An bukaci shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da ya tabbatar da sa ido sosai kan yadda aka fitar da kudade naira biliyan 758 domin warware duk wasu basussukan fensho da ake bin su domin hana yin zagon kasa.

 

A cikin wata sanarwa da kungiyar Muslim Media Watch Group ta fitar, kodineta na kasa, Alhaji Ibrahim Abdullahi ya kuma yabawa shugaba Tinubu kan matakin da ya dauka na ragewa ‘yan fansho na tarayya daga halin kuncin da suke ciki.

 

A cewar sanarwar, dole ne a sanya ido sosai kan sabuwar manufar domin hana duk wani zagon kasa daga wasu Ma’aikatan Asusun Fansho (PFA) da ake zargi da batawa wasu ‘yan fansho da suka yi rajista da su rai.

 

Ya bayyana cewa wasu Ma’aikatan Asusun Fansho sun kara wa ‘yan fansho matsalolin da suke fuskanta ta hanyar jinkirta biyan su fansho kusan shekaru 2 bayan sun yi ritaya.

 

Ta ce duk irin wadannan laifuffuka da rashin iya aiki sun karfafa cin hanci da rashawa a sassan al’umma na tattalin arzikin kasa.

 

Sanarwar ta yi kira da a samar da cikakken tsari da ingantaccen tsarin sa ido daga fadar shugaban kasa da hukumar fansho ta kasa PENCOM wajen magance matsalolin ‘yan fansho gaba daya.

 

Tana kira ga Gwamnonin Jihohi a fadin Tarayya da su yi koyi da Gwamnatin Tarayya wajen biyan basussukan da ake bin Jihohi da Kananan Hukumomi.

 

Sanarwar ta kuma yi kira ga gwamnatin tarayya da ta gaggauta yin la’akari da yin kwaskwarima ga dokokin gudanar da shari’ar laifuka (ACJ) domin hukunta laifukan tattalin arziki da ake tafkawa a Najeriya.

 

REL/ALI MUHAMMAD RABIU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kwara

এছাড়াও পড়ুন:

Martanin sojojin Iran ga Isra’ila zai zama mafi muni idan aka ci gaba da kai hari (Pezeshkian)

Shugaban aksar Iran, Massoud Pezeshkian, ya bayyana cewa martanin sojojin kasarsa ga Isra’ila zai zama mafi muni idan hare-haren Isra’ilar suka ci gaba.

A wata tattaunawa ta wayar tarho da firaministan Pakistan Shehbaz Sharif, shugaban kasar Iran Massoud Pezeshkian ya tabbatar da cewa dakarun gwamnatin Jamhuriyar Musulunci ta Iran za su dauki kwararan matakan mayar da martani mai tsauri idan har gwamnatin Isra’ila ta ci gaba da kai farmaki kan Iran.

“Masu da’awar kare hakkin bil’adama ba wai kawai suna goyon bayan zaluncin gwamnatin sahyoniyawa ba ne, har ma suna karfafa mata gwiwar aikata wadannan munanan ayyuka ta hanyar ba ta makamai da kayan aiki,” in ji shi.

Mr. Pezeshkian ya kara da cewa gwamnatin Isra’ila da ke samun goyon bayan Amurka da kasashen yammacin Turai ta sabawa dukkanin dokokin kasa da kasa.

A nasa bangaren, firaministan Pakistan ya bayyana goyon bayan kasarsa ga al’ummar iran, yana mai yin Allah wadai da keta hurumin kasar Iran da ‘yancinta, wanda ya zama cin zarafi ga dokokin kasa da kasa da kuma kundin tsarin mulkin MDD.

Sharif ya sake jaddada cewa Iran na da cikakken ‘yancin kare kanta a karkashin doka ta 51 na kundin tsarin mulkin MDD inda ya bayyana fatan ganin an dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wang Yi Ya Tattauna Ta Wayar Tarho Da Ministocin Harkokin Wajen Iran Da Isra’ila
  • Martanin sojojin Iran ga Isra’ila zai zama mafi muni idan aka ci gaba da kai hari (Pezeshkian)
  • Dimokuradiyya A Shekara 26: Ba Yabo Ba Fallasa
  • Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA
  • Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
  • Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya
  • Masana Ilimin Nukiliyar Iran Sun Yi Shahada
  • Gwamnati Ta Yi Karin Haske Kan Biyan Tallafin Rage Radadi Da Mafi Karancin Albashi
  • Ambaliya: Gwamnatin Kano ta fara tsaftace magudanan ruwa
  • NAJERIYA A YAU: Rashin Aikin Yi Da Hanyoyin Magance Su A Najeriya