Rahotanni daga Yemen na cewa sojojin Amurka sun kai hari a filin tashi da saukar jiragen sama na Hudayda a wani sabon hari kan kasar Yemen tun bayan da Washington ta sanar da kai munanan hare-hare kan kasar dake adawa da hare-haren da Isra’ila ke kai wa al’ummar Gaza.
Tashar talabijin ta al-Masirah ta kasar Yemen ta ce an kai hare-hare ta sama har sau uku a filin jirgin saman da ke gabar tekun Bahar Maliya a daren Asabar.
Kafafan yada labaran Yaman sun kuma bayar da rahoton cewa, an kai hari da jiragen yakin Amurka a tashar jiragen ruwa ta Salif da ke lardin Hudaidah.
Jiragen yakin Amurka sun kara kai hare-hare biyar a gundumar Majzar da ke lardin Ma’rib da ke tsakiyar kasar Yemen.
A wani labarin kuma a lardin Sa’ada dake arewa maso yammacin kasar, sojojin Amurka sun kaddamar da hare-hare ta sama a yankunan Sahar da Kitaf wa al-Boqe’e.
A ranar 15 ga watan Maris ma Amurka ta sanar da kai wani hari ta sama wanda jami’an Yemen suka ce ya kashe mutane 53.
Hare-haren, wanda shi ne na farko tun bayan da Shugaba Donald Trump ya koma kan karagar mulki, ya zo ne bayan da sojojin Yaman suka yi alkawarin sabunta ayyukansu na hana duk wata safarar jiragen ruwa na Isra’ila ko kuma wadanda ke da alaka da Tel Aviv, domin nuna goyan baya ga al’ummar Falasdinu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Sojojin Kasar Iran Sun Ce Bazasu Dakatar Da Yaki ba Har Zuwa Samun Nasara A kan HKI
Babban kwamandan dokarun khatamul Ambiya (s) a nan birnin Tehran ya bayyana cewa sojojinsa zasu ci gaba da fafatawa da HKI har zuwa lokacinda zata dakatar da kawowa Iran yaki, ko kuma ta sami nasara a kansu,
Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya nakalto Janar Ali Shudmoni, yana fadar haka a yau Lahadi bayan da suke cilla makamai masu linzami da kuma jiragen yaki wadanda ake sarrafasu da nesa kan HKI a karon farko na rana, a cikin kwanaki uku da fara yakin.
Janar Shodmani ya kara da cewa zasu ci gaba da kaiwa yahudawan hare-hare har zuwa lokacinda zasu yi nadama sun daina yakin.
Kwamnatin ya bayyana cewa ya zuwa yanzu sun saminar kasar lalata cibiyoyin da jiragen yakin HKI suke shan makamashi wanda yake basu damar isa kasar Iran don kai hare-hare. Banda haka akwai nasarori da dama da suka samu a hare-haren wadanda nan gaba zasu bayyana.