Aminiya:
2025-09-18@10:00:57 GMT

Malamai sun fara yajin aiki a Ebonyi

Published: 6th, February 2025 GMT

Ƙungiyar Malamai ta Najeriya NUT reshen Jihar Ebonyi ta sanar da fara yajin aikin sai baba-ta-gani a ƙananan hukumomi bakwai na jihar sakamakon rashin biyan albashin watanni.

Yankunan da abin ya shafa sun haɗa da: Ebonyi, Edda, Ezza South, Ezza North, Ivo, Ishielu da Ƙaramar Hukumar Ohaukwu.

Mutuwar Almajirai: Tinubu ya buƙaci a samar da matakan kare ɗalibai Uwa ta fusata ta jefa ’yarta cikin kogi a Bayelsa

Ƙungiyar ta koka kan rashin biyan albashin sama da watanni uku ga malaman da ke Ƙananan hukumomin da abin ya shafa.

Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun sakataren ƙungiyar, Bassey Asuquo kuma aka rabawa manema labarai a Abakiliki babban birnin jihar a ranar Alhamis.

Sanarwar ta ci gaba da cewa: “Bayan sanarwar da muka bayar a baya kan shirin fara yajin aikin, mun yi nazari sosai kan yadda shugabannin ƙananan hukumomi suka amince da biyan albashin mambobinmu.

“Ya zuwa ranar aiki ta Laraba, 5 ga Fabrairu, 2025, mun amince da cewa wasu ƙananan hukumomi sun biya albashin mambobinmu.

“Duk da haka, muna nadamar sanar da ku cewa shugabannin ƙananan hukumomi da dama sun gaza biyan kuɗaɗen albashin mambobinmu.

“A kan haka, an umurci dukkan mambobinmu na jihar da na reshen ƙananan hukumomin da abin ya shafa da su bi wannan umarni da kuma tabbatar da aiwatar da yajin aikin nan take daga ƙarfe 12:00 na daren ranar Alhamis 6 ga Fabrairu, 2025.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu Ya Jajantawa Iyalai Wadanda Gobara Ta Shafa A FIRS, UBA Da United Capital

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana matukar alhininsa kan asarar rayuka da aka yi a gobarar da ta tashi a ranar Talata a Afriland Towers da ke Broad Street, a  Legas.

 

A cikin wata sanarwa da mai baiwa shugaban kasa shawara kan yada labarai, Bayo Onanuga ya fitar, ya ce shugaba Tinubu ya jajantawa iyalan wadanda abin ya shafa, da kuma hukumomi da ma’aikatan hukumar tara haraji ta tarayya (FIRS), United Capital, United Bank for Africa (UBA) Plc, da kuma Afriland Properties Limited.

 

Ya kuma jajanta wa wadanda suka rasa ‘yan uwansu a wannan bala’in, tare da yi wa wadanda suka jikkata fatan samun sauki cikin gaggawa.

 

Shugaba Tinubu ya yaba da matakin da hukumomin gaggawa suka dauka da suka hada da hukumar kashe gobara ta tarayya, da masu bayar da agajin gaggawa, da kungiyoyin likitoci, da sauran jama’a, wadanda suka taimaka wajen kwashe mutanen daga ginin da lamarin ya shafa a kan lokaci.

 

Yayin da yake ba da shawarar yin taka tsantsan, horarwa, da kuma taka tsan-tsan don hana afkuwar irin haka nan gaba, shugaban ya yi addu’ar Allah ya jikan wadanda suka rasu, ya kuma yiwa iyalan wadanda suka rasa rayukansu ta’aziyya.

 

Bello Wakili

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Jajantawa Iyalai Wadanda Gobara Ta Shafa A FIRS, UBA Da United Capital
  • Gwamnatin Tarayya ta raba wa talakawa N330bn — Ministan Kuɗi
  • ’Yan bindiga sun sako ma’auratan da suka sace a Katsina bayan biyan N50m
  • Kwara ETF Ya Dauki Nauyin Karatun Fitattun Dalibai A Matakin Sakandare
  • An tattauna yadda za a inganta walwalar malamai a Gombe
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima
  • Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo
  • Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
  • Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja