Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas ta ce matakin da Isra’ila ta dauka na hana shigar da kayayyakin jin kai da bukatun yau da kullum a zirin Gaza da aka yi wa kawanya ya zama “laifi na yaki da kuma hukuncin gama-gari.”

A cikin wata sanarwa da ta fitar, Hamas ta ce matakin rufewar ya saba yarjejeniyar tsagaita bude wuta ta watan Janairu ne.

“Irin wannan matakin keta dokokin kasa da kasa da na jin kai, da yarjejeniyar Geneva, kuma laifukan yaki ne da hukuncin gama-gari da ke barazana ga rayukan fararen hula wadanda basu ji basu gani ba.”

Hamas ta ce rufewa da kuma hana shigar da kayan agaji sama da kwana 10 a jere yana kara tsananta radadin da Falasdinawa sama da miliyan biyu ke fama da su, kuma yana nuna yiwuwar fuskantar yunwa a Gaza.

“hana shigar da abinci, magunguna, man fetur, da hanyoyin agaji na yau da kullun ya haifar da tashin gwauron zabin abinci da kuma tsananin karancin magunguna, lamarin da ya ta’azzara matsalar jin kai a Gaza.”

Hamas ta yi kira ga masu shiga tsakani da su matsa wa gwamnatin kasar lamba wajen “cika alkawurran da ta dauka” a karkashin yarjejeniyar tsagaita bude wuta.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: hana shigar da

এছাড়াও পড়ুন:

Araghchi : Iran a shirye take ta shiga tattaunawa da Turawa bisa mutunta juna

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya ce Tehran a shirye take ta shiga tattaunawa da kasashen Turai bisa mutunta juna.

A wata tattaunawa ta wayar tarho, Araghchi da Ministan Harkokin Wajen Netherlands Caspar Veldkamp sun tattauna hanyoyin inganta alakar juna da sabbin abubuwa dake faruwa a yankin da na kasa da kasa.

Babban jami’in diflomasiyyar na Iran ya nanata tsarin kasar na kulla kyakkyawar alaka ta diflomasiyya da kasashen.

Iran da kasashen Turai dai na tattaunawar ba-zata kai a kai tun shekara ta 2021, shekaru uku bayan da Amurka ta fice daga yarjejeniyar nukiliyar iran – tare da maido da takunkumin da Washington ta kakaba wa Jamhuriyar Musulunci ta Iran.

bangarorin kasashen Turai da suka shiga yarjejeniyar nukiliya – Birtaniya, Faransa da Jamus – sun kasa cika alkawarin da suka dauka na dawo da Washington cikin yarjejeniyar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Araghchi : Iran a shirye take ta shiga tattaunawa da Turawa bisa mutunta juna
  • Harin da Isra’ila ta kai ya kashe Falasdinawa 9 a arewacin Gaza
  • Fitar Da Nama Zuwa Saudiyya: Mayankar Dabbobi Ta Jurassic Ta Yi Hadin-gwiwa Da Shirin CDI
  • Iran Ta Yi Tir Da HKI Da Kokarin Wanke Kanta Tare Da Rabawa Addinin Musulunci Ta’addanci
  • Kasashen Sin, Rasha Da Iran Sun Yi Kira Da Dakatar Da Matakin Kakaba Takunkumi Na Bangare Guda
  • Sudan Ta Haramta Shigar Da Kayayyakin Daga Kenya
  •  An Yi Gargadi Akan Rushewar Kungiyar  Agajin Falasdianwa Ta UNRWA
  • Hamas Ta Yi Gargadin Bullar Yunwa A Gaza A Cikin Watan Ramadan
  • Hamas ta yi maraba da matakin Yemen na haramtawa jiragen ruwan Isra’ila shiga teku
  • Rasha  na goyon bayan sake farfado da yarjejeniyar nukiliyar Iran