HausaTv:
2025-11-03@04:07:55 GMT

Tashe-tashen Hankula Na Ci Gaba Da Yin Sanadin Rayuka A Siriya

Published: 9th, March 2025 GMT

Rahotanni daga Siriya na nuni da cewa gomman mutane ne sukayi shahada a sabon rikicin da ya barke a baya baya nan a wasu sassan kasar.

Majiyoyin cikin gida na kasar sun tabbatarwa da tashar Al-Mayadeen cewa, a safiyar Asabar an yi ta kashe-kashe a kauyuka da garuruwa da dama a yankunan karkarar Latakia, Tartous da kuma Hama.

Majiyar ta yi nuni da cewa an yi wani kisan kiyashi a kauyen Al-Sanobar da ke gundumar Jableh.

A cewar wani rahoto na wucin gadi, an kashe mutane 72.

An tabbatar da mutuwar wasu mutane 10 a kauyen Harisoun da ke cikin karkarar Baniyas a cikin gundumar Tartous.

A sa’i daya kuma, kungiyar kare hakkin bil’adama ta kasar Syria (SOHR) ta yi nuni da cewa mazauna al’ummar Alawite na cikin fargabar da ke da alaka da yiwuwar kisan kiyashi a kansu daga kungiyoyi masu dauke da makamai masu alaka da gwamnatin al-Jolani.

Kungiyar kare hakkin bil adama ta Syria ta tabbatar da cewa an raba dimbin iyalai daga kauyuka da garuruwan da ke gabar teku, ba tare da wani bayani kan makomar wadannan iyalai ba.

Majiyoyin cikin gida sun ruwaito wa Al-Mayadeen cewa an kashe fararen hula fiye da 400 a kisan kiyashi da kisa a gabar tekun Siriya.

Kungiyar da ke sa ido kan kare hakkin bil adama a Syria ta bayar da rahoton cewa, sama da fararen hula 300 ne aka kashe tun daga ranar alhamis a yayin wani samame da suka kan magoya bayan tsohon shugaban kasar Bashar al-Assad a yankin gabar tekun yammacin kasar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

HKI Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza Inda Take Kashe Falasdinawa

Rahotanni sun bayyana cewa Isra’ila ta kashe wasu falasdinawa guda 5  yankin gaza a ci gaba da keta yarjejeniyar dakatar da bude wuta da suka cimma tsakaninta da kungiyar Hamas a farkon watan oktoba,

A yau juma’a kafar yada labarai ta falasdinu ta bayyana cewa sojojin Isra’ila sun harbe wani bafalasdine a yankin jabaliya dake arewacin yankin Gaza, haka zalika wani bafalasdine mai suna Mahmud suleman al- wadiya sojojin isaraila sun kashe shi a gabashin shuja’iyya dake makwabtaka da gabashin gaza, gari mafi girma a gaza kuma an jikkata wani dan uwansa,

Har ila yau  hamdi al-barim da mohamma salem qadi sun ji mummunan rauni sakamakon harin da sojojin Isra’ila suka kai musu a khan yunus dake yammacin gaza a yan kwanakin nan,

Tun daga lokacin da Isra’ila ta kaddamar da hare-hare a yankin Gaza zuwa yanzu a shekara ta 2023 sojojin Isra’ila na ci gaba da kai hare – hare a yankuna daban – daban inda akalla sun kashe mutane 1062 tare da jikkata wasu dubbai fiye da 20,000 kuma da suka hada da yara kana 1600 an cafkesu ana tsare da su .

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka An Tube Yarima Mai Jiran Gado Na Birtaniya Bayan Da Aka Tabbatar Da Laifinsa October 31, 2025 Kasashen Pakistan Da Afghanistan Sun Tsawaita Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta October 31, 2025 M D Duniya Tayi Gargadi Game Da Gwajin Nukiliya Da Amurka Ta Sanar Za ta yi October 31, 2025 Sudan Ta Yi Kira Ga Kwamitin Tsaro Da Ya Ayyana RSF A Matsayin Kungiyar ‘Yan Ta’adda October 31, 2025 Araqchi: Gwajin Makaman Nukiliya Na Amurka Babbar Barazana Ce Ga Duniya October 31, 2025 Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan October 31, 2025 Shugaban Lebanon Ya Umarci Sojoji Da Su Fuskanci Kutsen Na Isra’ila A Kudancin Kasar October 31, 2025 Madagascar Ta Sanar da Kafa Sabuwar Gwamnati Tare da Manyan ‘Yan Adawa October 31, 2025 Iran ta yi fatali da kalamman IAEA Kan Shirin Nukiliyarta October 30, 2025 Trump Ya Umarci Ma’aikatar Yakin Amurka Ta koma gwajin makaman nukiliya October 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Al’ummar Kauru Sun Koka Game Da Karuwar Hare-hare Da Ke Barazana Ga Gonaki Da Rayuka
  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
  • Kisan Kiristoci: Ba zan yaƙi ƙasar iyayena kan labaran ƙarya ba — Sojan Amurka
  • MDD Tana Sa Ido Akan Kashe-kashen Da Ake Yi A Zaben Kasar Tanzania
  • Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
  • ‘An Kashe Masu Zanga-zanga Akalla 500 a Tanzania’
  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • Za mu ci gaba da shirye-shiryen babban taronmu — PDP
  • HKI Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza Inda Take Kashe Falasdinawa
  • An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkuku