Sojojin HKI Sun Ce Ba Zasu Fita Daga Wurare 5 A Kudancin Kasar Lebanon Ba
Published: 18th, February 2025 GMT
Sojojin HKI Sun Bada sanarwan cewa ba zasu bar wasu tuddai guda 5 a kudancin kasar Lebanon ba, har zuwa wani lokacin da basu sani ba, saboda tsaron haramtacciyar kasar.
Tashar talabijin ta Almayadin ta kasar Lebanon, ta nakalto cewa tankunan yakin HKI sun kutsa cikin garin kafarshuba na kudancin kasar Lebanon kuma sun kafa sansanin sojojin a garin.
A jiya litinin ce yakamata sojojin HKI su fice daga kudancin kasar Lebanon da suka mamaye, amma a jiyan din ne suka bada sanarwan cewa ba zasu fita daga wurare 5 daga kudancin kasar ta Lebanon ba.
Kafin haka bayan kwanaki 60 da tsagaita budewa juna wuta ne, yakamata sojojin HKI su fice daga kudancin kasar ta Lebanon, amma tare da shiga tsakani na gwamnatin kasar Amurka, gwamnatin kasar Lebanon ta tsawaita wanzuwar sojojin yahudawan har zuwa yau Talata 18 ga watan Fabrayrun shekara ta 2025. A yau ne yakamata sojojin kasar Lebanon su karbi dukkan wuraren da sojojin yahudawan suke mamaye da su a kudancin kasar.
Har yanzun dai ba’a ji ta bakin gwamnatin kasar Lebanon dangane da wannan al-amarin.
Mai magana da yawan sojojin HKI sojojinsa ba zasu fita daga wadannan wurare 5 ba sabaoda tsaron HKI kuma a duk lokacinda suka ga mutanensu a yankin arewacin HKI zasu sami amince da zaman lafiya suna iya ficewa daga wadannan wurare.
Kafin haka dai babban sakatarin kungiyar Hizbullah Sheikh Na’im Qasim ya bayyana cewa sojojin HKI basu da wani uzuri na ci gaba da kasancewa a kudancin kasar Lebanon daga yau Talata 18 ga watan Fabrayrun shekara ta 2025
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: a kudancin kasar Lebanon
এছাড়াও পড়ুন:
CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka
Babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na Sin CMG, ya gabatar da labarin ganawar da aka yi jiya Alhamis tsakanin shugabannin Sin da Amurka a Busan na Korea ta Kudu, cikin harsuna 85. Kuma zuwa yau Juma’a, mutanen da suka karanta rahotanni masu alaka da ganawar ta hanyoyin watsa labarai na dandalin CMG sun kai miliyan 712. Haka kuma, kafafen watsa labarai na kasa da kasa 1678, sun wallafa tare da tura rahotanni da bidiyon labaran CMG na harsuna daban daban game da ganawar, har sau 4431.
Har ila yau a wannan rana, an gudanar taron tattaunawa na kasa da kasa kan bude kofa da kirkire kirkire da ci gaba na bai daya a kasar Uruguay, wanda CMG da hadin gwiwar ofishin jakadancin Sin dake kasar suka shirya a Montevideo babban birnin Uruguay. (Mai fassara: FMM)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA