Tinubu ne ya buɗe wa Buhari ƙofar zama shugaban ƙasa — Hadimi
Published: 10th, July 2025 GMT
Hadimin Shugaban Ƙasa, Bola Tinubu, kan Harkokin Yaɗa Labarai, Temitope Ajayi, ya mayar wa tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya, Boss Mustapha martani, kan cewa Tinubu bai taimaka wa tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ba wajen zama shugaban ƙasa a 2015.
Ajayi, ya ce Buhari yana da ƙarfi sosai a Arewa amma hakan bai hana shi faɗuwa zaɓukan 2003, 2007 da 2011 ba.
Ya bayyana cewa a zaɓen fidda gwanin jam’iyyar APC da aka yi a 2014, Tinubu ne, ya taka muhimmiyar rawa wajen ganin Buhari ya lashe.
Ya ce Tinubu ne ya shawo kan gwamnonin APC da wakilan Kudu maso Yamma su mara wa Buhari baya a lokacin zaɓen da aka yi a filin wasa na Teslim Balogun a Legas.
Ya ce ba don wannan goyon baya ba, da Buhari bai samu tikitin takarar shugaban ƙasa ba.
Ajayi, ya ce bai dace a raina ƙoƙarin Tinubu da sauran waɗanda suka taimaka wa Buhari ba.
Ya ce Boss Mustapha bai faɗi gaskiyar abin da ya faru ba.
“Mu bar maganar babban zaɓen da Buhari ya lashe. Ai da bai zama ɗan takara a jam’iyyar APC ba, da ba zai taɓa zama shugaban ƙasa ba.
“Kuma da babu goyon bayan Tinubu a zaɓen fidda gwanin APC da aka yi a Legas a 2014, da Buhari bai lashe ba.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ajayi Buhari Siyasa
এছাড়াও পড়ুন:
Tsohon Ɗan Takarar Gwamna A CPC, Haruna Sa’eed Kajuru, Ya Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Binciki Kisan ‘Yan Zariya A Filato
Tsohon ɗan takarar gwamna ƙarƙashin jam’iyyar CPC ta shuɗe a Jihar Kaduna, Alhaji Haruna Sa’eid Kajuru, ya bukaci Gwamnatin Tarayya ta gudanar da cikakken bincike kan kisan da aka yi wa wasu mazauna Zariya da suka je dauren aure a Jihar Filato kwanan nan.
Alhaji Kajuru ya yi wannan kira ne a lokacin da ya kai ziyara ta jaje ga iyalan waɗanda suka rasa ‘yan uwansu a Zaria, inda ya nuna alhini da ta’aziyya ga dangin waɗanda wannan al’amari ya shafa.
Tsohon Akanta Janar na Jihar Kaduna, Alhaji Haruna Kajuru, ya yi Allah-wadai da kisan, yana mai jaddada cewa babu wani mutum ko ƙungiya da ke da ikon da kundin tsarin mulki ya ba shi na kashe wani ɗan ƙasa.
Ya ce dole ne a kama masu hannu a kisan kuma a gurfanar da su a gaban shari’a domin hakan ya zama izina ga sauran mutane.
“Kundin tsarin mulki bai amince da kisan wani ɗan ƙasa ba. Dole ne mu tsaya tsayin daka wajen ganin an tabbatar da doka da oda a kasa,” in ji shi.
Alhaji Haruna Sa’eid Kajuru, wanda shi ne tsohon ɗan takarar gwamna na CPC a Jihar Kaduna, ya kuma yi kira ga gwamnatocin tarayya da na Jihar Kaduna su tallafa wa iyalan da abin ya shafa, domin rage musu raɗaɗin rashin ‘yan uwa da masu ciyar da su.
Kazalika, ya yi kira ga ‘yan Najeriya da su ci gaba da zauna lafiya da juna, yana mai cewa zaman lafiya da haɗin kai su ne ginshiƙan ci gaban tattalin arziki da zamantakewar al’umma.
Kisan da aka yi a Jihar Filato ya janyo tashin hankali da kiraye-kiraye daga sassa daban-daban na ƙasa kan buƙatar ƙara tsaro da tabbatar da adalci a cikin al’ummomin da abin ya shafa.
Rel: Adamu Yusuf