2027: Idan ADC na son lashe zaɓe dole ta bai wa ɗan Arewa takara — Okonkwo
Published: 9th, July 2025 GMT
Tsohon jigo a Jam’iyyar LP, Kenneth Okonkwo, ya ce dole ADC ta tsayar da ɗan Arewa takara idan tana son ta kayar da Shugaba Bola Tinubu a zaɓen 2027.
A cikin wata hira da aka yi da shi a gidan talabijin na Channels, Okonkwo, ya ce idan ADC ta tsayar da ɗan Kudu takara, Tinubu zai sake lashe zaɓe ba tare da wata tangarɗa ba.
Ya ce dole ne ’yan adawa su yi aiki da hikima da dabaru idan suna son yin nasara.
“Shirina a wannan karon shi ne zan goyi bayan ɗan Arewa a 2027,” in ji shi.
Ya ce wannan ɗan takarar dole ne ya kasance mutum mai farin jini a Arewa.
Ya ambaci sunan Atiku Abubakar da Aminu Tambuwal a matsayin misali na mutanen da ke da farin jini a yankin.
“Mutumin dole ne ya cancanta. Idan ya taɓa riƙe muƙamin shugaban ƙasa ko kusa da hakan, to hakan zai ƙara wa tafiyar armashi.
“Idan ya haɗu da ɗan Kudu a matsayin mataimaki, to hakan zai taimaka sosai,” in ji Okonkwo.
Ya bayyana shugabancin Tinubu a matsayin “mara amfani,” inda ya ce ƙarfin ɗan Arewa ne kawai zai iya kawowa takarar Tinubu cikas.
Ya yi gargaɗin cewa tsayar da ɗan Kudu takara a jam’iyyar zai sa Tinubu ya lashe zaben cikin sauƙi.
“Idan ka tsayar da ɗan Kudu domin yin takara da Tinubu, wanda shi ma ɗan Kudu ne, to zai lashe zaɓe cikin sauƙi.”
“Idan aka kawo ɗan Kudu Maso Gabas, ko da ya yi nasara, za su murɗe zaɓen a hannunsa ,” in ji shi.
Ya bayyana cewa a siyasar Najeriya, sai ka samu goyon bayan “tsari” kafin ka iya kare nasararka.
Ya ce yankin Kudu Maso Yamma bai taɓa fafatawa da shugaban ƙasa mai ci ba saboda sun san dabarar siyasa.
Ya sake jaddada cewa Peter Obi ne ya lashe zaɓen 2023, amma an ƙwace masa.
Ya ce hakan na iya sake faruwa idan ba a shirya da kyau ba.
“Amma idan ɗan Arewa ne ya ci, babu wanda zai murɗe masa ko a ce ya sauka domin ba su fito daga yankin ɗaya da Tinubu ba,” in ji shi.
Okonkwo, ya fice daga jam’iyyar LP a watan Yulin 2024 saboda rikice-rikicen cikin gida da jam’iyyar ke fama da shi.
Yanzu da ’yan adawa suka haɗu ƙarƙashin jam’iyyar ADC, yana fatan za su iya ƙirƙiro tafiya mai ƙarfi domin tukarar zaɓen 2027.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Siyasa Zaɓe tsayar da ɗan da ɗan Kudu a jam iyyar
এছাড়াও পড়ুন:
MDD: Mutane 300,000 Su Ka Gudu Daga Sudan Ta Kudu A 2025
MDD ta bayyana cewa; saboda fadan da ake yi a tsakanin magoya bayan shugaban kasa Silvaa Kiir da mataimakinsa Riek Machar ya tilastawa mutane kusan 300,000 su ka yi hijira.
Shi dai mataimakin shugaban kasar ta Sudan Ta Kudu, Riek Machar ana yi masa shari’a bisa zarginsa da aikata laifuka akan bil’adama.
Hukumar kare hakkin bil’adama ta fitar da bayanin da yake cewa: Ana ci gaba da yin fadace-fadace a cikin yankuna da yawa, ba tare da an daina ba, tun daga rattaba hannu akan yarjejeniyar sulhu a 2017, tare da kara da cewa; A cikin wannan shekarar ta 2025 kadai mutane 300,000 ne su ka fice daga cikin kasar.
A tsakanin wannan adadin da akwai mutane 148,000 da su ka isa kasar Sudan, sai kuma wasu 50,000 da su ka shiga kasar Habasha. Har ila yau, wani adadin na mutane 50,000 sun isa Uganda, yayin da wasu 30,000 suka shiga kasar DRC, sai kuma 25,000 a kasar Kenya.
A cikin gida kuwa adadin mutanen da sun kai rabin miliyan ne su ka fice daga gidajensu zuwa inda za su sami tsaro.
A wani rahoto na MDD a karshen watan Yuli, ta bayyana cewa; yakin basasar kasar ta Sudan ya yi sanadiyyar mutuwar mutane fiye da 1800 a tsakanin watan Janairu na wannan shekara zuwa Satumba da ya shude.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Ta Gabatar Da Shawarar Kulla Yarjejeniyar Tausayawa A Tsakanin Matan Duniya October 14, 2025 Larijani: Gagarumar Tarbar Da Aka Yi Wa Fursunonin Falasdinawa Ta Nuna Hakikanin Wanda Ya Sami Nasara October 14, 2025 Hamas Ta Mika Yahudawa 7 Daga Cikin 20 Da ke Hannunta Ga Kungiyar Red Cross October 13, 2025 Iran: Kakabawa Kasa Mai Makwabta 16 Takunkumi Ba Abu Ne Mai Sauki Ba. October 13, 2025 An Gano Gawarwaki 323 Karkashin Burabutsai Bayan Dakatar Da Bude Wuta A Gaza October 13, 2025 Tehran Ta yi Gargadi Game Da Barazanar Yaduwar Fadan Iyakar Afghanisatan Da Pakistan. October 13, 2025 Kungiyar (ASUU) Ta Sanar Da Shiga Yajin Aikin Gargadi A Kasa Baki Daya . October 13, 2025 Aragchi: HKI Ba Zata Mutunta Tsaida Wuta A Gaza Ba October 13, 2025 Iran Ta Ki Zuwa Masar Saboda Bata Son Haduwa Da Azzaluman Da Suka Kashe Falasdinwa A Gaza October 13, 2025 Shugaban Kasar Amurka Donal Trump Ya Isa HKI Kafin Taron Sharm Sheikh October 13, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci