Aminiya:
2025-06-06@16:34:05 GMT

Sojoji sun dakile hare-haren ‘Yan Boko Haram biyu a Borno

Published: 5th, June 2025 GMT

A wani hari ta kasa da na sama, rundunar sojojin Operation Hadin Kai sun dakile wasu manyan hare-haren ta’addanci guda biyu a ranar Alhamis a Jihar Borno.

Dakarun sun kashe da dama daga cikin maharan tare da kwato tarin makamai da alburusai.

Wani mutum ya mutu a cikin rijiya a Kano Mahajjata kusan miliyan biyu na hawan Arfa a Saudiyya

Rahoton da hukumar tsaron sojan Najeriya suka fitar na nuna cewar, dakarun sojan rundunar ta OPHK an kaddamar da hare-haren ne a wasu wurare daban-daban na sojoji a Buratai da ke karamar hukumar Biu da kuma Mallam Fatori da ke karamar hukumar Abadam.

An bayyana cikakkun bayanan hare-haren a cikin wata sanarwa da Mukaddashin mataimakin daraktan hulda da jama’a na rundunar soji na hedikwatar Operation Hadin Kai, Kyaftin Reuben Kovangiya ya fitar ranar Alhamis, 5 ga Yuni, 2025.

Sanarwar ta ce, lamarin na farko ya faru ne da sanyin safiyar Alhamis a garin Buratai, inda ‘yan ta’addan suka yi yunkurin kutsawa inda dakarun suke daga wurare da dama.

“Sojojin, duk da haka, cikin hanzari sun yi artabu da ‘yan ta’addan da manyan bindigogi, yayin da dakarun sama da manya-manyan Jiragen yakin Tucano suka ba da tallafi ta sama ga sojojin.”

Kyaftin Kovangiya ya bayyana daga bayan an gano gawarwakin ‘yan Boko Haram dama, tare da tarin makamai da alburusai iri-iri.

Hakazalika, sojojin a Mallam Fatori sun dakile wani harin da ‘yan tada kayar bayan suka tunkaro inda suke daga bangarori daban-dabam.

Sanarwar ta kara da cewa, “Sojojin sun yi wa ‘yan Boko Haram mummunan barna lamarin da ya sa su tserewa cikin rudani.”

Bayan da ‘yan tada kayar bayan da suka ja da baya ya kai ga kashe mutane da dama, yayin da wasu suka tsere da raunukan harbin bindiga.

Abubuwan da aka kwato daga hannunsu a Mallam Fatori sun hada da: bindigogi kirar AK-47 da yawa, manyan bindigogi masu linzami (GPMGs), bindigogin roka (RPGs), da sauran kayan aikinsu na ta’addanci.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Boko Haram hare hare Operation Hadin Kai

এছাড়াও পড়ুন:

DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Kayan Miya Gabanin Bikin Sallah

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Yayin da sallah ya gabato, mutane da dama kan yi fadi tashi don biyan wasu bukatun su na bukukuwan sallah, kuma kamar yadda aka saba, a irin wannan lokaci ne iyalai da dama kan maida hankulan su don ganin sun biya wasu daga cikin bukatun su musamman wadanda suka jibanci bikin sallah.

 

Siyayyan kayan kayan abinci na daya daga cikin wadannan hidindimu, sai dai kayan miya da suka zama dole ayi amfani dasu yayin bikin sallah sun yi tashin gwauron zabo inda alumma da dama ke ta bayyana damuwar su kan wannan batu.

NAJERIYA A YAU: Hanyoyin kauce wa ɓarnar ambaliyar ruwa DAGA LARABA: “Sai Na Tara Kudin Cin Abinci Na Nake Iya Siyan Audugar Al’ada”

shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi nazari ne kan dalilan da suka sa farashin kayan miya suka yi tashin gwauron zabo gabanin bikin Sallah.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji sun kashe manyan Kwamandojin ISWAP 3 a Borno
  • Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
  • Ministan Tsaro Ya Yi Gargadin Sake Dawowar Boko Haram Na Barazana Ga Nijeriya
  • ‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 
  • Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno
  • DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja
  • Medvedev : babu makawa Rasha za ta mayar da martani mai zafi ga hare-haren kyiv
  • DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Kayan Miya Gabanin Bikin Sallah
  • Guardian: Isra’ila Tana Kai Wa Makarantun Dake Dauke Da ‘Yan Gudun Hijira a gaza Hari, Tana Sane Da Hakan