HausaTv:
2025-03-18@00:44:30 GMT

Jamus, Faransa, Birtaniya Da Italiya Sun Yi Maraba Da Shirin Larabawa Kan Gaza

Published: 9th, March 2025 GMT

Kasashen Jamus, Faransa, Birtaniya da Italiya “sun yi maraba” da shirin kasashen Larabawa na sake gina Gaza.

 A cikin wata sanarwa ta hadin guiwa da ministocin harkokin wajen kasashen suka fitar a birnin Berlin, sun ce shirin idan an aiwatar da shi zai bada damar gaggauta warware mummunan halin da Falasdinawa ke ciki a Gaza.

A yayin taron da suka gudanar ne a ranar Talata data gabata a Masar kasashen Larabawan suka gabatar da wani shiri da zai lakume dalar Amurka Biliyan 53 na sake gina Gaza cikin fiye da shekara biyar inda shirin zai mayar da hankali kan taimakon gaggawa,dawo da ababen more rayuwa da kuma ci gaban tattalin arziki mai dorewa.

Shirin na kasashen Larabawa tamakar neman maye gurbin shirin da shugaban Amurka Donald Trump, ya fitar a watan da ya gabatar na karbe iko da zirin Gaza dama tilasta musu hijira zuwa kasashen Masar da Jordan.

Matakin na Trump dai ya fuskanci martini da tofin Allah tsine daga daga Falasdinawa da kasashen Larabawa da kuma gwamnatoci da yawa a duniya, inda sukayi fatali da duk wani shiri na korar mutanen Gaza daga kasarsu ta asali.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasashen Larabawa

এছাড়াও পড়ুন:

Kofar JMI A Bude Take Don Tattaunawa Da Kasashen Turai

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa kofar JMIa bude yake ga kasashen Turai don tattaunawa da fahintar juna kan matsalolin da bangarorin biyu suke sabani a kansu, tare da mutunta hurumin Juna.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto ministan yana fadar haka a jiyaAsabar a lokacinda yake zantawa ta wayar tarho da tokwaransa na kasar Netherlands Caspar Veldkamp a jiya Asabar.

Ministan ya kara da cewa dangantakar diblomasiyya tsakanin Dutch da Iran tsohuwar dangantaka ce. Sannan Iran tana da nufin fadada shi.

A Nashi bangaren ministan harkokin wajen kasar Netherlands yay aba da yadda dangantaka tsakanin kasashen biyu yake bunkasa. Sannan dangane da tsabirin kasar Iran guda uku, Abu Musa, Tumbe kucek da Bozorg wadanda iran take takaddama da UAE dangane da mallakarsu, ya ce abu ne wadanda kasashen biyu suke iya warwarewa a tsakaninsu. Banda haka yace dokokin kasa da kasa ma suna iya warware wannan sabanin da ke tsakaninsu.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Kasar Amurka Ya Kara Yawan Kasashen Da Ya Sa Wa Takunkumin Shiga Amurka
  • Adadin Shahidan Falasdinawa A Gaza Ya Karu Da 14 A Jiya Lahadi Saboda Hare-Haren Sojojin HKI
  • Hizbullah ta yi Allah wadai da harin Amurka da Birtaniya a kan Yemen
  • Sojoji sun kashe ’yan bindiga 31, sun lalata sansaninsu a Katsina
  • Ma’aikatar Ilimin Amurka Na Shirin Korar Ma’aikata 1,300
  • Kofar JMI A Bude Take Don Tattaunawa Da Kasashen Turai
  • Gwamnatin Da Mutanen Kasar Somalia Sun Ki Amincewa Da Karban Mutanen Gaza
  • Gwamnati Za Ta Goyi Bayan Shirin Fim Kan Tarihin Shekaru 25 Na Dimokuraɗiyyar Nijeriya
  • Karkush: Ganawata Da Arakci A Tehran Ta Yi Kyau
  • Fitar Da Nama Zuwa Saudiyya: Mayankar Dabbobi Ta Jurassic Ta Yi Hadin-gwiwa Da Shirin CDI