Yara miliyan 5.4 na fama da karancin abinci a jihohin arewa 9 – Red Cross
Published: 9th, July 2025 GMT
Kungiyar bayar da agaji ta kasa da kasa ta Red Cross ta ce akwai yara akalla miliyan biyar da dubu 400 da ke fama da matsalar karancin abinci a jihohi tara na arewacin Najeriya da ke fama da matsalar tsaro.
A cewar kungiyar, jihohin su ne Borno, Adamawa, Yobe, Sokoto, Katsina, Zamfara, Neja, Binuwai da kuma Kano.
Mai rikon mukamin Darktan Lafiya da Kula na kungiyar Dr Aminu Abdullahi, shi ne ya bayyana hakan a yayin taron gangamin neman tallafi kan karancin abinci na kungiyar na shiyyar Arewa maso Yamma da ya gudanar a Kano ranar Talata.
Kwanan nan gwamnati za ta sake kara kudin lantarki a Najeriya – Minista Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikaciyar ofishin jakadancin Ghana a AbujaYa ce daga cikin adadin, akalla yara miliyan daya da dubu 900 ne kuma ke fama da matsanancin karancin abincin, yana mai bayanin cewa akwai alaka mai karfi tsakanin rashin tsaro da karancin abinci.
Dr Aminu ya ce, “Munahimci cewa yaduwar cutar yunwa da sauran cututtuka kamar su maleriya da amai da gudawa da kuma kalubalen tsaro a wasu sassa na Najeriya, ya zama wajibi a dauki matakan kariya da kuma wayar da kan jama’a ta hanyar hada kai da mutane domin lalubo bakinn zaren.
“Duk inda ake da matsalar tsaro, mutane kan kyale gonakinsu su bar yankunan. Sannan mutane da dama sun rabu da muhallansu sun koma ’yan gudun hijira a wasu wuraren. To duk lokacin da aka raba ka da hanyar samun abinci, akwai barazanar fuskantar matsalar yunwa.
“Sannan ba wai iya maganar abinci kawai ake ba, magana ce ta abinci main gina jiki da kuma ruwan sha mai tsafta,” in ji shi.
Shi ma shugaban kungiyar na Najeriya, Prince Oluyemisi Adetayo Adeaga, ya ce karancin abinci babbar cuta ce da ke bukatar agajin gaggawa saboda kada ta ta’azzara.
“Idan ka je asibitocin gwamnati da na masu zaman kansu, za ka ga yadda jama’a ke tururuwar zuwa saboda cututtukan da ke da alaka da yunwa. Hakan na da barazana ga dan Adam da ci gaban kasa,” in ji shugaban.
Shi ma shugaban kungiya a Kano, Barista Salisu Sallama, ya ce kodayake jihar ba ta da yawan masu fama da cutar idan aka kwatanta da takwarorinta, amma akwai barazana idan aka yi la’akari da halin da ake ciki da zai iya ta’azzara matsalar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: karancin abinci yunwa karancin abinci
এছাড়াও পড়ুন:
Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan
Shugaban Masar Abdel Fattah al-Sisi ya gana da Shugaban Eritrea Isaias Afwerki domin tattauna halin da ake ciki a yankin, Shugaba al-Sisi ya tabbatar da jajircewar Masar wajen tallafawa ‘yancin kai da kuma ‘yancin yankin Eritrea.
A yayin taron, wanda Ministan Harkokin Wajen Masar Badr Abdel-Aty da takwaransa na Eritrea, Osman Saleh Mohammed suka halarta, shugabannin biyu sun tattauna halin da ake ciki a yankin.
Sun tabbatar da hangen nesansu kan hanyoyin kawo karshen yakin a Sudan, suna masu jaddada bukatar tallafawa cibiyoyin gwamnati na kasa, musamman Sojojin Sudan, tare da kin amincewa da duk wani yunkuri na kafa hukumomi ko cibiyoyi masu kishiyantar gwamnati a kasar.
Shugaba al-Sisi ya jaddada matsayar Masar da kuma kokarin da take yi don kawo karshen yakin da kuma rage wahalhalun jin kai na al’ummar Sudan, ta hanyar yin aiki tare da abokan huldar Masar don tabbatar da hadin kan Sudan, mutuncin yankin, da kuma ‘yancin kan kasa.
A nasa bangaren, Shugaba Afwerki ya nuna matukar godiyarsa ga rawar da y ace Masar tana takawa karkashin jagorancin Shugaba El-Sisi, wajen karfafa zaman lafiya da kuma kokarin ci gaban yankin kusurwar Afirka da Gabashin Afirka. Ya yi maraba da fadada hadin gwiwar tattalin arziki da Masar da kuma karfafa hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu kan batutuwan kasa da kasa da na yanki masu amfani ga junansu.
Taron ya kuma yi magana kan sabbin abubuwan da suka faru a Somaliya, inda Shugabannin biyu sun jaddada kudurin kasashensu na amincewa da sanarwar hadin gwiwa da aka fitar a taron kolin Masar, Eritrea, da Somaliya a Asmara a watan Oktoban 2014, wanda ya tabbatar da wajibcin girmama ka’idoji da dokokin kasa da kasa, musamman ma cikakken yankin Somaliya da dukkan kasashen yankin.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Shugaban Lebanon Ya Umarci Sojoji Da Su Fuskanci Kutsen Na Isra’ila A Kudancin Kasar October 31, 2025 Madagascar Ta Sanar da Kafa Sabuwar Gwamnati Tare da Manyan ‘Yan Adawa October 31, 2025 Iran ta yi fatali da kalamman IAEA Kan Shirin Nukiliyarta October 30, 2025 Trump Ya Umarci Ma’aikatar Yakin Amurka Ta koma gwajin makaman nukiliya October 30, 2025 Isra’ila ta amince da fadada matsugunai a Yammacin Kogin Jordan October 30, 2025 Gaza: hare-haren Isra’ila sun kashe mutane 100 Cikin Kwanaki Biyu October 30, 2025 Sudan : Kasashen duniya na tir da cin zarafi a El-Fasher October 30, 2025 Iran Ta Jaddada Bin Hanyar Diflomasiya Ko Da A Lokacin Yaki Ne Amma Ba Zata Amince Da Bin Umarni Ba October 30, 2025 Qalibaf: Amurka Tana Yaudarar Duniya Da Zaman Lafiya, Alhalin Tana Ci Gaba Da Kai Harin Wuce Gona Da Iri October 30, 2025 Ci Gaba Da Killace Gaza Bayan Tsagaita Bude Wuta Ya Janyo Mutuwar Mutane 1000 A Yankin October 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci