Gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ta yi furuci da cewa Iran ta kai hare-hare kan cibiyoyin sojojinta

Wani jami’in sojan gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ya yi furuci a ranar Talata cewa; Hare-haren da Iran ta kai a watan da ya gabata sun afkawa wuraren sojojin mamayar Isra’ila, matakin da tuni duniya ta amince da kai irin wadannan hare-hare kan cibiyoyin sojin mamaya.

Jami’in da ke magana da kamfanin dillancin labaran Reuters, ya ki bayar da karin bayani, ciki har da gano wuraren da abin ya shafa ko kuma irin barnar da harin ya yi ga kayayyakin aikin soja.

Iran ta kaddamar da hare-haren makamai masu linzami da jiragen sama  marasa matuka ciki kan haramtacciyar kasar Isra’ila a watan da ya gabata a matsayin mayar da martani ga hare-haren ba-zata da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ta kai a ranar 13 ga watan Yuni kan Iran  wanda harin ya auna fitattun shugabannin sojoji da masana kimiyyar makamashin nukiliyar Iran.

Harin na Iran ya sha mai da hankali kan birnin Tel Aviv da Haifa, matsugunan yahudawan sahayoniyya ‘yan kaka gida musamman wuraren da suke dauke da mutane masu yawa da kuma yankin kudancin Falasdinu da aka mamaye kusa da Beersheba, inda ake da cibiyoyin soji.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: haramtacciyar kasar Isra ila

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Yace Mutanen Kasarsa Suna Cikin Shiri Don Kare Kansu Da Karfi

Ministan harkokin wajen kasar Aran Abbas arachi ya bayyana cewa mutanen kasarsa a shirin suke su ci gaba da kare kasarsu daga Amurka da kuma HKI .

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Abbas Aragchi yana fadar haka a jiya litinin a lokacinda yake ganawa da tawagar kasar Brazil a gefen taron kungiyar BRICS karo 17 wanda ke tafiya a halin yanzu a birnin Rio de Jenero na kasar Brazil.

An gudanar da wannan taron ne saboda hare-haren da HKI da kuma Amurka suka kaiwa JMI a baya bayan nan, da kuma tasirinsa a cikin al-amuran siyasa da kuma tattalin arziki a yankin Asiya ta yamma da kuma duniya gaba daya.

Abbas Aragchi ya bayyana cewa hare-haren HKI da kuma Amurka ya sabawa dikokin kasa da kasa sannan ko wane bangare yana da rawar da zai take don ganin an tabbatar da zaman lafiya a duniya.

A nashi bangaren ministan harkokin wajen kasar Rasha Sergey Lavrov yace: hare-hare kan kasar Iran musamman a kan shirinta na makamashin nukliya na zaman lafiya abin yin tir da shi ne. Sannan ya kara da cewa kasar Rasha a shirye take ta taimaka ko a fagen kwamitin tsaro na MDD ne.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • A Karon Farko HKI Ta Yi Furuci Da Cewa Iran Ta Kai Wa Cibiyoyinta Na Soja Hare-hare
  • Falasdinawa 13 Ne Suka Yi Shahada Wasu Da Dama Suka Jikkata A Hare-Haren Sojojin Mamayar Isra’ila A Gaza
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Yace Mutanen Kasarsa Suna Cikin Shiri Don Kare Kansu Da Karfi
  • Gwamnatin Kasar Iran Ta Yi Allawadai Da Hare-Haren HKI Kan Kasar Yemen
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kai Hare-Haren Wuce Gona Da Iri Kan Lardin Hodeidah Na Kasar Yemen
  • Kungiyoyin Gwagwarmayar Falasdinawa Sun Yi Allah Wadai Da Harin Mamayar Isra’ila Kan Kasar Yemen
  • Gwamnatin Kasar Iran Ta Yaba Da Kungiyar BRICS Saboda Yin Tir Da HKI A Yakin Kwanaki 12
  • Turji: Sai ka sako mutanen da ka sace za a yi sulhu — Gwamnatin Sakkwato
  •  Nijar: An Kashe Sojoji 10 A Wasu Hare-hare Biyu Na ‘Yan Ta’adda