HausaTv:
2025-11-07@07:10:42 GMT

Yemen zata sake kai hare-hare kan jiragen ruwan Isra’ila

Published: 12th, March 2025 GMT

Kasar Yemen ta sanar da cewa za ta ci gaba da kai hare-haren soji kan jiragen ruwan Isra’ila a wasu muhimman yankunan teku da ke gabar tekun kasar bayan cikar wa’adin da ta gindaya wa Isra’ila na ta sake bude mashigar zirin Gaza tare da bayar da damar kai agaji cikin yankunan Falasdinawa da yaki ya daidaita.

Rundunar sojin Yaman ta fitar da sanarwar a cikin daren jiya, inda ta ce za a ci gaba da kai hare-hare kan duk wasu jiragen ruwa masu alaka da ISra’ila kamar yadda Abdul-Malik al-Houthi shugaban kungiyar gwagwarmayar Ansarullah ta kasar ya bada umurni.

Tunda farko Shugaban kungiyar ta Ansarullah ya bai wa gwamnatin Isra’ila kwanaki hudu ta bude hanyoyin kai kayan agaji Gaza ko ta fuskanci martini.

Sanarwar ta kara da cewa “Wannan haramcin zai ci gaba da kasancewa har sai an sake bude hanyoyin shiga Zirin Gaza kuma an ba da izinin shigar da agajin jin kai da suka hada da abinci da magunguna.

A karshe sojojin sun jaddada goyon bayansu ga al’ummar Falasdinawa masu tsayin daka a yankin zirin Gaza da kuma gabar yammacin kogin Jordan da ke mamaye da su, wadanda kuma suka fuskanci mummunar ta’addancin Isra’ila, tare da jaddada goyon bayansu ga gwagwarmayar Falasdinawa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Zanga zanga Ta Barke A Birmingham Ta Nuna Kin Jin Isra’ila .

Rahotanni su bayyan cewa zanga-zanga ta barke a wajen filin wasan kwallon kafa a Birmingham kafin fara gasar kwallon kafa tsakanin isra’ils maccabe tel aviv da kuma England Ason villa inda suke yi ta rera taken nuna damuwa da halin da yankin Gaza ke ciki da kuma yin kira ga hukumar fifa da ta kori Isra’ila daga cikintta,

Wannan yana nuna irin yadda kin jinin Isra’la ya yadu a duniya saboda irin kisan gillan da take yi wa alummar gaza, inda lamarin ya shafi hatta a harkokin wasanni da sauran rayuwar alumma a kasashen turai .

Rahotano da jaridar the independent ta nakalto ya nuna cewa magoya bayan falasdinawa sun lika hotuna a fadin birnin dake yin kira ga hukumar fifa da ta dakatar da wasan kuma sun kewaye filin wasan da tutocin falasdinu , sai dai magoyan bayan kungiyar kwallon kafa ta Maccabi yan tsiraru sun tsaya cirko-cirko a wajen.

Gwamnatin birtaniya ta aike da jami’an yan sanda sama da 700 a wajen domin tabbatar da tsaro, masu rajin kare hakkin dana dam suna ta kiraye –kirayen korar isra’ila daga fifa kuma sun bayyana wasan a masatayin abin kunya a daidai lokacin da isra’ila ke kisan gilla a gaza.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label Name* Email* Website Label Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Pezeshkiyan: Masu Kawo Rarraba Tsakanin Musulmi Suna yi wa Yan Sahayuniya Aiki Ne November 7, 2025 Shugaban Najeriya Bola Tinubu Ya yi Alwashin Kawo Karshen Ta’addanci A Kasar November 7, 2025 Araqchi Ya Ce: Harin Amurka Kan Kasar Venezuela Ya Bayyana Karara Duniya Tana Gani November 6, 2025 Qalibaf: Iran Da Pakistan Zasu Aiwatar Dukkan Yarjejeniyar Da Suka Cimma A Tsakaninsu November 6, 2025 Kwamitin Tsaro Ya Ce: Amurka Ta Bukaci Duba Kudurin Neman Kafa Rundunar Kasa Da Kasa A Gaza November 6, 2025 Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kashe Mutum Guda Tare Da Jikkata Wasu Uku A Kudancin Lebanon   November 6, 2025 Sayyid Muqtada al-Sadr Ya Fadakar Da Magoya Bayansa Kwanaki Kafin Zabe A Iraki November 6, 2025 Araghchi : Yakin kwanaki 12 ya bamu babban darasi November 6, 2025 Putin : zamu dauki mataki idan Amurka ta koma gwajin makaman nukiliya November 6, 2025 Iran, China da Rasha sun tattauna gabanin taron Gwamnonin IAEA November 6, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zanga zanga Ta Barke A Birmingham Ta Nuna Kin Jin Isra’ila .
  • Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu
  • Hafsan sojin sama ya umarci a yawaita yi wa ’yan ta’adda ruwan bama-bamai
  • Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki
  • Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa
  • Gaza : MDD Ta damu kan keta yarjejeniya tsagaita wuta da Isra’ila ke yi 
  • Gwamnan Kano Ya Yaba Da Matakin Da Sojoji Suka Dauka kan Matsalar Tsaron Tsanyawa
  •  Ansarullah: Dakarunsu A Shirye Suke Don Tunkarar Duk Wata Barazana Daga Isra’ila
  • Admiral Sayyari Ya Ce: Isra’ila Ba Ta Kai Matsayin Da Zata Yaki Iran Ba
  • Shugaban Xi Ya Gana Da Firaministan Rasha