Aminiya:
2025-10-15@21:41:01 GMT

HOTUNA: Obi ya ziyarci iyalin Ɗantata don yi musu ta’aziyya

Published: 9th, July 2025 GMT

Ɗan takarar Shugaban Ƙasa na jam’iyyar LP a zaɓen 2023, Peter Obi, ya ziyarci iyalin marigayi, Alhaji Aminu Dantata a Jihar Kano, don yi musu ta’aziyya.

Obi, ya bayyana cewa ya yi matuƙar baƙin ciki da rasuwar Alhaji Ɗantata, inda ya bayyana shi a matsayin “uba ga kowa.”

An gabatar da Ganduje a matsayin shugaban kwamitin hukumar FAAN 2027: Idan ADC na son lashe zaɓe dole ta bai wa ɗan Arewa takara — Okonkwo

Ya yaba yadda Ɗantata ya zama babban attajiri kuma ya taimaka wa mutane da dama suka samu nasara a rayuwarsu.

Ya ce Ɗantata ya taka muhimmiyar rawa wajen ci gaban Najeriya.

“Mun zo nan yau don jimami tare da iyalinsa da kuma ɗaukacin ‘yan Najeriya, saboda wannan babban rashi ne,” in ji Obi.

“Alhaji Aminu Dantata ba mai kuɗi ba ne kawai, ya taimaka wa wasu wajen cimma nasararsu a rayuwa.

“Ya kula da mutane sosai kuma ya zama kamar uba ga mutane da dama.”

Obi, ya bayyana Ɗantata a matsayin mutum mai tausayi da kishin ƙasa.

Ya ce mutuwarsa ta shafu al’amura da dama a wannan zamani.

Haka kuma, Obi ya yi addu’ar Allah Madaukakin Sarki Ya gafarta masa, ya saka masa da alheri, ya kuma albarkaci iyalinsa.

“Rayuwarsa abin koyi ce. Ba wai kasuwanci kawai ya yi ba, ya zuba jari a cikin al’umma. Abin da ya bari zai ci gaba da zama abin koyi.

“Allah Ya albarkaci wannan gida, ya albarkaci Najeriya baki ɗaya,” in ji Obi.

Alhaji Aminu Ɗantata fitaccen ɗan kasuwa ne luma mai taimakon jama’a daga Arewacin Najeriya.

Ya rasu yana da shekarau 94.

Mutane da dama daga sassa daban-daban na ƙasar nan sun yi alhini bisa gudunmawar da ya bayar a harkar tattalin arziƙi da taimakon jama’a.

Ga hotunan ziyarar a ƙasa:

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗantata rasuwa ta aziyya ziyara

এছাড়াও পড়ুন:

 MDD: Mutane 300,000 Su Ka Gudu Daga Sudan Ta Kudu A 2025

 MDD ta bayyana cewa; saboda fadan da ake yi a tsakanin magoya bayan shugaban kasa Silvaa Kiir da mataimakinsa Riek Machar ya tilastawa mutane kusan 300,000 su ka yi hijira.

Shi dai mataimakin shugaban kasar ta Sudan Ta Kudu, Riek Machar ana yi masa shari’a bisa zarginsa da aikata laifuka akan bil’adama.

Hukumar kare hakkin bil’adama ta fitar da bayanin da yake cewa: Ana ci gaba da yin fadace-fadace a cikin yankuna da yawa, ba tare da an daina ba, tun daga rattaba hannu akan yarjejeniyar sulhu a 2017, tare da kara da cewa; A cikin wannan shekarar ta 2025 kadai mutane 300,000 ne su ka fice daga cikin kasar.

A tsakanin wannan adadin da akwai mutane 148,000 da su ka isa kasar Sudan, sai kuma wasu 50,000 da su ka shiga kasar Habasha. Har ila yau, wani adadin na mutane 50,000 sun isa Uganda, yayin da wasu 30,000 suka shiga kasar DRC, sai kuma 25,000 a kasar Kenya.

A cikin gida kuwa adadin mutanen da sun kai rabin miliyan ne su ka fice daga gidajensu zuwa inda za su sami tsaro.

A wani rahoto na MDD a karshen watan Yuli, ta bayyana cewa; yakin basasar kasar ta Sudan ya yi sanadiyyar mutuwar mutane fiye da 1800 a tsakanin watan Janairu na wannan shekara zuwa Satumba da ya shude.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Ta Gabatar Da Shawarar Kulla Yarjejeniyar Tausayawa A Tsakanin Matan Duniya October 14, 2025 Larijani:  Gagarumar Tarbar Da Aka Yi Wa  Fursunonin Falasdinawa Ta Nuna Hakikanin Wanda Ya Sami Nasara October 14, 2025 Hamas Ta Mika Yahudawa 7 Daga Cikin 20 Da ke Hannunta  Ga Kungiyar Red Cross October 13, 2025 Iran: Kakabawa Kasa Mai Makwabta 16 Takunkumi Ba Abu Ne Mai Sauki Ba. October 13, 2025 An Gano Gawarwaki 323 Karkashin Burabutsai Bayan Dakatar Da Bude Wuta A Gaza October 13, 2025 Tehran Ta yi Gargadi Game Da  Barazanar Yaduwar Fadan Iyakar Afghanisatan Da Pakistan. October 13, 2025 Kungiyar (ASUU) Ta Sanar Da Shiga Yajin Aikin  Gargadi A Kasa Baki Daya . October 13, 2025 Aragchi: HKI Ba Zata Mutunta Tsaida Wuta A Gaza Ba October 13, 2025 Iran Ta Ki Zuwa Masar Saboda Bata Son Haduwa Da Azzaluman Da Suka Kashe Falasdinwa A Gaza October 13, 2025 Shugaban Kasar Amurka Donal Trump Ya Isa HKI Kafin Taron Sharm Sheikh October 13, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya 
  • Dakta Umar Kabir Yusuf-Bakatsinen da ya kirkiro manhajar Masjid Suite da ke sada zumuncin hada masallaci da masallata
  • An Bukaci An Bukaci Asusun JICHIMA Ya Fadada Hanyoyin Samun Kudade Baya Ga Gwamnatin Jigawa
  • Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima
  • Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani
  • Yadda Najeriya ta casa Jamhuriyar Benin 4-0
  •  MDD: Mutane 300,000 Su Ka Gudu Daga Sudan Ta Kudu A 2025
  • NAJERIYA A YAU: Shin Babu Wata Hanyar Magance Matsalolin ASUU Ne Sai Ta Yajin Aiki?
  • Yaƙin Gaza: Hamas da Isra’ila sun fara sakin fursunoni
  • Ta’addanci: Ana Fuskantar Ƙarancin Man Fetur A Mali Sakamakon Datse Hanyoyin Shiga Bamako