Da wahala City ta yi nasara a gidan Madrid — Guardiola
Published: 18th, February 2025 GMT
Kociyan ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Manchester City, Pep Guardiola, ya ce damarsu ta samun nasara kan Real Madrid ’yar kaɗan ce a yayin da a gobe Laraba ƙungiyoyin biyu za su yi karon-batta a Gasar Zakarun Turai.
Ana iya tuna cewa, a karawar farko da ƙungiyoyin suka yi a Talatar makon jiya, Madrid ce ta je har gida ta lallasa City da ci 3-2, minti huɗu kafin a tashi wasan.
To sai dai gabanin karawar ta biyu da za a yi a filin wasa na Bernabeu, a wasan neman gurbin tsallakawa zagayen ’yan 16, Guardiola ya ce damar da suke da ita kan Madrid kaɗan ce, amma za su yi iya ƙoƙarinsu wajen ganin sun yi amfani da ita.
City dai ta farfaɗo daga dukan da ta sha a hannun Madrid a wasan da ta yi da Newcastle a gasar Firimiyar Ingila, inda ta lallasa ta da ci 4 da nema, lamarin da ya sa a ke ganin wataƙila ta iya sauya sakamakon na Madrid, sai dai Guardiola ya ce ba ya tunanin hakan ta kasance.
A karawar ta gobe dai, ya zama wajibi ɗaya daga cikin manyan ƙungiyoyin biyu ta fice daga Gasar Zakarun Turai ba tare da kai wa zagayen ’yan 16 ba, wanda ke zama karo na farko a cikin shekaru.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gasar Zakarun Turai Pep Guardiola
এছাড়াও পড়ুন:
Iran ta kai sabbin hare-hare birnin Tel Aviv da Haifa
Iran ta kai sabbin hare-hare kan manyan biranen Isra’ila da suka haɗa da Tel Aviv da Haifa, inda ta yi amfani da makaman linzami da jiragen yaƙi marasa matuƙa.
A cewar gidan talabijin na Iran, gomman makamai masu linzami da jirage marasa matuƙa ne suka tashi zuwa Isra’ila, kuma wasu daga cikinsu sun ƙetare garkuwar kariyar iska ta Isra’ila.
An tallafa wa mata 250 da abinci da kayan sana’a a Kaduna Yadda wani ɗan sanda ya rasu a hanyar zuwa ɗaurin aurensaSai dai har yanzu ba a ji wani bayani daga sojojin Isra’ila ba.
Faɗan Iran da Isra’ila ya fara ne bayan Isra’ila ta kai hari kan wani sashen ofishin jakadancin Iran da ke birnin Damascus na Siriya, wanda ya yi sanadin mutuwar wasu manyan jami’an Iran.
Wannan mataki ya tayar da hankalin Iran, inda ta sha alwashin ramawa kuma wannan hari da ta kai yanzu na daga cikin mayar da martani kan harin Isra’ila.