Darakta a ofishin lura da harkokin waje na kwamitin kolin JKS, kuma ministan harkokin wajen kasar Wang Yi, ya gana da mataimakin shugaban kwamitin kasa na Amurka mai lura da alakar Sin da Amurka Evan Greenberg.

Yayin da suke zantawa a yau Laraba, Wang ya jinjinawa Greenberg, bisa tsawon lokaci da ya shafe yana ingiza tattaunawa, da hadin gwiwa tsakanin bangaren Sin da na Amurka, yana mai fatan kwamitin kasa na Amurka mai lura da alakar Sin da Amurka, da sauran kwararru daga dukkanin fannonin rayuwa na Amurka, za su bayar da sabbin gudummawa don wanzar da daidaito, da tabbatar da kyakkyawar alakar Sin da Amurka yadda ya kamata.

A nasa bangare kuwa, mista Greenberg ya ce alakar Sin da Amurka ita ce mafi muhimmanci tsakanin alakokin wasu kasashe 2 na duniya. Don haka ya dace sassan biyu su yi amfani da kwarewa da basirarsu, wajen inganta fahimtar juna, da fadada hadin gwiwa da zaman jituwa. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: alakar Sin da Amurka

এছাড়াও পড়ুন:

Dokta Bashir ya zama shugaban Majalisar Shari’ar Musulunci ta Nijeriya

Majalisar Shari’ar Musulunci ta Najeriya ta naɗa Sheikh Bashir Aliyu Umar a matsayin shugabanta bayan rasuwar Sheikh AbdulRasheed Hadiyyatullah.

Wata sanarwa da majalisar ta fitar a yau Laraba ta ce an amince da shuagabancin Dokta Bashir ne kai-tsaye saboda kasancewarsa mataimakin shugaba.

A ranar Litinin ne Sheikh Hadiyyatullah ya rasu yana da shekara 81 a Jihar Osun.

“Nan gaba za a sanar da mataimakin shugaban,” in ji sanarwar da Nafiu Baba Ahmed ya sanya wa hannu a matsayin sakataren majalisar.

Sheikh Bashir sanannen malami ne kuma shi ne babban limamin masallacin Juma’a na Al-Furqan da ke Alu Avenue a Unguwar Nasarawa ta Jihar Kano.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Najeriya Wajen Yin Watsi Da Kariyar Cinikayya Da Yin Adawa Da Danniya Da Cin Zarafi
  • Dokta Bashir ya zama shugaban Majalisar Shari’ar Musulunci ta Nijeriya
  • Xi Ya Jaddada Muhimmancin Tsara Nagartaccen Shirin Raya Tattalin Arziki Da Zamantakewar Al’umma Tsakanin 2026-2030
  • Riza’i: Babu Hannun  Waje A Cikin Hatsarin Da Ya Faru A Tashar Ruwa Ta Shahid Raja’i
  • Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Binciken Yawaitar Haɗurran Tankokin Man Fetur A Nijeriya 
  • Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
  • Hajjin 2025: Gwamna Namadi Ya Nada Sarkin Kazaure Amirul Hajj
  • Sin Na Maraba Da Karin Abokai Daga Kasa Da Kasa Su Ziyarci Kasar
  • Tawagar Jami’ai Da ‘Yan Kasuwar Ta Tunusiya Ta Gana Da Mataimakin Shugaban kasar Iran
  • Takht Ravanji: Iran Ba Za Ta Taba Yin Tattaunawa Akan Dakatar Da Tace Sanadarin Uranium Ba