alkawarin cewa za a biya diyya ga wadanda lamarin ya shafa, yana mai jaddada cewa gwamnati ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen tabbatar da adalci ga wadanda abin ya shafa.
ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: wadanda abin ya shafa
এছাড়াও পড়ুন:
Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
Sojojin Najeriya sun kashe aƙalla mayakan ƙungiyar ISWAP 8, ciki har da manyan kwamandojinta biyu a Jihar Borno.
Wata majiyar leƙen asiri daga rundunar haɗin kai ta OPHK ta bayyana cewa an kashe ’yan ta’addan ne a wata arangama da suka yi da sojojin a kan hanyar Maiduguri zuwa Baga a safiyar ranar Litinin.
DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabalaA cewar majiyoyin, an yi arangamar ce a kusa da Garin Giwa da ke gab da ƙauyen Kauwa, lokacin da ’yan ta’addan suka yi wa dakarun da ke sintiri kwanton ɓauna.
“A yayin wannan artabu, an kashe ’yan ta’adda takwas, ciki har da Munzirs biyu (kwamandojin filin daga na ƙungiyar) da kuma Qaid ɗaya (shugaban sashe).
“An kashe Modu Dogo, Munzir daga Dogon Chukun, wani Munzir da ba a bayyana ba, da Abu Aisha, shugaban sashe (Qaid) daga Tumbun Mota,” in ji wata majiya.
Majiyar ta ƙara da cewa wasu mayaƙa da dama sun samu raunuka, musamman waɗanda suka tsere da ƙafa bayan sun yi watsi da babura 14 da sojojin suka ƙwato.