Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas ta ce matakin da Isra’ila ta dauka na hana shigar da kayayyakin jin kai da bukatun yau da kullum a zirin Gaza da aka yi wa kawanya ya zama “laifi na yaki da kuma hukuncin gama-gari.”

A cikin wata sanarwa da ta fitar, Hamas ta ce matakin rufewar ya saba yarjejeniyar tsagaita bude wuta ta watan Janairu ne.

“Irin wannan matakin keta dokokin kasa da kasa da na jin kai, da yarjejeniyar Geneva, kuma laifukan yaki ne da hukuncin gama-gari da ke barazana ga rayukan fararen hula wadanda basu ji basu gani ba.”

Hamas ta ce rufewa da kuma hana shigar da kayan agaji sama da kwana 10 a jere yana kara tsananta radadin da Falasdinawa sama da miliyan biyu ke fama da su, kuma yana nuna yiwuwar fuskantar yunwa a Gaza.

“hana shigar da abinci, magunguna, man fetur, da hanyoyin agaji na yau da kullun ya haifar da tashin gwauron zabin abinci da kuma tsananin karancin magunguna, lamarin da ya ta’azzara matsalar jin kai a Gaza.”

Hamas ta yi kira ga masu shiga tsakani da su matsa wa gwamnatin kasar lamba wajen “cika alkawurran da ta dauka” a karkashin yarjejeniyar tsagaita bude wuta.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: hana shigar da

এছাড়াও পড়ুন:

Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Kai Hare-Haren Wuce Gona Da Iri Kan Birnin Tul-Karam Na Falasdinu

Sojojin mamayar Isra’ila na ci gaba da kai hare-haren wuce gona da iri kan birnin Tulkaram da sansanoninsa da ke gabar yammacin kogin Jordan

Sojojin mamayar Isra’ila na ci gaba da kai hare-hare kan birnin Tulkaram da sansanoninsa a rana ta 119 a jere, da kuma sansanin Nour Shams a rana ta 106, a daidai lokacin da sojojin suke ci gaba da tsananta kai hare-hare kan yankuna Falasdinawa da kuma kma su tare da yinawungaba da su zuwa wuraren da baa san ko’ina ba ne.

Da sanyin safiyar Lahadi ne sojojin mamayar Isra’ila suka kai farmaki gidan Essam Odeh, sakataren kungiyar hadin kan iyalan shahidai da ke yankin kudancin Falasdinu, inda suka kama shi da diyarsa Sarah mai shekaru 20 bayan an yi musu tambayoyi. An saki Issam Odeh, yayin da sojojin mamayar suka tafi da diyarsa Sarah, da nufin matsawa dansa Amir ya mika kansa. Idan dai ba a manta ba, an sha tsare Issam Odeh, sannan kuma an tsare ‘ya’yansa biyu Muhammad da Isma’il a gidan yari na tsawon watanni ba tare da gurfanar da su a gaban kotu ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gaza : Spain ta bukaci kasashen duniya su kakabawa Isra’ila takunkumi
  • Falasdinawa 30 sun yi shahada a Wani harin Isra’ila kan wata makaranta
  • Shugaban Jam’iyyar Adawa A Burtaniya Ya Ce HKI Tana Yaki A Gaza Ne A Madadin Gwamnatin Kasar
  • Sheikh Na’im Kassim: Gwagwarmaya Tana Da Wata Hanyar Ta Korar ‘Yan Mamaya
  •  Sojojin HKI Sun Yi Wani Sabon Kisan Kiyashi A Gaza
  • Shugaban Shirin  HKI Da Amurkan  Na Raba Kayan Agaji A Gaza Ya Yi Murabus
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Kai Hare-Haren Wuce Gona Da Iri Kan Birnin Tul-Karam Na Falasdinu
  • ‘Yar Majalisar Dokokin Ireland Ta Yi Suka Kan Shugabannin Turai Tare Da Neman Afuwa Daga Falasdinawa
  • Kafafen Watsa Labarun Isra’ila: Kungiyoyin Kasa Da Kasu Sun Ki Shiga Cikin Shirin Isra’ila Da Amurka Na Raba Kayan Agaji
  • Iran: Amurka Ta Shiga Tattaunawa Da Ita Ne Bayan Da Fahimci Daukar Matakin Soja Ba Zai Yi Amfani Ba