HausaTv:
2025-07-09@23:16:09 GMT

Abdullahi Ojlan Ya Sanar Da Kawo Karshen Fada Da Makami

Published: 9th, July 2025 GMT

Shugaban kungiyar Kurdawa ta kasar Turkiya ( PKK) Abdullah Ojlan ya sanar da kawo karshen amfani da makamai a fafutukar da kungiyarsu take yi na kare hakkokinsu a kasar Turkiya.

Shugaban kungiyar Kurdawan na Turkiya wanda yake tsare a kurkuku na shekaru masu tsawo, ya aiko da sako na bidiyo da a cikin ya ce; Har yanzu ina kan kiran da na yi a ranar 27 ga watan Febrairu  na ajiye makamai”.

Ojlan ya kara da cewa; Muna sanar da kawo karshen amfani da makamai ne bisa radin kanmu, haka na kuma ya ce; Mun shiga Zangon aiki da doka da kuma siyasa da tsarin demokradiyya, wanda shi kanshi nasara ce mai dimbin tarihi ba asara ba.”

Kuniyar PKK ta kurdawan Turkiya dai ta yi fiye da shekaru 40 tana dauke da makamai a fadan da take yi da gwamnatin Turkiya. A watan Mayu da ya shude ne dai kungiyar ta sanar rusa kanta, sannan kuma ta sanar da Shirin ajiye makamanta na yaki.

Tun a 1999 ne gwamnatin kasar Turkiya take tsare da Abdullahi Ojlan.

An kafa kungiyar PKK ne a shekarar 1978, ya kuma fara kai hare-hare a cikin kasar Turkiya a 1984, da ya zuwa ajiye makaman kungiyar an kashe mutane fiye da 40,000.

A cikin shekarun bayan nan ne da aka bude tattaunawa a tsakanin kungiyar da kuma gwamnatin Turkiya akan batun kawo karshen tawaye, da samar da hanyoyin sulhi da zaman lafiya domin warware korafin Kurdawan.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Turkiya

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka Ta Soke Dokar Da Ta Tabbatar Da Hai’at Tarirusham Cikin Jerin Kungiyoyin Yan Ta’adda

Shugaban kasar Amurka Donal Trump ya sanya hannu a takardan doka ta soke kungiyar yan ta’adda ta Jihatun Nusra, wacce ake kira Hay’at Tahrirusham a matsayin kungiyar yan ta’adda a duniya.

Shafin yanar gizo na labarai Arab News na kasar Saudiya, ya bayyana cewa shugaban ya cire HTSH daga jerin kungiyoyin yan ta’adda ne, saboda taimakawa kungiyar tabbatar da ikonta a kan kasar Siriya ta kuma share fagen dauke wa kasar takunkujman tattalin arzikin da aka dorawa kasar.

Labarin ya kara da cewa sakataren harkokin wajen kasar Amurka Marco Rubio ne ya sanya hannu a kan takardan cire shugaban kasar Siriya mai ci Ahmed Al-Sharaa ko wanda aka fi sani da Jolani daga jerin yan ta’adda a duniya. Wanda kuma zai share fagen wa ma’aikatar kudin Amurka ta kara virewa kasar Siriya takunkuman tattalin arziki da aka dorawa a kasar ta Siriya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwanan nan gwamnati za ta sake kara kudin lantarki a Najeriya – Minista
  • Hizbullah Ta Kasar Lebanon Ta Godewa JMI Dangane Da Tallafawa Kungiyar Saboda Gwagwarmaya Da HKI
  • Amurka Tana Fatan HKI da Hamas Su Tsaida Budewa Juna Wuta Na Kwanaki 60 A Karshen Wannan makon
  • DAGA LARABA: Shin Ko Zafin Nema Na Kawo Samu?
  • Gwamnatin Tinubu na shirya mana zagon ƙasa — ADC
  • Gwamnatin Kasar Iran Ta Yi Allawadai Da Hare-Haren HKI Kan Kasar Yemen
  • Amurka Ta Soke Dokar Da Ta Tabbatar Da Hai’at Tarirusham Cikin Jerin Kungiyoyin Yan Ta’adda
  • Amurka za ta ɗauki nauyin ’yan tawaye domin yaƙi da ta’addanci
  • Gwamnatin Kasar Iran Ta Yaba Da Kungiyar BRICS Saboda Yin Tir Da HKI A Yakin Kwanaki 12