Gwamana Charles Soludo na Jihar Anambra ya ce mafi rinjayen kaso na waɗanda jami’an tsaro ke kamawa da aikata laifuka tsawon shekara uku da suka gabata ’yan kabilar Ibo ne.

BBC ya ruwaito Soludo yana bayyana hakan a yayin wani taro da ’yan asalin jihar mazauna ƙetare suka gudanar a Amurka.

Jami’an tsaro sun hallaka ’yan bindiga 30 a Katsina HOTUNA: Obi ya ziyarci iyalin Ɗantata don yi musu ta’aziyya

Soludo wanda tsohon Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN) ne ya yi watsi da zargin da ake yi wa Fulani makiyaya na aikata satar mutane a jihar.

“Yanzu shekara uku da wata uku ke nan ina kan mulki. Idan muka kama masu laifi 100 to kashi 99 cikin 100 matasan ƙabilar Ibo ne,” a cewar gwamnan.

“Karya da farfaganda ake yaɗawa cewa Fulani ne ke aikata laifukan. Waɗannan karerayin da ake yaɗawa su suka buɗe kofa ga matasanmu shiga satar mutane saboda ta fi kawo kuɗi kan sana’arsu ta ‘Yahoo’ da safarar ƙwayoyi.”

Anambra na cikin jihohin Kudu maso Gabashin Najeriya da ’yan bindiga masu fafutikar kafa ƙasar Biafra suka dinga hana mutane fita harkokinsu duk ranar Litinin a baya domin nuna ɓacin ransu kan kamawa da kuma tsare jagoransu Nnamdi Kanu da Gwamnatin Tarayya ta yi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Farfesa Charles Soludo jihar Anambra

এছাড়াও পড়ুন:

Hukumar Abinci Ta Duniya ( WFP) Ta Jefa Wa Mutanane Kudancin Sudan Abinci Ta Sama

Hukumar abinci ta duniya ta fara aikewa da kayan abinci zuwa kudancin Sudan, ta hanyar amfani da jiragen sama domin jefa kayan agaji ga mazauna Kudancin Sudan da sauran yankunan da suke a killace tun cikin watan Maris.

Tun watanni 4 da su ka gabata ne dai hukumar abincin ta duniya ta fara aikewa da kayan agaji a kudancin Sudan din, bayan da fada mai tsanani ya hana a iya bi ta hanyoyin kasa.

A gefe daya, shugabar kungiyar ta Abinci reshen Afirka Mary Elen macgroti ta ce, fada da ake ci gaba da yi a yankin ya haddasa karacin ab inci, tare da yin kira da a dauki matakin gaggawa domin magance wannan matsala.

Da akwi mutane kusan miliyan daya a yankin tekun Nilu  da suke fuskantar yunwa mai tsanani, wasu 34,000 daga cikinsu yanayinsu ya fi tsananta.

Tun da yaki ya barke a kasar Sudan a 2023, masu bukatuwa da taimako suke kara yawa, da hakan ya tilastawa miliyoyi yin hijira zuwa kasashen makwabta da kuma a cikin gida.

A kasar Habasha kadai da akwai ‘yan hijirar Sudan da sun kai 50,000, kamar yadda hukar ta ambata.

A cikin jahohin Nilul-A’ala, da Arewacin Junqali kadai, hukumar Abincin ta Duniya tana son kai wa mutane 470,000 taimakon abinci daga nan zuwa watan Ogusta.

Sai dai hukumar taka korafin karancin abinci, ta yadda ya zuwa yanzu yake da bukatuwa da dalar Amurka miliyan 274 daga nan zuwa karshen wannan shekara. Yunwa tana yin barazana ga rayuwar mutane miliyan 7.7 a kudancin Sudan, amma a halin yanzu, hukumar za ta iya ciyar da mutane miliyan 2.5 ne kadai.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Na Biya Bashin Garatutin Naira Biliyan 13.6 Da ’Yan Fanshon Zamfara Ke Bi Tun 2011 – Gwamna Lawal
  • Tsohon Ɗan Takarar Gwamna A CPC, Haruna Sa’eed Kajuru, Ya Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Binciki Kisan ‘Yan Zariya  A Filato
  • Hukumar Abinci Ta Duniya ( WFP) Ta Jefa Wa Mutanane Kudancin Sudan Abinci Ta Sama
  • ‘ADC za ta mayar da APC jam’iyyar adawa a 2027’
  • Gwamna Peter Mbah Ya Ƙaddamar Da Jiragen Kasuwanci 3 Na ‘Enugu Air’ Mallakin Jihar
  • Mutane 21 Suka Mutu A Hatsarin Mota A Hanyar Zaria Zuwa Kano
  • Adadin Mutanen Da Suka Mutu A Ambaliyar Texas Ya Haura 80
  • Sojoji Da Masu Gadin Gandun Daji Zasu Murkushe Masu Aikata Laifuka A Kwara
  • Gwamna Yusuf Ya Kaddamar Rabon Na’urorin Rarraba Lantarki 500