Aminiya:
2025-09-18@03:48:06 GMT

Biza: UAE ta ƙaƙaba wa ’yan Najeriya sabbin takunkumai

Published: 9th, July 2025 GMT

Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa (UAE), ta ƙara sanya wa ’yan Najeriya da ke son ziyartar Dubai sabbin sharuɗa.

Haka kuma, ta dakatar da bayar da bizar wucin gadi ga ’yan Najeriya.

Yara miliyan 5.4 na fama da karancin abinci a jihohin arewa 9 – Red Cross Kwanan nan gwamnati za ta sake kara kudin lantarki a Najeriya – Minista

Aminiya ta samu labarin cewa hukumomin shige da fice na Dubai ne suka bayar da umarnin sabbin matakan ga ofishin jakadancin ƙasar da ke Najeriya.

Daga cikin sabbin dokokin, duk ɗan Najeriyar da ke tsakanin shekaru 18 zuwa 45 ba zai samu bizar yawon buɗe ido ba sai idan zai yi tafiya tare da wani.

Wannan na nufin cewa yawan ’yan Najeriya da ke tafiya Dubai zai ragu, duba da yadda birnin ke da farin jini wajen kasuwanci da yawon buɗe ido.

A bara UAE, ta janye haramcin biza da ta sanya wa ’yan Najeriya na tsawon shekaru biyu.

Amma janye haramcin ya zo ne da sharuɗa masu tsauri, kuma yanzu ta ƙara tsaurara su.

Wani muhimmin canji a cikin sabbin ƙa’idojin shi ne cewa ba za a ƙara neman bizar wucewa ba daga ’yan Najeriya.

Sannan duk wanda ya haura shekaru 45, sai ya gabatar da bayanin asusun bankinsa na tsawon watanni shida da suka gabata.

Kuma kowane wata dole ne asusun ya zamana akwai aƙalla dala 10,000 ko dai daidai da hakan a kuɗin Naira.

Ƙasar ta ce dole ne a cika waɗannan sharuɗan tare da sauran takardun da ake buƙata da bayanan fasfo.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Najeriya Sharuɗa yan Najeriya

এছাড়াও পড়ুন:

DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya

A daidaikun kasuwannin Abuja da wasu manyan birane na ƙasar nan, an bayyana yadda farashin doya ke ƙara hawa fiye da yadda ake tsammani.

 

Wannan na faruwa ne duk da cewa yanzu sabuwar doya ta fara shigowa kasuwa, bisa al’ada, a duk shekara fitowar sabuwar doya kan karya farashin wanda yake kasuwa. Sai dai a bana, wasu daililai na sa farashin doya kara hawa.

NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba DAGA LARABA: Dalilan Da Suka Sa Nayi Yunkurin Kashe Kaina Har Sau Uku

wannan shine batun da shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi duba akai.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 
  • Microsoft ya ƙwace shafukan wasu kamfanoni 340 a Najeriya
  • Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi
  • DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya
  • Najeriya Na Asarar Dala Biliyan 10 Bayan Girbi Duk Shekara- Gwamnatin Tarayya
  • Iran Ta Gabatar Da Sabbin Kayayyaki Guda 5 A Wajen Taron Kolin kere-kere .
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • Hauhawar farashi ya ragu a watan Agusta — NBS
  • Sarki Sanusi II ya koka kan yawan cin bashin Najeriya
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa