HausaTv:
2025-05-01@01:07:57 GMT

Moscow : Dole ne Rasha da China su shiga tattaunawar nukiliya da Iran

Published: 23rd, March 2025 GMT

Kasar Rasha ta bayyana cewa dole Moscow da Beijing su shiga shawarwarin tattaunawar nukiliya da Iran.

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Rasha Maria Zakharova ta bayyana cewa, Moscow a shirye take ta samar da ingantacciyar hadin gwiwa da dukkan bangarorin kan batun yarjejeniyar nukiliyar Iran.

Shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da cewa ya aike da wasika zuwa Tehran domin fara tattaunawa kan shirin nukiliyar Iran; yayin da shi da kansa ya fice daga yarjejeniyar nukiliyar Iran a wa’adinsa na farko.

A halin da ake ciki dai ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya bayyana cewa, Jamhuriyar Musulunci ta Iran za ta mayar da martani ga wasikar shugaban Amurka Donald Trump a cikin kwanaki masu zuwa ta hanyoyin da suka dace.

Araghchi ya bayyana hakan ne a lokacin da yake jawabi kai tsaye a gidan talabijin na Jamhuriyar Musulunci ta Iran (IRIB) ranar Alhamis.

Araghchi ya kuma lura cewa a wannan karon, ci gaban ya zo tare da wani yunkuri na diflomasiyya daga Amurkawa, ciki har da wasika da bukatar yin shawarwari.

Ya kuma bayyana cewa manufar Jamhuriyar Musulunci ta Iran a bayyane take. “Ba za mu shiga tattaunawa kai tsaye karkashin matsin lamba, barazana, ko karin takunkumi.”

Ministan harkokin wajen kasar ya kuma bayyana cewa wasikar “mafi yawan barazana ce,” amma kuma akwai damamaki a ciki.

A farkon watan Maris ne Trump ya bayyana cewa ya rubuta wasika zuwa ga Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: bayyana cewa

এছাড়াও পড়ুন:

Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China

kauyuka a China, ana nufin yankunan da suka bunkasa, wadanda suka kasance, sun yi kamance-ceniya da sun anguwanin GRA a Nijeriya da kuma a nahiyar Afirka.

 

A yankin na Hero Bay, an tanadar da tituna inganciyyar wutar lantarki, tsaftatattacen ruwan sha da kuma kafar Inernet

 

Akwai manyan bene masu tsawo a yankin, wadanda tsawonsu ya dara na bene mai hawa biyar, inda kuma aka tanadar wa da yankin, ababen more rayuwa.

 

kananan hukumomi ne, suka gina wadannan matsugunnan, musamman donin a dakile barazanar kwararowa alumma daga kauye, zuwa cikin birane.

 

A gwajin da aka yi na yankunan da su habaka sosai a China, ana buga misali da Hero Bay kan yadda gwamnati ke bai wa alumma kwarin guiwa na su ci gaba da zama a yankunan da suke, musamman ta hayar samar masu tallafin kudi da gidaje.

 

Wannan dabarun, baya ga kara bunkasa fannin aikin noma a kauyukan, sun kuma kara habaka fannin fasaha kimiyya a kauyukan da kuma kara bunkasa tattalin arzikin kasar.

 

Wani mai gudanar da aikin bincike a cibiyar yin bincike a fannin fasaha ta kasar Wang Yongzhong, ya alakanta kauyukan a matsayin guraren da suka yi fice a duniya, da makuntan kasar, suka samar masu da ababen more rayuwa.

 

Samar da hanyoyi na daga cikin ayyukan da gwamnatin China, ke bai wa mahimmanci, musamman domin a samar da damar gudanar da zirga-zirgar gudanar da ayyukan yau da kullum, a cikin sauki.

 

Samar da yankin na Hero Bay, na daga cikin babban misalin mayar da kan gwamnatin kasar, na dakile kwararowar mazauna a karkara, musamman a tsakanin matasa zuwa cikin birane.

 

Wasu biranen sun kasance cike suke da manyan rukunonin gidage, amma wannan sabanin haka ne, a Hero Bay, duba da yadda aka samar da gidaje, ga ‘yan kauyen da ke da ra’ayin zama a cikinsu, wanda kuma za su iya habaka kasuwancinsu da gudanar da aikin noma, tare da kuma samar da makarantu, Asibiti da jami’an tsaro da sauransu.

 

Daura da Hero Bay, akwai masana’antar kera motoci, wadda kuma ke samar da ayyukan yi ga mazauna yankin, ta hanyar goyon bayan ayyuakn shirye-shirye na kananan hukumomi.

 

A cewar Mataimakin Daraktan shirin bayar da horo China, Mista Wu Hao, gwamnatin kasar ta samar da wadannan ababen more rayuwar ne, domin a dakile kwararar mazauna kauyukan zuwa cikin biranen kasar.

 

daya daga cikin mazauna yankin Madam Yang Baozhen, ta tabbatar da wannan maganar ta Mista Wu Hao, inda ta ce, ana karfafawa, musamman matasa guiwa domin su shiga a dama da su, a fannin hada-hadar kasuwancin yankin, wanda hakan ka samar da kauyukan kudaden shiga.

 

Kazalika, mazauna kauyukan da ba su da bukatar shiga fannin noma ko yin aiki a masana’anta, su kan bude gidajen sayar da abinci ko kuma yin wasu kanannan sana’oi.

 

A kauykan, ana kuma bayar da ilimin zamani kyauta, tun daga matakin Firamare zuwa na Sakandare.

 

Bisa tsarin mallakar filaye a kauyukan ba za ka sayi fili ko kuma ka sayar da shi ba, amma za ka iya bayar da jinginarsa, har zuwa tsawon shekaru 50 zuwa 70, wanda daga baya, za ka sabunta jinginar.

 

A cewar wani mai zagaya wa masu yawon bude ido, “A kasar duk wani fili da ke kasar, mallakar gwamnatin kasar ne, wadda kuma kowanne fili, an tsara abinda za a yi a kansa,”

 

A yayin da ake ci gaba da tattauna wa kan batun bunkasa nahiyar Afrika ciki har da Nijeriya, akwai bukatar a rungumi irin wannan tsarin na China, duba da cewa, abu ne, da kwalliya za ta biya kudin Sabulu.

 

Kazalika, ta hanyarin yin hadaka da tsarin samar da hanyoyi na BRI na China hakan zai samar da wata ingantacciyar hadaka ga kasashe masu tasowa da kuma ga cibiyar bunkasa kasuwanci ta kasa da kasa ta AIBO da ke a karkashin ikon ma’aikatar bunkasa kasuwanci ta China, musamman wajen bayar da horo kan dabarun zamani na bunkasa kasuwanci.

 

Hakazalika, ta hanyar rungumar wannan tsarin China, Afirka za ta iya magance yawan kwararowar mazauna karkara, zuwa cikin birane, wanda hakan zai kuma taimaka wa kasashen da ke a Afrika, wajen kara bunkasa tattalin arzikinsu da samar wa da ‘yan Afrika, alkibla mai dorewa.

 

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Araghchi : Za’ayi Tattaunawar Iran da Amurka ta gaba a Rome bayan taron E3
  • Ma’aikatar Sharia A Nan Iran Zata Bayyana Abinda ya farsu A Tashar Jiragen Ruwa Na Shahid Rajae
  • NEMA Ta Karɓi ‘Yan Nijeriya 203 Da Suka Maƙale A Libya
  • Nazarin CGTN: Ana Kara Bayyana Rashin Gamsuwa Da Sabuwar Gwamnatin Amurka Daga Ciki Da Wajen Kasar
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Na Iran Ya Ce: Maganar ‘Yan Sahayoniyya Rudu Ne Maras Amfani
  • Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Ci Gaba Da Killace Gaza Da Kashe Mutane, Laifi Ne Da Ba A Taba Yin Irinsa Ba
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Tattauana Da Shugaban Hukumar IAEA
  • Takht Ravanji: Iran Ba Za Ta Taba Yin Tattaunawa Akan Dakatar Da Tace Sanadarin Uranium Ba
  • Iran Da Rasha Sun Jaddada Yin Aiki Tare A Fagen Kiwon Lafiya