Kotu Ta Dakatar Da INEC Karɓar Buƙatar Yin Kiranye Ga Senata Natasha
Published: 21st, March 2025 GMT
Kotun Tarayya da ke Lokoja, Jihar Kogi, ta bayar da umarnin dakatar da Hukumar Zaɓe ta ƙasa (INEC) daga karɓar kowace buƙatar da aka gabatar domin fara shirin kiranye ga Senata Natasha Akpoti-Uduaghan daga Majalisar Dattawa.
Haka kuma, kotun ta hana ma’aikatan INEC, da wakilansu, ko duk wani wanda ke da hannu daga karɓar ko yin aiki da kowace buƙata da ke ɗauke da sunayen ƙarya daga mutanen mazaɓar Kogi ta tsakiya, sannan ta hana gudanar da kowanne zaɓe ko taro kan lamarin har sai kotu ta yanke hukunci.
An bayar da wannan umarnin ne bayan buƙatar gaggawa da Anebe Jacob Ogirima da wasu mutane huɗu daga yankin Kogi ta tsakiya, waɗanda suka yi rajista a matsayin masu zabe suka yi. Buƙatar ta samu wakilcin lauya Smart Nwachimere, na West-Idahosa, SAN & Co., inda kotu ta ɗage shari’ar zuwa 6 ga Mayu, 2025, don samun rahoton aikawa da gayyata da kuma ci gaba da sauraron shari’ar.
A cikin martani ga wannan hukunci, wata ƙungiya mai suna, Action Collective, ta yabawa kotu bisa wannan umarnin, inda shugaban ƙungiyar, Dr. Onimisi Ibrahim, ya ce wannan umarnin zai ƙara bayyana rashin biyayya daga wasu mutanen da ke goyon bayan shirin ƙoƙarin cire Natasha daga Majalisar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Kar A Mika Wuya Ga “Damisar Takarda”
To, bayanai a sama sun nuna ra’ayi iri daya na gwamnatocin dimbin kasashe masu tasowa. Ban da haka, wani binciken jin ra’ayin jama’a da kafar yada labarai ta Sin CGTN, da jami’ar Renmin ta kasar Sin suka gudanar a kasashe 38, ya nuna cewa, matakan ramuwar gayya da kasar Sin ta dauka kan kasar Amurka suna samun goyon baya tsakanin al’ummun kasashe daban daban, inda a dimbin kasashe masu tasowa da suka hada da Najeriya, da Kenya, da Masar, da Ghana, da Afirka ta Kudu, da Turkiya, matakan kasar Sin suka samu goyon baya daga mutane fiye da kaso 70% da aka gudanar da bincike kansu. Kana a kasashen yamma da suka hada da Faransa, da Jamus, da Canada, da Birtaniya, da dai sauransu, jimillar ta kai tsakanin kaso 65.5% zuwa 70.5%.
Sai dai kasar Sin ba ta son yakin ciniki, ko da yake tana wakiltar ra’ayi mai adalci na akasarin kasashe. Kamar yadda ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ta ce, “Babu mai samun nasara a yakin harajin fito, da na ciniki.” Amma, bisa la’akari da cewa kasar Amurka ce ta ta da yakin ciniki, to, kasar Sin ba za ta taba mika wuyarta ba, kuma ba za ta yi hakuri da matakin cin zarafi ba. Sin ta nanata cewa, idan kasar Amurka na son daidaita al’amarin ta hanyar tattaunawa, to, ya kamata ta “daina barazana da matsin lamba, ta yi tattaunawa bisa tushen daidaito, da mutunta juna, da amfanawa juna.”
Hakika, ban da wadannan abubuwan da aka ambata, don kaddamar da tattaunawa, ana bukatar sanin ya kamata, wanda kasar Amurka ta rasa. Misali, yadda kasar Amurka ta janye jikinta daga dimbin kungiyoyin kasa da kasa, da yarjeniyoyin duniya, da daina samar da tallafi ga sauran kasashe, sun nuna yunkurinta na kaucewa daukar nauyi sakamakon raguwar karfinta a fannin tattalin arziki. Sai dai wannan yanayi mai kunci bai hana ta ci gaba da neman ba da umarni ga sauran kasashe, da cin zarafinsu ba. Ban da haka, mu kan ga yadda shugabannin kasar Amurka suke ba da umarni da gyara shi cikin sauri, da yin karairayi yadda suka ga dama, da wulakanta takwarorinsu na sauran kasashe, da kasa kare bayanan sirrin da suka shafi yaki, wadanda suka nuna gazawarsu wajen aiki. Ma iya cewa, yanzu haka, kasar Amurka tamkar damisar takarda ce, mai ban tsoro amma maras karfi.
Za mu jira lokacin da za a iya komawa teburin shawarwari don tattauna batun kawo karshen yakin ciniki, inda za a jira har zuwa lokacin da kasar Amurka za ta gamu da dimbin matsaloli, ta yadda za ta yi watsi da matakan zalunci, da sake samun sanin ya kamata. Amma yanzu muna iya tabbatar da matakin da ya kamata kasashe masu tasowa su dauka, wato karfafa hadin kansu, maimakon mika wuya ga kasar Amurka, wadda ta kasance tamkar wata “damisar takarda”, da ke neman cin zarafin sauran kasashe, da ta da rikici a duniya. (Bello Wang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp