Tsohon jigo a Jam’iyyar LP, Kenneth Okonkwo, ya ce dole ADC ta tsayar da ɗan Arewa takara idan tana son ta kayar da Shugaba Bola Tinubu a zaɓen 2027.

A cikin wata hira da aka yi da shi a gidan talabijin na Channels, Okonkwo, ya ce idan ADC ta tsayar da ɗan Kudu takara, Tinubu zai sake lashe zaɓe ba tare da wata tangarɗa ba.

Biza: UAE ta ƙaƙaba wa ’yan Najeriya sabbin takunkumai Yara miliyan 5.4 na fama da karancin abinci a jihohin arewa 9 – Red Cross

Ya ce dole ne ’yan adawa su yi aiki da hikima da dabaru idan suna son yin nasara.

“Shirina a wannan karon shi ne zan goyi bayan ɗan Arewa a 2027,” in ji shi.

Ya ce wannan ɗan takarar dole ne ya kasance mutum mai farin jini a Arewa.

Ya ambaci sunan Atiku Abubakar da Aminu Tambuwal a matsayin misali na mutanen da ke da farin jini a yankin.

“Mutumin dole ne ya cancanta. Idan ya taɓa riƙe muƙamin shugaban ƙasa ko kusa da hakan, to hakan zai ƙara wa tafiyar armashi.

“Idan ya haɗu da ɗan Kudu a matsayin mataimaki, to hakan zai taimaka sosai,” in ji Okonkwo.

Ya bayyana shugabancin Tinubu a matsayin “mara amfani,” inda ya ce ƙarfin ɗan Arewa ne kawai zai iya kawowa takarar Tinubu cikas.

Ya yi gargaɗin cewa tsayar da ɗan Kudu takara a jam’iyyar zai sa Tinubu ya lashe zaben cikin sauƙi.

“Idan ka tsayar da ɗan Kudu domin yin takara da Tinubu, wanda shi ma ɗan Kudu ne, to zai lashe zaɓe cikin sauƙi.”

“Idan aka kawo ɗan Kudu Maso Gabas, ko da ya yi nasara, za su murɗe zaɓen a hannunsa ,” in ji shi.

Ya bayyana cewa a siyasar Najeriya, sai ka samu goyon bayan “tsari” kafin ka iya kare nasararka.

Ya ce yankin Kudu Maso Yamma bai taɓa fafatawa da shugaban ƙasa mai ci ba saboda sun san dabarar siyasa.

Ya sake jaddada cewa Peter Obi ne ya lashe zaɓen 2023, amma an ƙwace masa.

Ya ce hakan na iya sake faruwa idan ba a shirya da kyau ba.

“Amma idan ɗan Arewa ne ya ci, babu wanda zai murɗe masa ko a ce ya sauka domin ba su fito daga yankin ɗaya da Tinubu ba,” in ji shi.

Okonkwo, ya fice daga jam’iyyar LP a watan Yulin 2024 saboda rikice-rikicen cikin gida da jam’iyyar ke fama da shi.

Yanzu da ’yan adawa suka haɗu ƙarƙashin jam’iyyar ADC, yana fatan za su iya ƙirƙiro tafiya mai ƙarfi domin tukarar zaɓen 2027.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Siyasa Zaɓe tsayar da ɗan da ɗan Kudu a jam iyyar

এছাড়াও পড়ুন:

Najeriya Ta Kara Ƙaimi Wajen Kawar da Cutar HIV Nan da 2030

Daga Bello Wakili 

Najeriya ta ƙarfafa ƙoƙarinta na kawar da cutar HIV nan da shekarar 2030, inda Uwargidar Shugaban Kasa, Sanata Oluremi Tinubu, ta yi kira ga ’yan Najeriya, shugabanni da jami’an lafiya su haɗa hannu wajen cimma wannan manufa.

Yayin jawabi a bikin ranar Yaki da Cutar AIDS ta Duniya ta 2025 da aka gudanar a Fadar Shugaban Ƙasa, Oluremi Tinubu ta jaddada cewa za a iya kawar da cutar HIV a Najeriya idan aka ci gaba da yin aiki cikin tsari, haɗin kai da kuma samun tallafi.

Ta ce duk da cewa an samu cigaba a fannoni na rigakafi, magani da kulawa, ana buƙatar ci gaba da dagewa domin tabbatar da cewa kowane ɗan Najeriya na samun kariya.

Ta yi nuni da muhimmancin yaki da wariya, hantara da nuna bambanci, abubuwan da har yanzu ke hana mutane neman taimako.

Ta kuma jaddada aikin da ake yi a matakin ƙasa na dakile yaduwar cutar daga uwa zuwa jariri, faɗaɗa magungunan yara masu dauke da HIV, da dorewar shirye-shiryen al’amuran da suka shafi cutar ta HIV a cikin gida.

Uwargidar Shugaban Ƙasar ta yabawa Shirin Ƙasa na Yaƙi da Cutar AIDS da STDs saboda ci gaban da aka samu, tare da tallafin Global Fund.

Oluremi Tinubu ta lura cewa ko da yake masu tallafawa daga waje na taka muhimmiyar rawa, gwamnatin tarayya ta amince da dala miliyan 200 domin ƙarfafa shirye-shiryen HIV, tarin fuka da zazzabin cizon sauro.

Ta kuma yaba wa cigaban da Hukumar Kula da  Cutar HIV ta Kasa (NACA) ke samu wajen haɗin gwiwa da gwamnatocin jihohi domin tabbatar da dogon tsari da ɗorewar shirin ƙasa na dakile cutar ta HIV.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Tsaro Badaru Abubakar Ya Yi Murabus
  • Ministan Tsaro Badaru Abubakar Ya Ajiye Aiki
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan 164
  • Sarkin Musulmi ya buƙaci gwamnonin Arewa suke saurarar ƙorafin jama’a
  • Najeriya Ta Kara Ƙaimi Wajen Kawar da Cutar HIV Nan da 2030
  • Dalilin da na koma jam’iyyar ADC — Atiku
  • Tinubu ya sake aike wa majalisa ƙarin sunayen jakadu 32