Tashe-tashen Hankula Na Ci Gaba Da Yin Sanadin Rayuka A Siriya
Published: 9th, March 2025 GMT
Rahotanni daga Siriya na nuni da cewa gomman mutane ne sukayi shahada a sabon rikicin da ya barke a baya baya nan a wasu sassan kasar.
Majiyoyin cikin gida na kasar sun tabbatarwa da tashar Al-Mayadeen cewa, a safiyar Asabar an yi ta kashe-kashe a kauyuka da garuruwa da dama a yankunan karkarar Latakia, Tartous da kuma Hama.
Majiyar ta yi nuni da cewa an yi wani kisan kiyashi a kauyen Al-Sanobar da ke gundumar Jableh.
A cewar wani rahoto na wucin gadi, an kashe mutane 72.
An tabbatar da mutuwar wasu mutane 10 a kauyen Harisoun da ke cikin karkarar Baniyas a cikin gundumar Tartous.
A sa’i daya kuma, kungiyar kare hakkin bil’adama ta kasar Syria (SOHR) ta yi nuni da cewa mazauna al’ummar Alawite na cikin fargabar da ke da alaka da yiwuwar kisan kiyashi a kansu daga kungiyoyi masu dauke da makamai masu alaka da gwamnatin al-Jolani.
Kungiyar kare hakkin bil adama ta Syria ta tabbatar da cewa an raba dimbin iyalai daga kauyuka da garuruwan da ke gabar teku, ba tare da wani bayani kan makomar wadannan iyalai ba.
Majiyoyin cikin gida sun ruwaito wa Al-Mayadeen cewa an kashe fararen hula fiye da 400 a kisan kiyashi da kisa a gabar tekun Siriya.
Kungiyar da ke sa ido kan kare hakkin bil adama a Syria ta bayar da rahoton cewa, sama da fararen hula 300 ne aka kashe tun daga ranar alhamis a yayin wani samame da suka kan magoya bayan tsohon shugaban kasar Bashar al-Assad a yankin gabar tekun yammacin kasar.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Falasdinawa Kimani 635 Amurka da HKI Suka Kashe A Cibiyoyin Karban Abinci A Gaza
Kamfanin dillancin Labaran Assosciated Press ta bayyana cewa ana ci gaba da sukar Amurka da HKI kan cibiyoyin kisa da suka kafa a Gaza da sunan tallafawa Falasdinawa da abinci.
Labarin ya bayyana cewa ya zuwa yanzu Amurka da HKI sun kashe Falasdinawa kimani 635 wajen karban abinda suka kira taimakon abinci bayan sun sa su yunwa mai tsanani wanda zai sa su dole su fito su ne mi aminda zasu a sa a cikinsu. Amma idan sun so sojojin HKI su kashesu.
Kamfanin dillancin labaran Associeated Press ya nakalto kamfanoni Amurka guda biyu wadanda sun ce sun shigar da kara Amurka da kuma HKI kan yadda suke gudanar da cibiyoyin rabon abinda suka kira abinci a gaza, wanda bai dace ba.
Kamfanin sun bayyana cewa jami’an tsaron da Amurka da HKI suka kawo a cibiyoyin, da alamun an basu izinin su kashe falasdinawa da suka fito karban abinda suka kira a gaji. Su kuma yi amfani da yuwan da suka sa su don tilasta ,masu fita da kuma kashe su daga karshe.
Wani kamfanin rabon abincin agajin ya ce sojojin na barin wuta kan Falasdinawa hatta kan wadansa suke layin karban agajin.