Iran Ta Musanta Neman Ci Gaba Da Gudanar Da Tattaunawa Da Amurka Kan Shirinta Na Makamashin Nukiliya
Published: 9th, July 2025 GMT
Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ta sanar da cewa: Iran ba ta gabatar da wata bukatu na ganawa ga bangaren Amurka ba
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya musanta kalaman shugaban Amurka dangane da muradin Iran na gudanar da tattaunawa, yana mai jaddada cewa: A bangaren Iran ba a gabatar da wata bukata ta yin wata ganawa da bangaren Amurka ba.
Da yake mayar da martani ga kalaman Donald Trump, Ismail Baqa’i ya ce: Iran tana musanta abin da Trump ya fada game da bukatar Iran na gudanar da tattaunawa, kuma ba ta gabatar da wata bukata ta ganawa da Amurkawa ba.
Yayin ganawarsa da Fira ministan gwamnatin Isra’ila Benjamin Netanyahu da yammacin ranar Litinin, Trump ya yi ikirarin cewa an sanya ranar tattaunawa da Iran, yana mai cewa: Iraniyawa suna son tattaunawa da Amurka.
A wani bangare na jawabin nasa, Trump ya sake nanata ikirarinsa game da shirin makamashin nukiliyar Iran, yana mai cewa: Ya yi imani cewa Iraniyawa suna son ganawa da Amurka ne domin samun zaman lafiya, ya kara da cewa; An lalata shirin makamashin nukiliyar Iran gaba daya, kuma hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa ta tabbatar da cewa an lalata wurin da Amurka ta kai hari a Iran.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Miliyoyin Yan Najeriya Ne Suka Gudanar da Tattakin Ashoora Wasu Kuma A Makarantunsu…
Miliyoyin yan Najeriya ne suka gudanar da tattakin Ashoora a birne daban daban a kasar a jiya Lahadi.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran, da farko ya nakalto daruwan da suka fito tattakin na Ashoora a Abuja babban birnin kasar a safiyar jiya Lahadi.
A wannan karon dai masu tattakin Ashoora a Abuja sun fito ba tare da sanya bakaken kaya ba saboda kaucewa rikici da kuma kamu daga Jami’an tsaro a birnin, kamar yadda suka sabayi a shekarun da suka gabata.
Labarin ya kara da cewa an gudanar da irin wannan tattakin na Ashoora a garurwa kimai 25 a duk fadin kasar, kuma an kammala ba tare da wata matsala ba.
An gudanar da tattaki a jihar Bauchi da kuma Jihar Yobe, wasu masu makokin Ashoora sun gudanar da su ne a cikin makarantu ko kuma masallatansu ko kuma wasu wurare da da suka kebe don haka Kungiyar muassasar Rasulul Azam sun gudanar da taron a makaransu da ke dan bare a birnin kano da kuma wasu wurare.