HausaTv:
2025-07-31@12:29:12 GMT

Sojojin HKI Sun Ce Ba Zasu Fita Daga Wurare 5 A Kudancin Kasar Lebanon Ba

Published: 18th, February 2025 GMT

Sojojin HKI Sun Bada sanarwan cewa ba zasu bar wasu tuddai guda 5 a kudancin kasar Lebanon ba, har zuwa wani lokacin da basu sani ba, saboda tsaron haramtacciyar kasar.

Tashar talabijin ta Almayadin ta  kasar Lebanon, ta nakalto cewa tankunan yakin HKI sun kutsa cikin garin kafarshuba na kudancin kasar Lebanon kuma sun kafa sansanin sojojin a garin.

A jiya litinin ce yakamata sojojin HKI su fice daga kudancin kasar Lebanon da suka mamaye, amma a jiyan din ne suka bada sanarwan cewa ba zasu fita daga wurare 5 daga kudancin kasar ta Lebanon ba.   

Kafin haka bayan kwanaki 60 da tsagaita budewa juna wuta ne, yakamata sojojin HKI su fice daga kudancin kasar ta Lebanon, amma tare da shiga tsakani na gwamnatin kasar Amurka, gwamnatin kasar Lebanon ta tsawaita wanzuwar sojojin yahudawan har zuwa yau Talata 18 ga watan Fabrayrun shekara ta 2025. A yau ne yakamata sojojin kasar Lebanon su karbi dukkan wuraren da sojojin yahudawan suke mamaye da su a kudancin kasar.

Har yanzun dai ba’a ji ta bakin gwamnatin kasar Lebanon dangane da wannan al-amarin.

Mai magana da yawan sojojin HKI sojojinsa ba zasu fita daga wadannan wurare 5 ba sabaoda tsaron HKI kuma a duk lokacinda suka ga mutanensu a yankin arewacin HKI zasu sami amince da zaman lafiya suna iya ficewa daga wadannan wurare.

Kafin haka dai babban sakatarin kungiyar Hizbullah Sheikh Na’im Qasim ya bayyana cewa sojojin HKI basu da wani uzuri na ci gaba da kasancewa a kudancin kasar Lebanon daga yau Talata 18 ga watan Fabrayrun shekara ta 2025

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: a kudancin kasar Lebanon

এছাড়াও পড়ুন:

DAGA LARABA: Dalilan al’ummomi na rungumar gwaji kafin aure

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Wasu al’ummomi sun bayyana dalilan da suka sa suka karbi tsarin yin gwajin lafiyar ma’aurata kafin a daura musu aure.

A wasu lokutan, akan samu matsaloli sakamakon rashin gwajin jini kafin a hada mace da na miji aure. Matsalolin sun hada da yaduwar cututtuka, samun ‘ya’ya marasa lafiya da sauran wasu matsalolin.

NAJERIYA A YAU: Yadda Za A Dama Da Matan Arewa A Fannin Kimiyya DAGA LARABA: Abubuwan da ya kamata yara su yi yayin hutun makaranta

Shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi nazari ne kan dalilan da suka sa wasu alummomin suka rungumi yin gwajin jini kafin aure.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Shugaban Kasar Lebanon Aun Ya Ce Mun Aike Wa  Amurka Sakwanni Akan Dakatar Da Hare-haren HKI
  • Sojan Amurka Ya Bada Ruwayar Yadda Sojojin Sahayoniyya Suka Kashe Wani Yaro Balasdine
  • Sojojin Yemen Sun Kai Zafafan Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila Guda Uku  
  • Amurka Ta Ce HKI Ba Zata Fice Daga Kasar Lebanon Ba Sai An Kwance Damarar Hizbullah
  • Siriya Da HKI Zasu Gudanar Da Taro A Baku
  • DAGA LARABA: Dalilan al’ummomi na rungumar gwaji kafin aure
  • Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana
  • Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa
  • Sojojin HKI Sun Ci Gaba Da Kashe Kawunansu
  • Shugaban Kasar Masar Ya Roki Trump Ya Kawo Karshen Yaki A Gaza