Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-05-01@00:20:29 GMT

An Aika Dan Canji Da Dan Walawala Gidan Yari A Kwara

Published: 23rd, March 2025 GMT

An Aika Dan Canji Da Dan Walawala Gidan Yari A Kwara

Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Ilorin, karkashin jagorancin Mai shari’a Abimbola Awogboro ta yanke wa Musa Buba hukuncin daurin sa’o’i 300 da hidimar al’umma, bisa samunsa da laifin gudanar da harkokin kasuwanci na canji ba tare da wani cikakken lasisi ba.

Hakazalika, alkalin ya kuma yanke hukuncin daure wani Akinwale Olamilekan daga Owena Ijesha a karamar hukumar Oriade ta jihar Osun, daurin sa’o’i 300 (dari uku) da yiwa al’ummar hidima na tsawon sa’o’i biyar a kowace rana ba tare da zabin biyan tara ba, bayan da ya same shi da laifin aikata laifukan da suka shafi yanar gizo wato walawala ko yahoo boyi.

Hukumar dake yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta EFCC ta gurfanar da Musa da Akinwale a gaban kotu a ranar Alhamis, 20 ga Maris, 2025.

Ana tuhumar Musa Buba a wani lokaci a watan Yulin 2024 a kasuwar Chikanda, gundumar Yashikira, a karamar hukumar Baruten, jihar Kwara, yana gudanar da harkokin wata cibiyar hada-hadar kudi, Bureau De Change Business, ba tare da wani sahihin lasisi da babban bankin Najeriya ya bayar ba.

Laifin ya ci karo da Sashe na 57 (1) & (2) na Dokar Bankunan da Sauran Cibiyoyin Kudi, 2020, kuma ana hukunta shi a karkashin sashe na 57(5) (b) na wannan dokar.”

A cikin tuhumar da ake wa Akinwale Olamilekan (Alias: Mary Williams), an zarge shi da samun wani lokaci a watan Nuwamba 2024, da damfara da wata Mary Williams ta hanyar sakon karta kwana na iMessage asusu don karbar kudi $950 (Dalar Amurka Dari Tara da 55) daga wani Mark Durham.

Laifin ya sabawa sashe na 22 (2) (b) (ii) na laifukan Intanet (Hana, Rigakafin, da sauransu) Doka kuma ana hukunta shi a ƙarƙashin sashe na 22 (2) (b) (iv) na wannan Dokar.

Wadanda ake tuhumar sun amsa laifinsu.

 

Da yake tabbatar da gaskiyar lamarin, hujjojin da masu gabatar da kara karkashin jagorancin Andrew Akoja suka gabatar da kuma kararrakin wadanda ake tuhumar, mai shari’a Awogboro ya yanke musu hukunci daidai laifin da suka aikata.

Baya ga hukuncin, kotun ta umurci Musa Buba da ya bata kudaden da suka kai CFA 409,500 da kuma Naira 1,973,200 (Miliyan Daya, Dari Tara da Dubu Saba’in da Uku, Naira Dari Biyu Kadai) ga gwamnatin tarayya.

Hakazalika, Alkalin ya umarci Akinwale da ya ba Gwamnatin Tarayya dalar Amurka $450 (Dalar Amurka dari hudu da hamsin), da kuma wata wayar iphone 12 Pro Max da ya yi amfani da ita wajen aikata laifin.

COV/ALI MUHAMMAD RABIU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Damfara Kwara

এছাড়াও পড়ুন:

Rashin tsaro: Gwamnan AbdulRahman Ya Gana Da Sarakuna Masu Daraja Ta Daya A Jihar Kwara 

“Gwamnati ta amince da hada hannu da shugabannin al’umma na cikin gida domin tabbatar da tsaro.

 

“Muna gode muku kan abin da kuke yi. Amma muna bukatar Sarakuna su yi magana da mutanenmu kan kokarin da dukkanmu muke yi don kare al’ummominmu daga masu kutse.”

 

Gwamnan ya yi kira da a inganta hadin gwiwa a tsakanin al’umma da hukumomin tsaro domin kare rayuka da dukiyoyi.

 

Mataimakin Shugaban Majalisar Sarakunan Jihar Kwara, Alhaji Ibrahim Bologi II, wanda shi ne Etsu Patigi, ya yaba wa gwamnan bisa hada gwiwa da su domin tabbatar da tsaro a jihar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe Falasdinawa kusan 30 a wani sabon kisan kiyashin Isra’ila a Gaza
  • An ɗaure ’yar shekara 80 a kurkuku saboda dukan jikarta da silifas
  • Rashin tsaro: Gwamnan AbdulRahman Ya Gana Da Sarakuna Masu Daraja Ta Daya A Jihar Kwara 
  • ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno
  • Sabbin Bayanai Kan Fashe-Fashe Wasu Abubuwa A Tashar Jiragen Ruwan Kasar Iran
  • Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno
  • Za a rataye wani soja saboda laifin kashe budurwarsa
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jadadda Cewa: Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kan Iran Zai Fuskanci Mayar Da Martani
  • Shekara 10 ina sayar da sassan jikin ɗan Adam — Wanda ake zargi
  • Jiragen Yakin Amurka Sun Kashe Mutane Da Dama A lardin Sa’ada Na Kasar Yemen