Yemen zata sake kai hare-hare kan jiragen ruwan Isra’ila
Published: 12th, March 2025 GMT
Kasar Yemen ta sanar da cewa za ta ci gaba da kai hare-haren soji kan jiragen ruwan Isra’ila a wasu muhimman yankunan teku da ke gabar tekun kasar bayan cikar wa’adin da ta gindaya wa Isra’ila na ta sake bude mashigar zirin Gaza tare da bayar da damar kai agaji cikin yankunan Falasdinawa da yaki ya daidaita.
Rundunar sojin Yaman ta fitar da sanarwar a cikin daren jiya, inda ta ce za a ci gaba da kai hare-hare kan duk wasu jiragen ruwa masu alaka da ISra’ila kamar yadda Abdul-Malik al-Houthi shugaban kungiyar gwagwarmayar Ansarullah ta kasar ya bada umurni.
Tunda farko Shugaban kungiyar ta Ansarullah ya bai wa gwamnatin Isra’ila kwanaki hudu ta bude hanyoyin kai kayan agaji Gaza ko ta fuskanci martini.
Sanarwar ta kara da cewa “Wannan haramcin zai ci gaba da kasancewa har sai an sake bude hanyoyin shiga Zirin Gaza kuma an ba da izinin shigar da agajin jin kai da suka hada da abinci da magunguna.
A karshe sojojin sun jaddada goyon bayansu ga al’ummar Falasdinawa masu tsayin daka a yankin zirin Gaza da kuma gabar yammacin kogin Jordan da ke mamaye da su, wadanda kuma suka fuskanci mummunar ta’addancin Isra’ila, tare da jaddada goyon bayansu ga gwagwarmayar Falasdinawa.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
An Kira Yi Gwamnatin Canada Da Ta Kama Olmert Da Livini Na “Isra’ila
Kungiyoyin kare hakkin bil’adama na kasar Canada sun shigar da kara ga jami’an ‘yan sandan kasar, da kuma ma’aikatar shari’a da su kama tsohon Fira ministan haramtacciyar kasar Isra’ila Ehud Olmert da kuma ministan harkokin waje Tzipi Livni bisa rawar da su ka taba a baya a laifukan yaki a Gaza a tsakanin 200-2009.
Kungiyoyin sun bukacin ganin an fitar da sammacin kamo ‘yan sahayoniyar biyu a bisa dogaro da dokokin kare hakkin dan’adama da laifukan yaki na kasar Canada, saboda kasar tana karkashin yarjejeniyar Geneva ta 4 da ta bukaci kasashe su hukunta masu irin wadannan laifukan.
Bugu da kari, kungiyoyin sun ce Olmert wanda ya yi fira minista daga 2006 zuwa 2009, shi ne mai rike da mukami na koli a lokacin hare-haren soja da su ka kashe fararen hula da lalata muhimman cibiyoyi. Haka nan kuma a wancan tsakanin sojojin Haramtacciyar kasar Isra’ila sun yi amfani da makamin Phosphorus mai fitar da farin hayaki da aka haramta amfani da shi a yake-yake. Sojojin na mamaya sun kuma rusa gidaje da lalata tsarin magudanan ruwa na kiwon lafiya, kamar kuma yadda su ka yi wa fararen hula da dama kisa ba tare da shari’a ba. Bugu da kari, sun hana shigar da kayan agaji zuwa yankin Gaza a wancan lokacin.
Ita kuwa Livini ta kasance memba a cikin karamar majalisar tsaro wacce ta taka rawa wajen shatawa sojoji ta’asar da su ka yi, ta kuma furta cewa, martanin da ya kamata “Isra’ila” ta mayar wa Falasdinawa ya kamata ya zama ” Na Hauka.”
Dama dai mutanen biyu suna da wata shari’ar da aka kai su kara a gaban kotuna daban-daban na kasashen turai. Kuma a 2009 ne wata kotu a Birtaniya ta fitar da sammaci a kamo su.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka An Kashe Shugaban ‘Yan Dabar Gaza “Abu Shabab” Da Isra’ila Ke Goyon Baya December 4, 2025 Iran : Jagora Ya Bayyana Ra’ayin Musulunci Kan Hakkokin Mata December 4, 2025 Taron IMO : Tehran Ta Yi Watsi Da Zarge-zargen Isra’ila Marasa Tushe December 4, 2025 MDD ta nemi a kawo karshen mamayar Isra’ila a Falasdinu da kuma Tuddan Golan December 4, 2025 Rundunar Ruwa ta IRGC na Gudanar Da Atisayen Soja a Tekun Fasha December 4, 2025 Dan wasan Taekwando Na kasar Iran Ya Samua Lambar Yabo Ta Zinariya December 4, 2025 Hamas Za ta Mikawa Isra’ila Samfurin Da Aka Samu A Karkashin Burabutsai A Gaza December 4, 2025 Iran: Tsaron Yankin Tekun Fasha Jan Layi Ne Da Za’a Fuskanci Mayar Da Martani Adan Aka Taba Shi December 4, 2025 Kungiyoyin Kare Hakkin Dan Adam Sun Kira Ga Kasar Kanada Ta Kama Olmert Da Livni December 4, 2025 Majalisa Ta Tabbatar Da Janar Christopher Musa A Matsayin Ministan Tsaro December 4, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci