HOTUNA: Obi ya ziyarci iyalin Ɗantata don yi musu ta’aziyya
Published: 9th, July 2025 GMT
Ɗan takarar Shugaban Ƙasa na jam’iyyar LP a zaɓen 2023, Peter Obi, ya ziyarci iyalin marigayi, Alhaji Aminu Dantata a Jihar Kano, don yi musu ta’aziyya.
Obi, ya bayyana cewa ya yi matuƙar baƙin ciki da rasuwar Alhaji Ɗantata, inda ya bayyana shi a matsayin “uba ga kowa.”
An gabatar da Ganduje a matsayin shugaban kwamitin hukumar FAAN 2027: Idan ADC na son lashe zaɓe dole ta bai wa ɗan Arewa takara — OkonkwoYa yaba yadda Ɗantata ya zama babban attajiri kuma ya taimaka wa mutane da dama suka samu nasara a rayuwarsu.
Ya ce Ɗantata ya taka muhimmiyar rawa wajen ci gaban Najeriya.
“Mun zo nan yau don jimami tare da iyalinsa da kuma ɗaukacin ‘yan Najeriya, saboda wannan babban rashi ne,” in ji Obi.
“Alhaji Aminu Dantata ba mai kuɗi ba ne kawai, ya taimaka wa wasu wajen cimma nasararsu a rayuwa.
“Ya kula da mutane sosai kuma ya zama kamar uba ga mutane da dama.”
Obi, ya bayyana Ɗantata a matsayin mutum mai tausayi da kishin ƙasa.
Ya ce mutuwarsa ta shafu al’amura da dama a wannan zamani.
Haka kuma, Obi ya yi addu’ar Allah Madaukakin Sarki Ya gafarta masa, ya saka masa da alheri, ya kuma albarkaci iyalinsa.
“Rayuwarsa abin koyi ce. Ba wai kasuwanci kawai ya yi ba, ya zuba jari a cikin al’umma. Abin da ya bari zai ci gaba da zama abin koyi.
“Allah Ya albarkaci wannan gida, ya albarkaci Najeriya baki ɗaya,” in ji Obi.
Alhaji Aminu Ɗantata fitaccen ɗan kasuwa ne luma mai taimakon jama’a daga Arewacin Najeriya.
Ya rasu yana da shekarau 94.
Mutane da dama daga sassa daban-daban na ƙasar nan sun yi alhini bisa gudunmawar da ya bayar a harkar tattalin arziƙi da taimakon jama’a.
Ga hotunan ziyarar a ƙasa:
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɗantata rasuwa ta aziyya ziyara
এছাড়াও পড়ুন:
Mutane 21 Suka Mutu A Hatsarin Mota A Hanyar Zaria Zuwa Kano
Mummunan lamari ya faru ne a lokacin da wata mota kirar bas ta kasuwanci da wata babbar mota ta yi taho-mu-gama da tare da daukar rayukan mutane 21 a hanyar Zariya zuwa Kano.
Hadarin ya afku ne a Kasuwar Dogo, Dakatsale, wanda ya hada da wata motar kasuwanci kirar Toyota Hiace da wata tirela ta DAF.
Hukumar kiyaye hadurra ta kasa (FRSC) ta bayyana cewa, binciken farko da aka gudanar ya nuna cewa direban motar bas din ya saba ka’idojin zirga-zirgar ababen hawa, lamarin da ya kai ga yin karo da babbar motar da ke zuwa.
Hatsarin ya yi sanadiyar mutuwar fasinjoji 21 nan take, wadanda suka hada da manya maza 19 da manya mata 2, yayin da wasu uku suka samu raunuka, kuma an kai musu daukin gaggawa.
Jami’an FRSC tare da sauran kungiyoyin bayar da agajin gaggawa sun isa wurin domin gudanar da aikin ceto tare da kwashe tarkacen motocin, wanda hakan ya baiwa ababen hawa damar ci gaba da amfani da hanyar.
Da yake tofa albarkacin bakinsa, Shugaban Rundunar FRSC, Marshal Shehu Mohammed, ya bayyana matukar alhininsa game da asarar rayuka da aka yi, ya kuma jajantawa iyalan wadanda abin ya shafa.
Ya kuma tabbatar da cewa, ana ci gaba da gudanar da cikakken bincike domin gano cikakken al’amuran da suka faru a hatsarin.
“Wannan mummunan bala’i kuma wani abin tunawa ne mai raɗaɗi na mummunan sakamakon rashin biyayya ga dokokin hanya,” in ji shi.
“Tuƙi gangaci da wuce gona da iri sune manyan abubuwan da ke ba da gudummawa ga irin waɗannan bala’o’in da za a iya gujewa a kan hanyoyinmu.”
Rundunar ta Corps Marshal ta bukaci dukkan direbobi musamman masu sana’ar tuki da su bi ka’idojin zirga-zirgar ababen hawa.
Ya kuma jaddada cewa za a kara kaimi wajen tabbatar da tsaro da wayar da kan jama’a domin hana ci gaba da asarar rayuka.
Hukumar ta FRSC ta yi kira ga masu amfani da hanyar da su kai rahoton hatsarita hanyar kiran lambar kyauta 122, ko kuma a tuntubi duk wata tawagar sintiri ta FRSC.
An ajiye gawarwakin wadanda suka mutu a asibitin Nasarawa dake Kano, inda ake jiran tantancewa da kuma mikawa iyalansu.
Rel/Khadijah Aliyu