Yadda garin Zip ya nutse a Kogin Binuwai
Published: 23rd, March 2025 GMT
Wani abin al’ajabi da ban tsoro ya auku inda rana tsaka garin Zip da ke Jihar Taraba ya nutse baki dayansa a cikin Kogin Biniwai.
Wakilin Aminiya ya ziyarci garin domin gani da ido, inda ya ruwaito cewa a halin yanzu babu sauran wani gini ko bishiya da ake gani a garin, duk kogin ya hadiye su, sun nutse a cikin ruwa.
Garin na Zip da ke Karamar Hukumar Karim-Lamido ta Jihar Taraba yana bakin Kogin Biniwai ne, kuma mafi yawan mazaunansa masunta ne da manoma.
Sun kuma bayyana wa wakilinmu yadda abin ya faru da yadda suka tsallake rijiya da baya da irin asarar da suka tafka da kuma halin da ibtila’in ya jefa su a halin yanzu.
Wani mazaunin garin, Alhaji Gambo Sa’idu, wanda kuma dan uwan sarkin garin ne, ya shaida wa wakilinmu cewa, a gidansa akwai dakuna fiye da takwas kuma gidan nasa kamar sauran gidajen garin duk sun nutse a cikin Kogin Biniwai.
Yadda abin ya faru
Ya kara da cewa tun a shekarun baya ne al’ummar garin suka fara ganin gine-ginen da suke bakin gabar kogin garin sun fara tsagewa, daga bisani wasu suka fara ruftawa suna fadawa cikin kwaryar kogi.
Alhaji Gambo ya ce, “Tsohon Sarkin Zip, Marigayi Alhaji Uba Sa’idu ya kai rahoto ga Karamar Hukumar Karim-Lamido da kuma Gwamnatin Jihar Taraba kan yadda gidaje ke ruftawa suna ta fadawa cikin ruwa, amma babu wanda ya zo ya duba abin dake faruwa.”
Kwatsam ƙasa ta fara motsi gidaje na ruftawa
“A cikin daminar da ta wuce ne kawai al’ummar garin suka ga wasu sassan garin na motsi sai kuma gine-gine suka fara darewa.
“Da muka ga kasa tana motsi gine-gine kuma suna darewa sai muka shiga kwashe iyalanmu da kayayyakinmu daga cikin gidajenmu domin gudun kada gidajen su rufta cikin ruwa da iyalanmu da kayayyakinmu.
“A cikin wannan yanayin gine-gine da suke cikin garin dukkansu suka rufta cikin ruwa kuma ruwa da yashi suka rufe garin baki daya,’’ in ji shi.
Ruwa ya haɗiye gine-gine
Ya ci gaba da cewa “In ba wanda ya san dama akwai gari a wajen ba, babu wanda zai taɓa cewa akwai gari a can baya kafin wannan lamari ya faru, ba za a taba cewa akwai gari a nan ba.
“Ga inda garin Zip yake can ruwa da yashi sun rufe shi, abu daya ne ake gani, shi ne rodin da aka yi amfani da su wajen gina masallacin Juma’a, su ne kadai ba su nutse a cikin yashi baki daya ba,’’ in ji Gambo.
Gidana ta nutse a ruwa – Malam Bashiru
Malam Bashiru Gambo shi ma mazaunin garin na Zip ne, ya shaida wa wakilin Aminiya cewa ya kashe kudi kimanin Naira miliyan bakwai wajen gina gidansa mai dakuna shida a lokacin da kayan gini ke da arha.
Ya ce gidan nasa dungurumgum ya nutse a ruwa, amma dai Allah Ya taimake shi iyalinsa sun tsira, in banda wasu kayayyakinsa da suka nutse a ruwa.
A cewarsa, idan zai sake gina gida kamar nasa a yanzu, to zai kashe kudi fiye da Naira miliyan goma sha biyar saboda tsadar kayan gini.
Iyalai sun koma zama a bukkoki
Magidancin ya ce yanzu shi da iyalinsa da sauran mutanen sun koma zama a cikin bukkoki da suka yi na ciyawa saboda ba su da kudin da za su sake gina wasu gidaje.
Malam Bashiru ya ce, “Masallacin Juma’a da makarantar firamare da asibiti da kuma coci kamar sauran ginegine da ke garin duk sun rufta a cikin ruwa.
“Yanzu masallacin Juma’a da ciyawa aka yi shi, sa’annan kuma yaranmu ba sa zuwa makaranta domin har yanzu ba a sake gina wata makaranta a garin ba, kuma mata masu juna biyu da kananan yara ba sa samun kula ta fuskar kiwon tafiya.
“Abin mamaki shi ne yanzu ba wani taimako da mu al’ummar wannan gari muka samu daga Gwamnatin Jihar Taraba kuma yanzu ga shi lokacin damina na kara gabatowa,’’in ji Bashiru.
Mijina ya kamu da rashin lafiya – Hussaina
Wata matar aure mai ’ya’ya takwas mai suna Malama Hussaina Muhammed ta shaida wa wakilin Aminiya cewa da kyar ta tsira tare da mijinta da ’ya’yanta a lokacin da garin ya nutse a ruwa.
Ta ce duk da cewa sun tsira, amma a sanadiyyar wannan matsalar mijin nata, Malam Muhammed ya sami rashin lafiya, wanda a yanzu haka ya bar garin Zip ya koma wani gari ya bar ta da ’ya’yanta suna zaune a ’yan bukoki.
Malama Hussaina ta ce katifunsu da wasu kayayyaki duk sun nutse a ruwa kuma tana cikin halin kaka-ni-ka-yi domin mjiiin nata ya bar ta ita kadai kuma ’ya’yan nata kanana ne.
Kamar girgizar kasa
Shi ma Malam Ya’u Baba Tsoho, ya ce ba su taba fuskantar irin wannan ibtila’in ba, duk da kasancewar garin na Zip ya dade.
Ya ce, “Za a iya danganta hatsarin da ya auku a garin da cewa girgizar kasa ce domin a ranar da lamarin ya faru, garin ya motsa kuma gine-gine suka dare kuma dukkan gidajen suka yi ta ruftawa cikin kogi har da bishiyoyi ma da ke ciki da kewayen garin na Zip, duk sun nutse a cikin ruwa.”
Babu dauki daga gwamnati
Ya ce, “A can baya lokacin da jama’ar garin suka ga ginegine na tsagewa sarkin garin, Marigayi Uba Sa’idu ya kai rahoto ga Karamar Hukumar Karim-Lamido da kuma Gwamnatin Jihar Taraba har ma da hotuna, amma babu abin da hukumomin Jihar Taraba suka yi har ya zuwa lokacin da garin baki daya ya rufta a cikin ruwa.
“Har zuwa yanzu babu wani jami’in gwamnatin Jihar Taraba ko kuma na Karamar Hukumar Karim-Lamido wanda ya ziyarci garin domin ganin abin da ya faru, kai ma da kanka ka ga inda tsohon garin yake, ruwa da yashi sun rufe garin baki daya, ba wani alamar gini ko bishiya, kuma a yanzu duk al’ummar garinmu a bukoki muke zaune,’’ in ji Ya’u.
Mista Micah Dantala lsoko, wanda shi ne Magatakardan Sarkin Zip, ya shaida wa Aminiya cewa duk gine-ginen da ke garin sun nutse a cikin ruwa wanda haka ya haifar wa da jama’ar garin asarar dukiya mai yawan gaske.
Ya bayyana cewa Masallacin Juma’a da coci da makarantan firamare da asibiti suna daga cikin gine-ginen da suka nutse baki daya a cikin kogin na Biniwai.
Ya ce har yanzu babu wani dauki da aka kawo wa jama’ar garin don a tsusayawa.
“Mun yi sa’a ba a samu asarar rai a laokacin wannan hadari ba, amma daukacin gine-ginenmu da kayayyakimu duk sun nutse a cikin ruwa yanzu kusan duk al’umma suna zaune tare da iyalansu a dakunan ciyawa domin kayan gini sun yi tsada sosai,’’ in ji Micah.
Shi ma Sarkin garin na Zip, Malam Yusuf Babatato, ya bayyana cewa al’ummar garin sun yi asarar daukacin gidajensu da wuraren kasuwanci da masallatai da coci da makarantar firamare da asibiti.
Ya ce, “Kamar yadda duk wanda ya zo nan zai gani, kusan dukkan jama’a dakunan ciyawa suke zaune tare da iyalinsu.”
Shirin gina sabon gari ya samu cikas
Malam Yusuf Babatato, ya ce a halin yanzu sun sami wani wuri nesa da tsohon garin da ya nutse a ruwa za su gina sabon gari, amma matsalar kudi ta kawo jinkiri wajen fara aikin.
Ya ce, “Babbar matsalar da ke damun al’ummar garin ita ce rashin makaranta da asibiti domin sai an tafi wurare masu nisa ake samun kulawa ta fuskar kiwon lafiya, yara kuma suna zaune ba sa zuwa makaranta domin har yanzu ba a sake gina wata makaranta ko asibiti a garin ba.”
Duk kokarin da wakilin Aminiya ya yi domin jin ta bakin Kwamishinar Ma’aikatar Muhalli ta Jihar Taraba, Hajiya A’isha Barde, ya ci tura domin ba ta amsa kiran waya ba.
Wakilin namu ya tura mata rubutaccen sakon waya, inda ta dawo masa da amsar cewa ba ta sami labarin abin da ya auku a garin na Zip ba. Sai dai kuma ba ta yi wani bayani game da ko akwai wani mataki da gwamnatin Jihar Taraba za ta dauka kan lamarin ba, har zuwa lokacin da muka kammala hada wannan rahoton.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Binuwai Jihar Taraba Karamar Hukumar Karim Lamido sun nutse a cikin ruwa al ummar garin nutse a ruwa garin na Zip Jihar Taraba
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda mota ta kashe mutum 8 ’yan gida daya bayan dawowa daga yawon Sallah a Kaduna
Wani mummunan hatsarin mota a hanyar Kaduna zuwa Zariya ya yi sanadin mutuwar mutum takwas ’yan gida daya, yayin da wasu mutum biyu ke can kwance a asibiti rai a hannun Allah.
Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne wajen misalin karfe 6:00 na yammacin ranar Litinin a garin Barakallahu da ke kan hanyar Kaduna zuwa Zariya, ana tsaka da bukukuwan Babbar Sallah.
A cewar rahotannin, lamarin ya faru ne lokacin da wata mota da ke tsala gudu ta kwace sannan ta danne mutanen da ke tsaye a gefen hanya bayan dawowarsu daga yawon sallah.
Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara Mutum ɗaya ya tsira da ransa cikin 242 a hatsarin jirgin IndiaA cewar mahaifin mamatan, Malam Jamilu Usman Maiyadi, wata mota kirar GLK Marsandi mai ruwan toka ce ta take iyalan nasa, kuma wani yaro ne yake tuka ta.
Sai da a cewarsa, yaron wanda suka yi ittifakin dan gidan wani fitaccen dan siyasa ne a yankin, ya cika wandonsa da iska bayan faruwar lamarin.
Ya ce, “Mun rasa iyalai takwas ’yan gida daya a rana daya. Daga ciki akwai matata Khadija Umar da ’ya’yana su biyu sai kuma kanne da yayyen matar tawa da kuma wata gwaggonsu, duk sun mutu.
“A jimlance, mutum takwas kenan motar ta take; takwas sun mutu nan take, biyu kuma har yanzu suna asibiti,” in ji shi.
Malam Jamilu ya ce iyalan nasa na tsaye ne a bakin hanya suna jiran su sami motar da za ta kai su gida lokacin da motar ta kwace daga kan titi ta afka musu.
Ya kuma ce, “Tabbas motar na gudun wuce sa’a lokacin faruwar lamarin saboda kafar matata ta yi karayar da ba za a iya gyarawa ba, sannan sai jami’an hukumar kiyaye hadura ne ma daga baya suka gano wasu sassan jikin dana Sadiq,” Malam Jamilu ya fada fuskarsa cike da alhini.
‘Har da mai cikin wata takwas da za ta haifi tagwaye a cikin wadanda suka mutu’
Daga cikin wadanda suka rasu har da Zainab Muhammad wacce ke dauke da juna-biyun wata takwas da za ta haifi tagwaye.
Mijin marigayiyar, Sulaiman Abdulkadir Mai Shinkafa, wanda malamin addini ne a Hayin Rigasa, ya bayyana lamarin a cikin alhini.
Ya ce, “Ta kusa haihuwa. Mun riga mun sayi duk kayan jarirai muna shirye-shiryen haihuwar. Har mun ma sanya wa jariran sunan Hassan da Hussaini. Sannan akwai danmu mai shekara shida mai suna Khalid da aka kashe.
“An take matar tawa, sannan dana sai da muka kankaro namansa da katako kafin a yi musu jana’iza. Abu ne da babu wanda zai yi fatan ya gani a rayuwarsa.”
‘Ko uffan iyalan yaron da ya take mu ba su ce mana ba’
Kamar sauran masu alhinin, Malam Sulaiman ya nuna takaici kan yadda ya ce iyalan yaron da gwamnati sun yi watsi da su ko uffan ba su ce musu ba.
“Babu wani daga cikin iyalan yaron, wanda dan wani fitaccen dan siyasa ne a yankin da ya tuka motar, ko kuma daga gwamnatin jihar Kaduna da ya zo ya yi mana ta’aziyya.
“Ko uffan ba su ce mana ba. hatta mahaifin direban motar bai zo ba, sai ka ce yaruwar iyalan namu ba ta da wani amfani,” in ji shi.
Hukumar Kiyaye Hadura ta Kasa (FRSC) ta tabbatar da faruwar lamarin inda ta alakanta shi da gudun wuce sa’a da kuma kwacewar mota a kan hanyar da ba a jima da dauke ruwan sama ba.
Kwamandan shiyya na hukumar a Kaduna, Tijjani Iliyasu ne ya tabbatar da hakan.
Sai dai ya ce sun mika lamarin zuwa hannun ’yan sanda domin fadada bincike a kai.
Kazalika, duk kokarin wakilinmu na jin ta bakin rundunar ’yan sandan Kaduna da gwamnatin jihar sun ci tura saboda sun ki cewa komai a kai.