Aminiya:
2025-09-18@02:18:14 GMT

Tinubu ne ya buɗe wa Buhari ƙofar zama shugaban ƙasa — Hadimi

Published: 10th, July 2025 GMT

Hadimin Shugaban Ƙasa, Bola Tinubu, kan Harkokin Yaɗa Labarai, Temitope Ajayi, ya mayar wa tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya, Boss Mustapha martani, kan cewa Tinubu bai taimaka wa tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ba wajen zama shugaban ƙasa a 2015.

Ajayi, ya ce Buhari yana da ƙarfi sosai a Arewa amma hakan bai hana shi faɗuwa zaɓukan 2003, 2007 da 2011 ba.

Isra’ila ta kashe Falasdinawa 24 a Zirin Gaza NAJERIYA A YAU: Abin Da Ya Sa ’Yan Najeriya Ba Sa Cin Kifi Yadda Ya Kamata

Ya bayyana cewa a zaɓen fidda gwanin jam’iyyar APC da aka yi a 2014, Tinubu ne, ya taka muhimmiyar rawa wajen ganin Buhari ya lashe.

Ya ce Tinubu ne ya shawo kan gwamnonin APC da wakilan Kudu maso Yamma su mara wa Buhari baya a lokacin zaɓen da aka yi a filin wasa na Teslim Balogun a Legas.

Ya ce ba don wannan goyon baya ba, da Buhari bai samu tikitin takarar shugaban ƙasa ba.

Ajayi, ya ce bai dace a raina ƙoƙarin Tinubu da sauran waɗanda suka taimaka wa Buhari ba.

Ya ce Boss Mustapha bai faɗi gaskiyar abin da ya faru ba.

“Mu bar maganar babban zaɓen da Buhari ya lashe. Ai da bai zama ɗan takara a jam’iyyar APC ba, da ba zai taɓa zama shugaban ƙasa ba.

“Kuma da babu goyon bayan Tinubu a zaɓen fidda gwanin APC da aka yi a Legas a 2014, da Buhari bai lashe ba.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ajayi Buhari Siyasa

এছাড়াও পড়ুন:

DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu

Hukumar Tsaron Farin Kaya a Nijeriya DSS, ta gurfanar da fitaccen ɗan gwagwarmayar nan, Omoyele Sowore a kotu.

A ƙunshin ƙarar da DSS ta gabatar a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, ta haɗa da shafukan sada zumunta na X da kuma Facebook, inda take zarginsu da ba da ƙofar aibata Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Bida Poly ta sa sojoji kula da jarrabawar ɗalibai Kukan al’umma kan lalacewar hanyar Dukku

Darekan shigar da ƙara na Ma’aikatar Shari’a ta Tarayya, M.B Abubakar da wasu lauyoyi huɗu —M.E. Ernest da U.B. Bulla da C.S. Eze da kuma E.G. Orubor, ne suka shigar da ƙarar a madadin Gwamnatin Tarayya da kuma hukumar ta DSS.

DSS wadda ta kafa hujja da sashe na 24 da ke cikin kundin dokokin yanar gizo, ta ce Sowore ya yi amfani da shafukansa na dandalan sada zumunta na X da Facebook wajen wallafa wani saƙo da ke cin mutuncin Shugaba Tinubu.

Tun dai a farkon watan nan ne DSS ta buƙaci goge wani saƙo da ɗan gwagwarmayar ya wallafa wanda ta riƙa a matsayin bayanan ƙarya, cin zarafi ta yanar gizo da kalaman haddasa ƙiyayya, waɗanda kuma ta ce na iya haddasa rikici su kuma ɓata sunan Najeriya a ƙasashen waje.

Sai dai har zuwa ranar Litinin, 15 ga watan Satumba, babu wani mataki da aka ɗauka na goge saƙon da DSS ɗin ta buƙata.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • Tinubu ya janye dokar ta-ɓaci da ya sanya a Ribas
  • Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu
  • Ana zargin mace da kashe ’yar uwarta a kan N800 din barkono
  • An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos
  • DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu
  • Tawagar Yan Wasan Damben Gargajiya Ta Iran Ta Zama Zakara A Damben Ta Duniya
  • Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 
  • Peter Obi ya kai wa Obasanjo ziyara