Aminiya:
2025-05-01@04:23:35 GMT

EFCC ta tsare tsohon Gwamnan Akwa Ibom kan almundahanar Naira biliyan 700

Published: 5th, March 2025 GMT

Hukumar EFCC mai yaƙi da cin hanci da rashawa a Nijeriya, ta tsare tsohon Gwamnan Akwa Ibom, Udom Emmanuel kan zargin almundanar naira biliyan 700.

EFCC ta tsare tsohon gwamnan ne bayan ya amsa gayyatar ta a ranar Talata domin amsa wasu tambayoyi kan zargin karkatar da kuɗi da wata ƙungiya mai rajin yaƙi da masu zamba ta yi masa.

’Yan sanda sun ceto wani mutum da aka yi garkuwa da shi a Gombe Gobara ta ƙone shaguna 17 a tsohuwar kasuwar Gombe

Ƙungiyar ta yi zargin cewa tsohon gwamnan ya karɓi naira tiriliyan uku daga asusun Gwamnatin Tarayya a tsawon shekara takwas da ya yi yana mulki, amma ya bar wa jihar bashin naira biliyan 500 da rashin biyan kuɗin wasu ayyuka na naira biliyan 300 bayan ya sauka.

Haka kuma, ƙungiyar ta zargi Mista Emmanuel da kasa yin bayani kan yadda aka kashe wasu maƙudan kuɗi har naira biliyan 700 kamar yadda wakilinmu ya ruwaito.

Emmanuel ya kasance Gwamnan Akwa Ibom daga 2015 zuwa 2023 a ƙarƙashin jam’iyyar PDP.

A ranar Juma’ar da ta gabata ma EFCC ta gurfanar da tsohon Gwamnan Abia, Theodore Orji da wasu mutum huɗu a gaban kotu, bisa zargin ɓarnatar da kusan naira biliyan 47.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Akwa Ibom tsohon Gwamnan naira biliyan

এছাড়াও পড়ুন:

Boko Haram Sun Hallaka ‘Yan Zaman Makoki 7, Sun Jikkata Wasu A Borno

Sanata Ali Ndume, mai wakiltar yankin Borno ta Kudu, ya bayyana cewa hare-haren na ƙara ƙamari a yankin abun takaici ne.

Ya ce ya samu rahoto tsakanin Hawul da Garkida inda aka ce an kashe ’yan sa-kai sama da 10 a ranar Litinin.

A cewarsa, sama da mutane 100 aka kashe cikin wata guda a hare-hare da aka kai Sabon Gari, Izge, Kirawa, Pulka, Damboa, Chibok, Askira Uba da wasu garuruwa da dama.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwastam Ta Kama Jirage Marasa Matuka Da Sauran Kayayyaki Da Darajarsu Ta Haura Naira Biliyan 921 A Legas
  • Amurka ta sake laftawa wasu kamfaninin mai na Iran takunkumi
  • Gwamnan Sokoto Ya Amince Da Sauya Wa Manyan Sakatarori 25 Ma’aikatu A Jihar 
  • Talauci Da Rashin Ilimi Ne Ya Sa Ayyukan Boko Haram Ke Dawowa – Gwamnan Yobe
  • Shugaba Tinubu Ya Taya Sabon Firaiministan Kanada Mark Carney Murna
  • Rashin tsaro: Gwamnan AbdulRahman Ya Gana Da Sarakuna Masu Daraja Ta Daya A Jihar Kwara 
  • Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok
  • Kotu Ta Kori Ƙarar Neman Diyyar N1bn A Kan Buhari Da Emefiele Kan Sauya Fasalin Naira
  • Boko Haram Sun Hallaka ‘Yan Zaman Makoki 7, Sun Jikkata Wasu A Borno
  • Shekara 10 ina sayar da sassan jikin ɗan Adam — Wanda ake zargi