Gwamna Edo Okpebholor Ya Jajantawa Iyalan Wadanda Aka Kashe
Published: 1st, April 2025 GMT
Game da aka yi wa mafarauta 16 a Udune Efandion, karamar hukumar Uromi ta jihar Edo, gwamna Monday Okpebholo ya yi kakkausar suka ga wannan aika-aika na rashin hankali, yana mai bayyana hakan a matsayin “wani abu da kuma muguwar dabi’a.
Okpebholo, tare da Gwamna Abdullahi Yusuf na Jihar Kano, sun yi addu’a ga rayukan wadanda abin ya shafa a kauyen Bunkure na jihar Kano inda wadanda abin ya shafa suka fita tare da kuma da bada tabbacin ga iyalan wadanda abin ya shafa cewa za a gurfanar da masu laifin gaban kuliya.
Allah wadai da gwamnan ya biyo bayan harin da wasu gungun ’yan bindiga suka kai wa mafarautan, wadanda aka yi kuskuren cewa masu garkuwa da mutane ne, wanda ya yi sanadin kashe mutane 16.
Lamarin dai ya janyo cece-ku-ce, inda shugaba Bola Tinubu ya bayar da umarnin a farauto wadanda suka aikata wannan aika-aika tare da umurtar jami’an tsaro da su gudanar da bincike cikin gaggawa.
Okpebholo ya bada tabbacin cewa gwamnatin sa za ta dauki dukkan matakan da suka dace domin ganin an kamo duk wanda ke da hannu a harin tare da gurfanar da shi gaban kuliya. Ya zuwa yanzu dai an kama mutane 14 da ake zargi da hannu a lamarin.
Gwamnan ya kuma yabawa al’ummar jihar Kano da ma daukacin yankin Arewa kan rashin daukar doka a hannunsu da sunan harin ramuwar gayya.
Ya sanar da cewa, ana shirin bayar da diyya ga duk wadanda lamarin ya shafa.
Gwamna Yusuf wanda ya karbi bakuncin Okpebolo a Kano, ya yi alkawarin bayar da tallafin kudi da kayan abinci ga iyalan mafarauta da aka kashe a Uromi, jihar Edo.
Ya kuma yi alkawarin cewa za a biya diyya ga wadanda lamarin ya shafa, yana mai jaddada cewa gwamnati ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen tabbatar da adalci ga wadanda abin ya shafa.
ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: wadanda abin ya shafa
এছাড়াও পড়ুন:
An kashe ’yan ta’adda 45 a Neja
Jami’an Hukumar Tsaron Farin Kaya DSS da takwarorinsu na rundunar sojin ƙasa sun kashe aƙalla ’yan ta’adda 45 da ke addabar wasu sassan Jihar Neja.
Bayanai sun ce an kashe ’yan ta’addan ne a ƙauyen Iburu da ke Ƙaramar Hukumar Shiroro a ranar Juma’ar da ta gabata bayan jami’an DSS sun tattaro bayanan sirri kan harƙallar miyagun a yankin.
Mutum miliyan 1.2 na fama da ciwon hanta a Kano Najeriya ta ba wa Habasha kyautar iri da itatuwan cashew 100,000Majiyoyin tsaro sun ce DSS ta samu bayanan sirri kan wani hari da ’yan ta’addan ke shirin kaiwa ƙauyen Iburu a kan babura, lamarin da sojojin da ke shirin ko-ta-kwana suka tari hanzarinsa.
Ɗaya daga cikin majiyoyin ya shaida cewa an yi musayar wuta tsakanin ɓangarorin biyu, inda aka harbe ’yan ta’adda 45 yayin da jami’an tsaro biyu suka kwanta dama sai kuma huɗu da suka jikkata.
“Mazauna ƙauyukan da lamarin ya shafa sun ce sun ƙidaya aƙalla gawawwakin ’yan ta’adda 40 da kuma gomman babura da aka lalata a yayin musayar wutar.”
Aminiya ta ruwaito cewa wannan tumke ɗamara da ƙara ƙaimi da jami’an tsaron suka yi na zuwa ne a daidai lokacin da Hukumar Kwastam ke bayyana damuwar cewa jami’anta na faɗawa tarkon ’yan ta’adda a yankin.
Ana iya tuna cewa, a watan Afrilun da ya gabata ne Kwanturola Janar na Kwastam, Bashir Adeniyi, ya yi ƙorafin cewa ’yan ta’adda na sheƙe ayarsu a Iyakar Babanna da ke Jihar Neja a ɓangaren da ta yi makwabtaka da Jamhuriyyar Benin.
A wancan lokacin, Adeniyi ya ce jami’ansa sun tsallake rijiya da baya bayan wani kwanton ɓauna da ’yan ta’addan suka yi musu a matsayin ramuwar gayya a sakamakon kame wasu jarkokin man fetur 500 da ake shirin kai musu.