Aminiya:
2025-10-15@12:21:26 GMT

Kwanan nan gwamnati za ta sake kara kudin lantarki a Najeriya – Minista

Published: 9th, July 2025 GMT

Ministan Lantarki na Najeriya, Adebayo Adelabu, ya ce Gwamnatin Tarayya na shirye-shiryen sake kara kudin wutar lantarki domin rage yawan bashin da bangaren lantarkin ke bi.

Bayanai dai sun nuna yanzu haka, bashin lantarkin da ake bi a Najeriya ya haura Naira tiriliyan hudu.

Amma a cewar ministan a yayin wani taron masu ruwa da tsaki 300 a Abuja, yunkurin wani bangare ne na tabbatar da cewa bangaren lantarki ya tsaya da kafarsa.

Matar tsohon Gwamnan Adamawa ta sauya sheka daga PDP zuwa ADC Kaso 90 na ’yan bindigar da suka addabi Katsina ’yan asalin jihar ne – Radda

Idan dai za a iya tunawa, duk da Karin kudin wutar da aka yi wa kwastomomin da ke tsarin Band A, mutane na ci gaba da korafin cewa ba sa samun isasshiyar wutar da ta kai ta kimar abin da suke biya.

Sai dai ministan ya ce yin karin na da muhimmanci ga ci gaban tattalin arzikin Najeriya da kuma ci gaban kasa.

A cewarsa, “A yanzu haka, akwai tarin bashin da lamfanonin da ke samar da wutar ke bin bashi sakamakon cire tallafin lantarkin da gwamnatin ta yi, wanda yah aura Naira tiriliyan hudu a karshen watan Disambar bara.

“Tuni gwamnatin ta fara tsare-tsaren ganin cewa wannan bashin bai ci gaba da taruwa ba, shi ya sa ma take kokarin kara farashin wutar, sannan ta kirkiro da sabon tallafi ga masu karamin karfi a cikin masu amfani da wutar.

“Abin da hakan ke nufi shi ne gwamnati za ta kawo karshen tallafin da take biya, wanda hakan ke nufin za a sami karuwar farashin a dukkan matakai,” in ji Ministan.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Karin kudin wuta Lantarki

এছাড়াও পড়ুন:

2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa

Ya ce manufofi da sauye-sauyen da Shugaba Tinubu ya aiwatar cikin shekaru biyu da suka gabata sun ƙara wa jama’a ƙwarin gwiwa game da tattalin arziƙin ƙasa da tafiyar da gwamnati, abin da ya sa zai yi wuya a kayar da shi a 2027.

“Babu wani ɗan siyasa a yau da zai iya ƙalubalantar Shugaba Bola Ahmed Tinubu. Muna tafiya da ‘sabon fata’ zuwa ‘farfafowa,’ kuma wannan farfaɗowar dole ne ta bayyana a rayuwar talakawa,” in ji Bwala.

Ya ƙara da cewa shugabannin ƙungiyoyi daga dukkanin shiyyoyi shida na ƙasar nan sun halarci taron, ciki har da wasu da suka zo daga Biritaniya.

Bwala, ya bayyana cewa taron ba yaƙin neman zaɓe ba ne, amma wata dama ce don gina kyakkyawar alaƙa tsakanin gwamnati da abokan hulɗa na ƙasa.

“Wasu mutane suna jiran lokacin zaɓe kafin su nemi ƙungiyoyi, amma wannan ba daidai ba ne. Ba kayan aiki ba ne, abokan tafiya ne, dole su kasance cikin abin da gwamnati ke yi,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa irin waɗannan taruka za a shirya su a Biritaniya, Amurka da Kanada don tattaunawa da ’yan Nijeriya mazauna ƙasashen waje da kuma yaɗa bayanai game da nasarorin gwamnatin Tinubu.

Bwala, ya bayyana cewa Fadar Shugaban Ƙasa tana shirin gudanar da babban taron tattaunawa a watan Nuwamba, inda dukkanin ƙungiyoyi za su haɗu domin nazarin dabarunsu da kuma kimanta yadda gwamnati ke aiki.

Ya ce sauye-sauyen tattalin arziƙi da gwamnatin Tinubu ta fara aiwatarwa sun fara bayar da sakamako a fannoni daban-daban kamar makamashi, noma, ayyukan gina ƙasa da samar da ayyukan yi.

“Mun riga mun fara ganin sakamako. Idan muka je fagen aiki, za mu ga ci gaba a bangaren tattalin arziƙi, tsaro, ilimi da noma. Waɗannan ƙungiyoyi za su ci gaba da yaɗa wannan saƙo,” in ji shi.

Shi ma tsohon ɗan majalisa, Hon. Ehiozuwa Johnson Agbonayinma, wanda ya halarci taron, ya yaba wa jagorancin Tinubu.

“Ko mutum ya so ko ya ƙi, Shugaban Ƙasa zai sake lashe zaɓe a 2027. Ba mu kai inda muke so ba tukuna, amma muna cimma nasara. Shugaban Ƙasa na yin duk abin da zai yi don kawo ci gaba,” in ji shi.

Agbonayinma, ya kuma yaba da cire tallafin man fetur, yana mai cewa hakan ya ba da damar a saki maƙudan kuɗaɗe don jihohi su inganta ci gaban al’umma a matakin ƙasa.

Dukkanin masu jawabin sun buƙaci ƙungiyoyin su ci gaba da yaɗa manufofin gwamnati da kuma tabbatar da haɗin kai tsakanin yankuna da jam’iyyu.

Bwala, ya kuma buƙaci magoya bayan Tinubu su ci gaba da nuna goyon baya da ƙauna ga Shugaban Ƙasa.

“Shugaba Tinubu ya yi abin da ya cancanci ba kawai goyon bayan jama’a ba, har ma da soyayya da jajircewarsu don ci gaba da abin da gwamnatinsa ta fara,” in ji shi.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai ‘Yan Bindiga Sun Hana Manoma Girbi A Zamfara, Al’umma Na Neman Taimako October 15, 2025 Manyan Labarai Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara October 15, 2025 Manyan Labarai Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima October 15, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa
  • Yansandan Italiya Sun Kara Da Masu Goyon Bayan Falasdinawa A Garin Udine
  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Bayyana Cewa: Sake Gina Gaza Zai Ci Dala Biliyan 70
  • Cirar kudin kwastoma: Majalisa ta gayyaci CBN da bankuna
  • NAJERIYA A YAU: Shin Babu Wata Hanyar Magance Matsalolin ASUU Ne Sai Ta Yajin Aiki?
  • ‘Yan Sandan Jihar Neja Sun Tabbatar Da Masu Sa-kai Kan Sahihiyar Kariya.
  • Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang
  • Ba Gudu Ba Ja-da-baya Kan Ci Gaba Da Kwaskwarima Ga Tsarin Haƙar Ma’adanai – Minista
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 9, sun kwato kudin fansa a Borno
  • Yajin Aikin ASUU:  Ba za mu biya duk wanda bai yi aiki ba — Gwamnatin Tarayya