Aragchi Ya Tattauna Da Bin Salman Kan Karfafa Zumunci Tsakanin Kasashen Biyu
Published: 10th, July 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya tattaunawa da Firay minister da kuma yerma mai jiran gadon sarautar kasar Saudiya Mohammad bin Salman kan karfafa dankon zumuncim tsakanin kasashen biyu da kuma abubuwan da ke faruwa a yankin.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran Aragchi ya hadu da dan sarkin ne a Makka, a ranar talata , kafin haka ministocin harkokin wajen kasashen biyu wato Faisal Bin Farhan kan wadan nan batutuwan.
Bin salman dangane rikicin da ke faruwa tsakanin Iran da HKI da kuma Amurka, y ace yana fatan karshensa ya zama mai samar da zaman lafiya a mai dorewa a yankin.
A nashi bangaren ministan harkokin wajen kasar Iran ya fadawa Bin salman kan cewa kasar Iran ta gode da yadda gwamnatin saudiya ta yi allawadai da hare-haren da HKI ta kaiwa Iran a yakin 12 da suka fafata.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa
Shi ma Uban taro mai masaukin baki, shugaban kasar Brazil Luiz Inacio Lula da Silva ya bayyana a jawabinsa na taron kolin cewa, “Idan har ba a samu sauyi a tsarin gudanar da harkokin kasa da kasa a wannan karni na 21 ba, to ya zama wajibi kasashen BRICS su taimaka wajen ganin an sabunta shi.”
BRICS taska ce ta hadin kai, daidaito da kuma kokarin tafiya tare don samun ci gaba da tsira tare, da kuma karfafawa kasashe masu neman ‘yancin fadin albarkacin bakinsu a harkokin tsare-tsare na hadin kan kasashen duniya.
Taron kolin kungiyar na bana, na zuwa ne a daidai lokacin da kasuwannin duniya ke cike da firgici biyo bayan yakin cinikayya da kasar Amurka ta kaddamar, amma BRICS ta tsaya tsayin daka wajen inganta harkokin tattalin arziki, inda kungiyar ke samar da wani dandali na bai daya da ke tallafawa cinikayya a kasashe daban-daban, da inganta cinikayyar a tsakaninsu, wanda hakan ya ba su damar bunkasa amfani da kudaden cikin gida, don rage dogaro kan wasu kasuwanni masu iyaka.
Yayin da kasashe da dama ke nuna sha’awar shiga kungiyar, hakan na nuni da tasiri da nasarar da kungiyar ke samu cikin sauri, saboda ta bayyana gaskiya da adalci a fili, ta inganta tsarin dimokuradiyyar duniya, kowa yana da ‘yancin fadi a ji.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp