Aragchi: Hare-hare Kan Cibiyoyin Makamashin Nukliya Na Kasar Iran Ba Za Su Wargaza Shirin Ba
Published: 8th, March 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa hare-hare a kan cibiyoyin makamashin Nukliyar kasar ba zasu dakatar da ayyuka a cibiyoyin ba. Sai dai yin haka zai kara yada yaki a yankin kudancin Asiya.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Aragchi yana cewa cibiyoyin nukliya na kasar Iran suna da kekyawar kariya daga makamai.
Ministan ya bayyana haka ne a taron kasashen musulmi na OIC wanda aka gudanar a birnin Jedda na kasar Saudiya a yau Asabar. Ya ce iran zata ci gaba da neman fahintar juna ta hanyar diblomasiyy, Amma idan sun dage zasu yi amfani da karfi to Iran a shirye take ta kare kanta, kuma bata da zabi sai hakan.
A wani bangare ministan ya bayyana cewa Iran ba ta cikin sauri wajen samar da hulda da sabuwar gwamnatin kasar Siriya.
A jawabinsa a taron na OIC Aragchi ya kawo baton kasar Falasdinu da kuma shirin Amurka na kwace Gaza daga hannun falasdinawa ta kore su zuwa kasashen Masar da Jordan. Ya yi allawadai da hakan ya kuma bayyana cewa ya sabawa dukkan dokokin kasa da kasa.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Za A Yi Manyan Zabuka A Kasar Habasha A Watan Yuni Na 2026
Hukumar zaben kasar Habasha ta sanar da cewa za a yi manyan zabukan kasar a ranar 1 ga watan Yuni na 2026.
Shugabar hukumar zaben kasar ta Habasha Melatwork Hailu ta fada wa kafafen watsa labarun kasar cewa; Ana gudanar da ayyukan ne a yanzu domin tsara wuraren da za a yi zabukan da samar da rumfunan zabe a cikin rassan da za a kada kuri’a.”
Har ila yau shugabar hukumar zaben kasar ta Habasha ta ce, jam’iyyun siyasar kasar sun sami horon da ya dace domin bayyana da tallata manufofinsu ga jama’ar kasar.
Sai dai yin zabe a kasar ta Habasha yana fuskantar kalubale mai yawa. Kasar dai ba ta dade da fitowa daga yakin basasa ba wanda aka yi a tsakanin gwamnatin tarayya da yankin Tigray da aka yi a tsakanin 2020 zuwa 2022.
Rikicin ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 600,000, kuma wasu da adadinsu ya kai miliyan 1 su ka bar gidajensu.
Kuma har yanzu ana fama da tashe-tashen hankula a cikin yankunan Oromia da Amhara.
A jawabin da ya gabatar a ranar 28 ga watan Oktoba, Fira ministan kasar ta Habasha Abiy Ahmed ya ce; Gwamnatin kasar tana da karfin da za ta iya gudanar da zabukan.”
Haka nan kuma ya ce, zaben da za a yi zai zama shi ne mafi tsaruwa a tarihin kasar.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Turkiya A Shirye Take Ta Aike Da Sojoji Zuwa Yankin Gaza December 12, 2025 Kremlin: Putin Ya Bayyana Wa Shugaba Maduro Na Venezuela Goyon Bayansa December 12, 2025 Ben Gafir Ya Sha Alwashin Rushe Kabarin Sheikh Izzuddin Alkassam December 12, 2025 Maduro: Amurka Ta Bude Sabon Salon Fashi Akan Doron Ruwa December 12, 2025 Ayatollah Khamenei : Iran na samun ci gaba duk da kalubale da dama December 11, 2025 Kyaftin Traoré : Yau Burkina ta zama misali a duniya December 11, 2025 Iran da Kazakhstan Sun rattaba hannu kan yarjeniyoyi da dama December 11, 2025 Hamas : Isra’ila ta gaza cika alkawarin da ta dauka kan yarjejeniyar tsagaita wuta December 11, 2025 Kasashen ECOWAS sun rage kudin sufirin jiragan sama a tsakaninsu December 11, 2025 Dakarun IRGC 3 Sun Yi Shahada A wani Harin Ta’addanci A Kudancin Kasar Iran December 11, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci