Malamai sun fara yajin aiki a Ebonyi
Published: 6th, February 2025 GMT
Ƙungiyar Malamai ta Najeriya NUT reshen Jihar Ebonyi ta sanar da fara yajin aikin sai baba-ta-gani a ƙananan hukumomi bakwai na jihar sakamakon rashin biyan albashin watanni.
Yankunan da abin ya shafa sun haɗa da: Ebonyi, Edda, Ezza South, Ezza North, Ivo, Ishielu da Ƙaramar Hukumar Ohaukwu.
Mutuwar Almajirai: Tinubu ya buƙaci a samar da matakan kare ɗalibai Uwa ta fusata ta jefa ’yarta cikin kogi a BayelsaƘungiyar ta koka kan rashin biyan albashin sama da watanni uku ga malaman da ke Ƙananan hukumomin da abin ya shafa.
Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun sakataren ƙungiyar, Bassey Asuquo kuma aka rabawa manema labarai a Abakiliki babban birnin jihar a ranar Alhamis.
Sanarwar ta ci gaba da cewa: “Bayan sanarwar da muka bayar a baya kan shirin fara yajin aikin, mun yi nazari sosai kan yadda shugabannin ƙananan hukumomi suka amince da biyan albashin mambobinmu.
“Ya zuwa ranar aiki ta Laraba, 5 ga Fabrairu, 2025, mun amince da cewa wasu ƙananan hukumomi sun biya albashin mambobinmu.
“Duk da haka, muna nadamar sanar da ku cewa shugabannin ƙananan hukumomi da dama sun gaza biyan kuɗaɗen albashin mambobinmu.
“A kan haka, an umurci dukkan mambobinmu na jihar da na reshen ƙananan hukumomin da abin ya shafa da su bi wannan umarni da kuma tabbatar da aiwatar da yajin aikin nan take daga ƙarfe 12:00 na daren ranar Alhamis 6 ga Fabrairu, 2025.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Da Alamu Amurka Ta Fara Dandana Kudarta
Kamar yadda Sin da masana suka sha fada, mummunan matakin na Amurka, zai fi yi mata illa maimakon kasashen da take neman cin zalinsu.
Tabbas Sin ta yi gaskiya da ta ce bayar da kai ko ja da baya, dama ce ga mai cin zali. Don haka, Sin ta yi daidai da ta tsaya haikan wajen mayar da martani ba tare da bada kai ba, domin Amurka ta gane kuskurenta, kana ta fahimci cewa, lokaci ya wuce da za a rika biye mata tana yin abun da ta ga dama.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp