Aminiya:
2025-07-31@12:24:45 GMT

Ahmad Lawan ya raba tallafin N27m da buhun shinkafa 300 a Yobe

Published: 27th, March 2025 GMT

Tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Ahmad Lawan, ya bayar da gudummawar Naira miliyan 27 da buhunan shinkafa 300 ga mutanen da gobara ta shafa a ƙananan hukumomi uku da ke mazaɓarsa a Jihar Yobe.

Ƙananan hukumomin da abin ya shafa sun haɗa da Machina, Nguru, da Yusufari.

An kama mutum 3 kan zargin sata da ƙone gidan bature a Gombe Tsohon hadimin gwamnan Kano, Abdullahi Tanka Galadanci, ya rasu

Sanata Lawan, ya jajanta wa mutanen da suka yi asarar dukiya sakamakon gobarar.

Ya ce haƙƙinsu ne su taimaka wa juna, kuma zai ci gaba da ƙoƙari don ganin cewa wadanda abin ya shafa sun samu tallafin da ya dace.

Ya bayyana cewa wannan tallafin zai ƙara ƙaimi ga ƙoƙarin da gwamnatin jihar ke yi na samar da agajin gaggawa ga mutanen da abin ya shafa, tare da taimaka musu, su farfaɗo daga ɓarnar da gobarar ta yi musu.

A cewarsa, an ware Naira miliyan 12 da buhunan shinkafa 150 ga Ƙaramar Hukumar Machina, wanda za a raba a garuruwan Ngabarawa, Dole, Ghana, da Damai.

Ƙaramar Hukumar Nguru, za ta karɓi Naira miliyan biyar da buhunan shinkafa 50, wanda za a raba wa al’ummar Askema da Mirba.

Ƙaramar Hukumar Yusufari, za ta samu Naira miliyan 10 da buhunan shinkafa 100, wanda za a raba wa mutanen Tulo-Tulo da Isufuri.

Sanata Lawan, ya buƙaci gidauniyar SAIL Foundation, wacce ke kula da rabon tallafin, da ta tabbatar da gaskiya da adalci wajen raba wa waɗanda suka cancanta.

Ya kuma yi addu’a Allah Ya ba waɗanda abin ya shafa ikon jure wannan jarabta da sauƙi a gare su, musamman a wannan wata mai alfarma na Ramadan.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gobara Sanata Ahmed Lawan da abin ya shafa Naira miliyan

এছাড়াও পড়ুন:

Tallafin matar Tinubu na N1bn ga ’yan gudun hijirar Binuwai ya bar baya da kura

Da alama tallafin da matar Shugaban Kasa, Sanata Remi Tinubu ta ba wadanda hare-haren jihar Binuwai ya raba da muhallansu na Naira biliyan daya ya bar baya da kura.

Kwana daya da bayar da tallafin, ’yan gudun hijirar sun fito suna zanga-zangar yunwa, amma kakakin hukumar bayar da agaji ta jihar (SEMA), Terna Ager, ya ce musu kudin ba na sayen abinci ba ne.

Remi Tinubu ta bai wa waɗanda harin Benuwe ya shafa tallafin Naira biliyan ɗaya Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya

Aminiya ta rawaito yadda Sanata Remi a ranar Talata ta ziyarci jihar inda ta mika wa Gwamnan Jihar, Hyacinth Alia tallafin kudin, a madadin ’yan gudun hijirar.

To sai dai kwana daya bayan hakan, sai wasu daga cikin ’yan gudun hijirar suka fantsama a kan tituna suna zanga-zangar yunwa da zargin masu kula da sansanin da gallaza musu tun da suka tare a can.

Mutanen dai sun tare babbar hanyar Makurdi zuwa Lafiya suna rera wakoki irin su “Gida muke so mu koma,” “Yunwa ta dame mu” da kuma “Matanmu na rasa ’ya’yansu suna yin bari”.

Daya daga cikin matan mai suna Rebecca Awuse, ta shaida wa ’yan jarida cewa, “Yunwa ta ishe mu. Ba mu da abinci, ba muhalli, ba magani sannan ba kulawar lafiya. ’Ya’yanmu na mutuwa da yunwa. Mata da yawa sun yi bari saboda yanayin da suke ciki sannan a kasa muke kwana.

Sai dai da yake mayar da martini, Terna Ager, ya yi zargin cewa akwai wata boyayyar manufar siyasa a zanga-zangar.

A cewarsa, “Babu dalilin da zai sa su yi wannan zanga-zangar sam. Wadanda ke sansanin Yelwata wani lokacin sukan koma sansanin Makurdi an fi samun tallafin abinci a can.

“Tallafin da matar Shugaban Kasa ta bayar na sake tusgunar da su ne ba wain a sayen abinci a raba musu ba ne. Kuma hakan ma yana daukar lokaci.

“Na yi imanin suna zanga-zangar ce saboda suna tunanin za a debi kudin kawai a raba musu, amma ba haka ba ne dalili,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Sandan Niger Sun Hada ‘Yan’uwa Mutanen 35 Da Aka Ceto Da Iyalansu 
  • Tallafin matar Tinubu na N1bn ga ’yan gudun hijirar Binuwai ya bar baya da kura
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Tallafin Miliyoyin Naira Ga Ƴan NURTW da Mahauta a Jigawa
  • Shugaban Hukumar Zaɓe Ta Bauchi, Ahmad Makama, Ya Rasu
  • Shugaban SUBEB Yayi Alkawarin Bayar Da Tallafin Ilimi A Jihar Nasarawa
  • Remi Tinubu ta bai wa waɗanda harin Benuwe ya shafa tallafin Naira biliyan ɗaya
  • An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa
  • Remi Tinubu ta ba da tallafin Naira biliyan ɗaya ga waɗanda harin Benuwe ya shafa
  • Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar
  • Mutum miliyan 1.2 na fama da ciwon hanta a Kano