Aminiya:
2025-11-02@06:25:18 GMT

Gobara ta ƙone shaguna 17 a tsohuwar kasuwar Gombe

Published: 5th, March 2025 GMT

Wata mummunar gobara ta ƙone shaguna sama da 17 a ɓangaren ’yan teloli da masu hada-hadar kayan abinci a tsohuwar kasuwar garin Gombe.

Gobarar, wadda ta fara da misalin ƙarfe 2:00 na dare, ta jefa ’yan kasuwa cikin jimamin asarar dukiya mai tarin yawa da aka kiyasta ta kai miliyoyin naira.

Mijina bai hana ni waƙa ba sai dai… – Fa’iza Badawa Ramadan: Abubuwa goma ga ma’aurata

Wasu da lamarin ya faru a kan idonsu, sun bayyana cewa gobarar ta bazu cikin sauri, inda ta riƙa laƙume kaya da kadarori kafin ’yan kwana-kwana su iso wurin.

Ko da yake ba a tabbatar da musabbabin tashin gobarar ba, amma wasu ’yan kasuwar na zargin cewa matsalar wutar lantarki ce ta haddasa ta.

Wani daga cikin ’yan kasuwar da lamarin ya shafa, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyana bakin cikinsa da cewa, “Mun rasa komai.

“Mutanenmu da dama sun saro kaya a kwanan nan, amma yanzu duk sun ƙone. Wannan babban kalubale ne a gare mu.”

Wakilinmu ya ruwaito cewa jami’an hukumar kashe gobara ta Jihar Gombe tare da gudunmawar wasu mazauna ne suka taimaka wajen hana gobarar bazuwa zuwa wasu sassan kasuwar.

Sai dai, kafin a kashe gobarar gaba ɗaya, tuni ta riga ta yi mummunar ɓarna.

Har yanzu mahukunta ba su fitar da wata sanarwa game da lamarin ba, sai dai shugabannin ’yan kasuwa suna kira ga gwamnati da ta taimaka wa ’yan kasuwar da abin ya shafa.

Sun kuma yi kira da a ɗauki tsauraran matakan daƙile gobara don hana faruwar irin wannan lamari a nan gaba.

Wannan gobarar ta shiga jerin gobarar da suka auku a kasuwannin Gombe a cikin ’yan shekarun nan, lamarin da ya jaddada muhimmancin samar da ingantattun matakan daƙile aukuwarta a wuraren kasuwanci.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gobara jihar Gombe kasuwa

এছাড়াও পড়ুন:

Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini ba — Tinubu

Shugaba Bola Tinubu ya mayar wa da Shugaban Amurka, Donald Trump martani cewa Najeriya ba ta yadda da duk wani nau’in zarafin addini.

Tinubu, ya yi wannan bayani ne bayan Trump ya sake sanya Najeriya cikin jerin ƙasashen da ake kiran “Ƙasashen da ke da Babbar Matsala wajen ’Yancin Addini.”

PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu ’yan tsagin Wike Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura Isa

Trump ya yi iƙirarin cewa Kiristoci a Najeriya na fuskantar barazana, amma ya sha alwashin cewa Amurka za ta kare su.

A cikin wani saƙo da ya wallafa a kafafen sada zumunta, Trump ya rubuta cewa: “Addinin Kirista yana fuskantar babbar barazana a Najeriya. Ana kashe dubban Kiristoci.”

A ranar Asabar, Tinubu ya mayar da martani ta kafar sada zumunta, inda ya ce Najeriya ƙasa ce mai dimokuraɗiyya wadda kundinta ya tabbatar da ’yancin yin addini.

“Najeriya tana da cikakken tanadi a kundinta da ya tabbatar da ’yancin yin addini,” in ji Tinubu.

“Tun daga shekarar 2023, gwamnatina na aiki tare da shugabannin Kiristoci da Musulmai don magance matsalolin tsaro da ke shafar jama’a daga kowane ɓangare da addini.”

Ya ƙara da cewa, kiran Najeriya ƙasa mai matsala wajen gudanar addini ba gaskiya ba ne.

“Za mu ci gaba da kare ’yancin kowane ɗan ƙasa na yin addininsa cikin walwala. Najeriya ba ta goyon bayan zaluncin addini ko kaɗan,” in ji Tinubu.

Ya kuma ce Najeriya za ta ci gaba da haɗa kai da Amurka da sauran ƙasashe domin inganta zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin mabiya addinai daban-daban.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini ba — Tinubu
  • PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu ’yan tsagin Wike
  • PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu da ke da alaƙa da Wike
  • Za mu ci gaba da shirye-shiryen babban taronmu — PDP
  • ’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi
  • Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar
  • Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP
  • Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aure
  • Gwamnatin Gombe ta saurari ra’ayoyin jama’a kan kasafin kuɗin 2026
  • Gobara ta tashi a babban kanti a Abuja