HausaTv:
2025-07-06@20:57:48 GMT

Tashe-tashen Hankula Na Ci Gaba Da Yin Sanadin Rayuka A Siriya

Published: 9th, March 2025 GMT

Rahotanni daga Siriya na nuni da cewa gomman mutane ne sukayi shahada a sabon rikicin da ya barke a baya baya nan a wasu sassan kasar.

Majiyoyin cikin gida na kasar sun tabbatarwa da tashar Al-Mayadeen cewa, a safiyar Asabar an yi ta kashe-kashe a kauyuka da garuruwa da dama a yankunan karkarar Latakia, Tartous da kuma Hama.

Majiyar ta yi nuni da cewa an yi wani kisan kiyashi a kauyen Al-Sanobar da ke gundumar Jableh.

A cewar wani rahoto na wucin gadi, an kashe mutane 72.

An tabbatar da mutuwar wasu mutane 10 a kauyen Harisoun da ke cikin karkarar Baniyas a cikin gundumar Tartous.

A sa’i daya kuma, kungiyar kare hakkin bil’adama ta kasar Syria (SOHR) ta yi nuni da cewa mazauna al’ummar Alawite na cikin fargabar da ke da alaka da yiwuwar kisan kiyashi a kansu daga kungiyoyi masu dauke da makamai masu alaka da gwamnatin al-Jolani.

Kungiyar kare hakkin bil adama ta Syria ta tabbatar da cewa an raba dimbin iyalai daga kauyuka da garuruwan da ke gabar teku, ba tare da wani bayani kan makomar wadannan iyalai ba.

Majiyoyin cikin gida sun ruwaito wa Al-Mayadeen cewa an kashe fararen hula fiye da 400 a kisan kiyashi da kisa a gabar tekun Siriya.

Kungiyar da ke sa ido kan kare hakkin bil adama a Syria ta bayar da rahoton cewa, sama da fararen hula 300 ne aka kashe tun daga ranar alhamis a yayin wani samame da suka kan magoya bayan tsohon shugaban kasar Bashar al-Assad a yankin gabar tekun yammacin kasar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Tsoro, Fargaba Da Wahala: ‘Bala’in Da Muka Gani A Yakin Sudan

Lamarin da ya haddasa daya daga cikin bala’i da mutane suka taba fadawa, inda sama da mutum miliyan 12 suka tsere daga gidajensu.

Darfur ta kasance yankin da nan da nan rikici kan tashi, inda RSF ke iko da yawancin yankin, in banda birnin el-Fasher wanda ya ci gaba da kasancewa a hannun rundunar sojin kasar da kawayenta.

Birnin el-Fasher ya sha ruwan bama-bamai a yayin da RSF ke kokarin kama shi.

A watan Afirilu RSF din ta sanar da shirin kafa gwamnati domin zama kishiya ga gwamnatin soji, abin da ya haddasa fargaba cewa hakan zai kai ga rarraba kasar.

Alawia ta ce yayin da fadan ya tsananta ake ta ruwan bama-bamai a watan da ya gabata, dole ita da mutanen gidansu suka tsere a kafa zuwa Tawila da ke yamma da el-Fasher.

‘Ya’yanta Marwan Mohamed Adam, mai shekara 21, ya gaya wa BBC cewa mayakan da ke da alaka da RSF sun ci zarafinsa a hanya inda suka lallasa shi da duka, har suka yi masa fashin ‘yan abubuwan da yake dauke da su.

Marwan ya ce ya tsira daga hannun gungun ne saboda ya yi musu karya daga inda ya fito.

Ya ce maharan sun debe matasan da suka gaya musu cewa daga el-Fasher suke suka je suka harbe su.

”Saboda haka a lokacin da suke yi min tambayoyi na ce musu daga Shakra nake – wanda zango ne a kan hanyar zuwa Tawila,” in ji shi.

“Za ka ji tsoro da fargaba, kana cikin tashin hankali, ka ji kamar ma ka riga ka mutu,” in ji Marwan mai shekara 21, a hirarsa da BBC, inda ya kara da cewa ya ga gawawwaki uku a kan hanya.

Wata matar, Khadija Ismail Ali, ta gaya wa BBC cewa “ga gawawwaki nan yashe a titi.”

Ta ce an kashe mutum 11 ‘yan gidansu a lokacin da ake yi wa el-Fasher ruwan makamai ta sama, kuma kananan yara uku sun mutum a lokacin tattakin da suka yi na kwana hudu daga birnin zuwa Tawila.

“Yaran sun rasu ne sakamakon kishirwa a hanya,” in ji Khadija.

‘Yanbindiga masu alaka da dakarun RSF sun kai hari kan kauyen iyalinta, el-Tarkuniya, a watan Satumba da ya wuce, inda kuma suka sace musu amfanin gona.

A lokacin suka tsere zuwa sansanin Zamzam inda ake fama da yunwa, daga nan kuma suka kara gaba zuwa el-Fasher yanzu kuma zuwa Tawila.

Kungiyar bayar da agajin lafiya – Alima ta ce ‘yanbindiga sun kwace filaye da gonakin yawancin iyalai a lokacin da suka kai musu hari.

Kungiyar ta kara da cewa wadanda suke zuwa Tawila, yawanci yara tuni sun kamu da cutar tsananin yunwa.

Alawia ta ce ‘yar uwarta ta jefar da dan abincin da suka yi guziri a lokacin da suke neman tsira daga hare-haren sama da suka gamu da su bayan sun wuce Shakra.

“Dan wani guntun wake ne da ya rage da dan gishiri muka rike a hannunmu domin ciyar da yara,” ta ce. Haka suke ta tattaki ba tare da ruwa ko abinci ba, har suka hadu da wata mata da ta ce musu za su iya samun ruwa a wani kauye da ke kusa.

Tawagar tasu ta tashi cikin dare domin ci gaba da tafiya zuwa wannan kauye, to amma ba su san cewa ashe suna yanki ne da ke karkashin ikon mayakan RSF ba.

“Mun gaishe su, amma kuma ba su amsa mana ba. Sun umarce mu, mu zauna a kasa, suka bincike kayanmu,” in ji Alawia.

Mayakan sun karbe kudin da muke rike da su fan 20,000 (na Sudan) (daidai da Dala 33), gaba daya kudin da iyalan ke da shi, tare da tufafi da takalman da suke dauke da su.

“Takalmana ba su da kyau amma duk da haka suka kwace su,” in ji Alawia.

Ta kara da cewa mayakan RSF sun ki su ba su ruwa, saboda haka suka ci gaba da tafiya har sai da suka kai kauyen el-Koweim.

A can suka hangi wata rijiya da mayakan RSF ke tsare da ita.

“Mun roke su, su ba mu ruwa akalla ko don yaron nan maraya, amma suka ki,” in ji Alawia.

Ta kara da cewa ta matsa domin ta je rijiyar amma mayakan suka mangare ta.

Iyalan sun ci gaba da tafiya haka a galabaice cikin kishirwa har sai da suka kai Tawila, inda isar su ke da wuya sai Alawia ta zube kasa, nan da nan aka garzaya da iya asibiti.

An sallame ta bayan an yi mata magani.

Haka shi ma yayanta Marwan an yi masa maganin raunukan da ya ji a lokacin da mayakan suka yi masa duka.

Alawia ta ce daga nan ne suka shiga neman dangin wannan yaron da suka ceto, bayan sun same su, suka danka musu shi.

A yanzu Alawia da iyalanta na zaune a Tawila, inda wasu iyalai suka karbe su, suka ba su masauki a gidansu.

“Yanzu dai rayuwa mun gode wa Allah, amma muna da fargabar yadda za ta iya kasancew

a a nan gaba,” Alawia ta shaida wa BBC.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Nijar: An Kashe Sojoji 10 A Wasu Hare-hare Biyu Na ‘Yan Ta’adda
  • Sheikh Kassim: Mayakan Hizbullah Mazajen Fagen Daga Ne
  • Mutane 8 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsari A Hanyar Lagos
  • Tsoro, Fargaba Da Wahala: ‘Bala’in Da Muka Gani A Yakin Sudan
  • Imam Khaminae Ya Halarci Makokin Ashoora A Gidansa A Tehran
  • Sheikh Na’im Kasim Yace Kare Kasa Baya Bukatar Izini Daga Wani
  • Ayatullahi Khatami Ya Ce Hukuncin Da Ya Cancanci Trump Da Netanyahu Shi Ne Kisa Saboda Zubar Da Jinin Bil’Adama
  • Haɗarin Da Ke Ƙunshe Da Jin Ɓangare Ɗaya Na Labari
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda da ƙwato makamai a Borno
  • Neja: Cikin Wata 10 Ibtila’i Ya Lakume Rayuka Sama Da 400 – NSMA