Labaran da suke fitowa daga kasar Yemen sunn bayyana cewa sojojin ruwan kasar sun nutsar da wani karin tankar dakon mai mallakin HKI a cikin tekun Red sea. Sojojin kasar sun bayyana cewa jigin ya sabawa Haramcin don haka sun tsutsar da ita. Sun yi haka ne don nuna goyon bayansu ga al-ummar Falasdinu wadanda ake zalinta a Gaza.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa jirgin yana nufin zuwa ummu Rash Rash ko Ilat kamar yadda yahudawan suke kiransa.

Sojojin kasar Yemen sun kara da cewa sun dauki wannan matakin kan jirgin ne bayan an gargade shi da ya koma amma yaki sauraro. Da wannan talilin sojojin ruwa na kasar yemen suka yi amfani da jiragen da ake sarrafasu daga nesa suka kaiwa jirgin mai suna ;ETERNITY C hare-hare sun tare da amfani da makamai masu linzami  samfurin har  ya nutse a cikin ruwa.

Labarin ya kara da cewa basu kashe wani ba, sai dai sun kama masu aiki a jirgin zu raka su zuwam kan tudu.

Labarin ya kammala da cewa wannan halin zai ci gaba har zuwa lokacin da HKI zata daina kissan Falasdinawa a Gaza.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Hizbullah Ta Yi Allawadai Da Harin HKI A Kasar Yemen

A yau Litinin ne kungiyar ta Hizbullah ta fitar da sanarwa wacce ta kunshi yin Allawadai da harin ta’addancin da HKI ta kai wa kasar Yemen, wanda ya shafi tasoshin jiragen ruwa da muhimmacin cibiyoyin kasar.

Bayanin na Hizbullah ya kuma ce; Makiya suna tsammanin cewa ta hanyar wannan irin harin na wuce gona da iri za su yi hana Yemen ci gaba da matakin da take dauka na daukaka wajen taimakawa Gaza, ta daina kai hare-hare masu tsanani da take kai musu.

Haka nan kuma Hizbullah ta ci gaba da cewa: Har yanzu ‘yan sahayoniya sun kasa fahimtar dabi’ar mutanen Yamen masu hakuri da juriya akan tafarkin jihadi, domin akida ce, cewa gaskiya ita ce wacce ta cancanci a yi biyayya a gare ta, haka nan kuma kare wadanda aka zalunta.”

Kungiyar ta Hizbullah ta kuma kara da cewa; Matsayar da mutane Yemen jagorori da al’umma suke dauka, ya samo asali ne daga koyarwar Imam Hussain ( a.s) wanda ba yi sassauta akan gaskiya ba, wajen kalubalantar dawagitai.”

Kungiyar ta Hizbullah ta kara da cewa; Abokan gaba ba za su cimma manufarsu ba, kuma kamar yadda a baya Amurka ta ci kasa akan Yemen, ita ma Isra’ila makomarta kenan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Manazaecin Kasar Amurka Ya Ce; Isra’ila Ta Sha Kashi A  Yakinta Da Jamhuriyar Musulunci Ta Iran
  • Zagaye na 5 A Tattaunawar Gaza da HKI  Ya tashi ba tare da Sun Dai-daita ba A Doha
  • Sojojin Yemen Sun Nutsar Da Jirgin Ruwan “Eternity” Dake Hanyar Zuwa HKI
  • HKI: Sojoji 62 Ne Su Ka Halaka A Gaza A Cikin Wannan Shekara Ta 2025
  • Kasar Yemen Ta Bayyana ‘Yancin Kowa Na Walwala A Teku Amma Ban Da ‘Yan Sahayoniyya Azzalumai
  • Hizbullah Ta Kasar Lebanon Ta Godewa JMI Dangane Da Tallafawa Kungiyar Saboda Gwagwarmaya Da HKI
  • Kakakin Rundunar Izzuddeen Qassam ya Bayyana Yadda Suka Yi Kofar Rago Ga Sojojin Mamayar Isra’ila
  • NAJERIYA A YAU: Sarkakiyar Dake Gaban Hadakar ADC — Atiku Ko Peter Obi
  • Hizbullah Ta Yi Allawadai Da Harin HKI A Kasar Yemen