An ƙaddamar wa ’yan kasuwa sabon tsarin biyan haraji a Gombe
Published: 6th, February 2025 GMT
A ƙoƙarin bunƙasa tattalin arziƙin Jihar Gombe, Hukumar Tattara Kuɗaɗen Shiga ta jihar, ƙarƙashin jagorancin Hajiya Aisha Adamu, ta ƙaddamar wa ’yan kasuwa sabon tsarin biyan haraji.
An ƙaddamar da tsarin ne a sakatariyar Ƙungiyar ’Yan Kasuwa da ke cikin babbar kasuwar Gombe.
Majalisa na son ƙirƙiro sabbin jihohi 31 a Najeriya An tsinci gawar Ɗan Majalisar da aka yi garkuwa a jajibirin KirsimetiHajiya Aisha ta jinjina wa haɗin kan ’yan kasuwa, musamman, Alhaji Sanusi Abdullahi Mai Rediyo.
Ta ce kuɗaɗen haraji suna da muhimmanci wajen aiwatar da ayyukan raya ƙasa don amfanin al’umma.
Ta yi kira ga ’yan kasuwa da su dage wajen biyan harajinsu na shekara-shekara, wanda kowane mai shago zai biya sau ɗaya kawai.
Hajiya Aisha ta kuma bayyana cewa an samar da hanyoyin biyan haraji masu sauƙi, ciki har da ofisoshin haraji, Intanet, da kuma hedikwatar Hukumar Tattara Kuɗaɗen Shiga.
Shugaban Ƙungiyar ’Yan Kasuwa, Alhaji Sanusi Mai Rediyo, ya tabbatar da cikakken goyon bayansu ga wannan tsari.
Shi ma Sakataren Tsare-tsare na ƙungiyar, Alhaji Sabo Coca Cola, ya jaddada muhimmancin haɗin kai domin cimma burin bunƙasa tattalin arziƙin jihar.
Sabon tsarin biyan harajin zai taimaka wajen ƙara kuɗaɗen shiga na cikin gida tare da inganta ayyukan ci gaba a Jihar Gombe.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: yan kasuwa gwamnati Haraji Sabon Tsari biyan haraji
এছাড়াও পড়ুন:
Iran ta sake kai hare-haren martani kan Isra’ila
Dakarun kare juyin juya halin Musulunci (IRGC) sun kaddamar da wani sabon harin makamai masu linzami da jirage marasa matuka kan Isra’ila a cikin daren jiya Asabar, biyo bayan matakin farko na harin ramuwar gayya na kan harin Isra’ila na ranar Juma’a.
Jim kadan bayan harba makamai masu linzami da jirage marasa matuka, sashen hulda da jama’a na IRGC ya ba da sanarwar kaddamar da wani sabon shiri na manyan makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuka.
Sanarwar ta yi nuni da cewa, sashen kula da sararin samaniya na IRGC ya fara wannan sabon mataki na aikin a matsayin mayar da martani kai tsaye ga sabbin ta’addancin gwamnatin sahyoniyawan.
Babban abin da aka fi mayar da hankali kan wannan sabon farmakin na ‘Operation True Promise III’ an bayar da rahoton cewa, birnin Haifa mai tashar jiragen ruwa ya kunshi muhimman wuraren soji da masana’antu na gwamnatin.
Hare-haren sun shafi wasu muhimman cibiyoyin soji da masana’antu na Isra’ila, da suka hada da matatun mai da na wutar lantarki a Haifa, inda aka ce gobara ta tashi a sanadiyar haka.
Daya daga cikin faifan bidiyon ya nuna wata gagarumar gobara da ta tashi a matatar mai ta Haifa bisa tasirin da manyan makamai masu linzami na Iran suka yi, wanda ya haskaka sararin samaniyar yankunan da aka mamaye.