HausaTv:
2025-03-20@11:47:03 GMT

Yemen zata sake kai hare-hare kan jiragen ruwan Isra’ila

Published: 12th, March 2025 GMT

Kasar Yemen ta sanar da cewa za ta ci gaba da kai hare-haren soji kan jiragen ruwan Isra’ila a wasu muhimman yankunan teku da ke gabar tekun kasar bayan cikar wa’adin da ta gindaya wa Isra’ila na ta sake bude mashigar zirin Gaza tare da bayar da damar kai agaji cikin yankunan Falasdinawa da yaki ya daidaita.

Rundunar sojin Yaman ta fitar da sanarwar a cikin daren jiya, inda ta ce za a ci gaba da kai hare-hare kan duk wasu jiragen ruwa masu alaka da ISra’ila kamar yadda Abdul-Malik al-Houthi shugaban kungiyar gwagwarmayar Ansarullah ta kasar ya bada umurni.

Tunda farko Shugaban kungiyar ta Ansarullah ya bai wa gwamnatin Isra’ila kwanaki hudu ta bude hanyoyin kai kayan agaji Gaza ko ta fuskanci martini.

Sanarwar ta kara da cewa “Wannan haramcin zai ci gaba da kasancewa har sai an sake bude hanyoyin shiga Zirin Gaza kuma an ba da izinin shigar da agajin jin kai da suka hada da abinci da magunguna.

A karshe sojojin sun jaddada goyon bayansu ga al’ummar Falasdinawa masu tsayin daka a yankin zirin Gaza da kuma gabar yammacin kogin Jordan da ke mamaye da su, wadanda kuma suka fuskanci mummunar ta’addancin Isra’ila, tare da jaddada goyon bayansu ga gwagwarmayar Falasdinawa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Gaza: Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sanadiyar Hare-Haren HKI Ya Dara 400

HKI ta keta yarjeniyar tsagaita wuta a Gaza, a jiya inda ta kai hare-hare masu yawa, wadanda suka yi sanadiyar mutuwar mutane fiye da 300 ya zuwa safiyar yau.

Tashar talanijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa, jiragen yakin HKI sun kai hare-haren a kan yankunan zirin Gaza da dama, kuma yawan mutanen da suka yi shahada ya zuwa yanzu ya kai 342 kumamafi yawansu mata da yara ne.

Labarin ya kara da cewa a garin Khan Yunus na kudancin Gaza jiragen yakin HKI sun kashe falasdinawa 77 sannan falasdinawa akalla 20 suka kashe a birnin Gaza. SAMA kamfanin dillancin labaran Falasdinawa ya bayyana cewa daruruwan Falasdinawa sun rasa rayukansu, kuma har yanzun ana neman wasu a wuraren da yahudawan suak kai hare hare.

Tashar talabijin ta Aljazeera ta bada labarin cewa hare-haren yahudawan sun game dukkan zirin gaza kuma sai da suka girgiza yanking aba daya.

Wasu masana suna ganin sojojin yahudawan sun yi amfani da sabbin makamai masu tun 20 wadanda gwamnatin Trump ta bawa HKI bayan ya dare kan kujerar shugabancin kasar ta Amurka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hare-Haren Isra’ila Cikin Dare Sun Hallaka Mutum Aƙalla 50 A Gaza
  • Amurka Ta Kai Sabbin Hare-Hare Kan Kasar Yemen Don Tallafawa HKI
  • Hare-haren Isra’ila sun yi sanadin shahadar falasdinawa kusan 1,000 a cikin sa’o’I 48
  • Iran : hare-haren Isra’ila a Gaza ci gaba da kisan kare dangi ne
  • Mutum 330 Sun Mutu Yayin da Isra’ila Ta Kai Wa Gaza Sabbin Hare-hare 
  • Yemen Ta Cilla Makamai Kan Kataparen Jirgin Ruwa Mai Daukar Jiragen Yaki Na Amurka A Tekun Red Sea
  • Gaza: Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sanadiyar Hare-Haren HKI Ya Dara 400
  • Sayyid Husi: Idan Amurka Ta Ci Gaba Da Kai Mana Hare-hare To Muna Da Hanyoyin Gasa Mata Aya A Hannu
  • Munanan Hare-hare  Sojojin HKI A Gaza Da Safiyar Yau Talata Sun Yi Sanadiyyar Shahadar Fiye Da Falasdinawa 200
  • Isra’ila ta ƙaddamar da sabon hari a Zirin Gaza