BUK ta ƙaddamar da Sabuwar Manhajar Duba Sakamako Jarabawa
Published: 1st, April 2025 GMT
Jami’ar Bayero Kano (BUK) ta kaddamar da wani tsari na yanar gizo wanda zai baiwa dalibai damar shiga da duba sakamakon kammala karatunsu ta hanyar lambobi.
Wannan sabon yunkuri shine karo na farko da cibiyar ta samar da sakamako ta hanyar irin wannan dandali.
An sanar da shirin ne a cikin wata takarda mai dauke da sa hannun mataimakin magatakarda kuma shugaban hukumar kula da harkokin jama’a Lamara Garba Azare.
A cewar sanarwar jami’ar, tsarin da myBUK Team ya kirkira kuma yana bawa ɗalibai damar dawo da sakamako kai tsaye ta hanyar amfani da sashen rajistar dalibai.
Takardun sakamakon za su nuna a sarari na kowane kwasa amma dole ne ɗaliban da suka kammala shekarar ƙarshe su jira amincewar Majalisar Dattawa kafin su sami sakamakonsu.
Daya daga cikin shugabannin kungiyar dalibai a Jami’ar, Bilal Muhammad Bello, ya yabawa ci gaban da aka dade ana jira tare da bada tabbacin cewa wannan zai rage damuwar dalibai da kuma kawar da jinkiri da aka samu wajen samun sakamakon.”
“Wannan tsarin yana ba ɗalibai damar sanya ido kan ci gaban karatun su tare da kawar da cunkoson da ake samu na jama’a a a allon manna sakamakon jarabawa.”
Da yake tsokaci kan zaman sa a matsayin Sanata na 24 na SUG mai wakiltar Sashen Sadarwa, Bello ya ce. “Na ba da shawarar samun damar samun sakamako ta yanar gizo a lokacin da nake majalisar dalibai, Alhamdulillah, wannan hangen nesa ya zama gaskiya.”
KHADIJAH ALIYU
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda wani ɗan sanda ya rasu a hanyar zuwa ɗaurin aurensa
Wani jami’in ɗan sanda, SP Mustapha Garba Gumau, ya yi gamo ajalinsa a wani hatsarin mota yayin da ya rage aƙalla sa’a ɗaya a ɗaura masa aure.
Aminiya ta ruwaito cewa, ajali ya katse hanzarin jami’in ne a kan hanyar Gumau zuwa Magaman-Gumau da ke Ƙaramar Hukumar Toro ta Jihar Bauchi, inda za a ɗaura masa aure.
Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikacin Jami’ar Northwest a Kano HOTUNA: Yadda aka yi sulhu da ƙasurgumin ɗan fashin daji Ado Aliero a KatsinaSP Gumau wanda hatsarin ya rutsa da shi da abokansa ya rasu ne da misalin ƙarfe 9 yayin da ake shirin ɗaura masa aure da misalin ƙarfe 10 na safiyar ranar Asabar.
Wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar ’yan sandan Bauchi, CSP Mohammed Ahmed Wakil ya fitar ta ce an tabbatar da rasuwar matashin da ke shirin angwancewa bayan an garzaya da shi asibiti.
Wakil ya ce jami’in ya rasu tare da wasu abokansa biyu da ke cikin wata mota ƙirar marsandi bayan sun yi karo da wata motar ƙirar Opel Vectra.
Sanarwar ta ambato Kwamishinan ’yan sandan Bauchi, CP Auwal Sani Omolori yana jajanta wa iyalan mamatan da kuma addu’ar mutuwa ta zamanto hutu a gare su.