Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ana zargin takalar faɗa tsakanin fadar Aminu Ado da Sanusi II

Tashin hankali ya sake kunno kai a Masarautar Kano, inda aka zargi wasu magoya bayan Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero, da kutsawa cikin fadar Sarki Muhammadu Sanusi II ta Gidan Rumfa da ke Kofar Kudu.

Shaidu sun bayyana wa Aminiya cewa lamarin ya faru ne lokacin da tawagar Sarki Aminu ke dawowa daga gaisuwar rasuwar attajirin ɗan kasuwa, marigayi Alhaji Aminu Ɗantata.

Jami’an tsaro sun hallaka ’yan bindiga 30 a Katsina HOTUNA: Obi ya ziyarci iyalin Ɗantata don yi musu ta’aziyya

A wata sanarwa da kakakin masarautar Kano, Sadam Yakasai, ya fitar ya bayyana cewa Sarki Sanusi ba ya cikin fadar lokacin da abin ya faru ba.

“Sun fasa kofar shiga fadar, sun kai wa masu gadi hari, har suka raunata wasu.

“Haka kuma sun lalata motocin ‘yan sanda da ke wajen fadar. Aminu ya yi amfani da titin gidan Sarki maimakon ya bi hanyar Koki zuwa Nasarawa, inda yake zaune. Wannan ya nuna cewa da gangan ya nufi Gidan Rumfa.”

Yakasai, ya ƙara da cewa wannan ba shi ne karon farko da Sarki Aminu ke fakewa da hanyar Gidan Rumfa ba, yana jefa fargaba a zukatan mazauna unguwar.

Wani makusancin Sarki Sanusi, da ya nemi a sakaya sunansa ya ce harin ya faru ne da gozon bayan wasu daga cikin majalisar Sarki Aminu.

Ya ce wani bidiyo da ya karaɗe kafafen sada zumunta kafin tashin hankalin ya tabbatar da hakan, inda aka jiyo wani daga cikin majalisar yana tabbatar da abin da za su yi.

Tawagar Sarki Bayero ta musanta

Sai dai wani daga cikin tawagar Sarki Aminu Ado Bayero, Mukhtar Dahiru, ya ƙaryata zargin.

Ya ce: “Ni kaina ina cikin tawagar Sarki Aminu a lokacin. Mun dawo daga Koki ne bayan gaisuwar rasuwar Alhaji Aminu Ɗantata. Sai dai a kusa da fadar Ƙofar Kudu muka tarar da wasu ɓata-gari da suka rufe hanya ɗauke da muggan makamai.

“Masoya Sarki ne suka tunkare su domin su ba mu hanya mu wuce.”

Ya ƙara da cewa babu wani hari da suka kai wa jami’an tsaro a fadar Sarki Sanusi, sai dai ‘yan sanda ne suka yi amfani da barkonon tsohuwa domin shawo kan lamarin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ana zargin takalar faɗa tsakanin fadar Aminu Ado da Sanusi II
  • Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki
  • Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa
  • Kamfanin Sin Ya Cimma Nasarar Shimfida Layin Dogo Na Farko Dakon Kaya Mafiya Nauyi A Hamadar Afirka
  • An ƙayyade maki da shekarun shiga jami’a a Nijeriya
  • ‘Yansanda Sun Kuɓutar Da ‘Yan Ghana 19 Da Aka Yaudare Su Zuwa Nijeriya
  • Kasar China Ta Yi Watsi da Barazanar Trump Na Kakabawa Kasashen BRICS Karin Takunkuman Tattalin Arziki
  • Amurka Ta Soke Dokar Da Ta Tabbatar Da Hai’at Tarirusham Cikin Jerin Kungiyoyin Yan Ta’adda
  • NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19