Aminiya:
2025-06-13@11:00:23 GMT

Sojoji sun dakile hare-haren ‘Yan Boko Haram biyu a Borno

Published: 5th, June 2025 GMT

A wani hari ta kasa da na sama, rundunar sojojin Operation Hadin Kai sun dakile wasu manyan hare-haren ta’addanci guda biyu a ranar Alhamis a Jihar Borno.

Dakarun sun kashe da dama daga cikin maharan tare da kwato tarin makamai da alburusai.

Wani mutum ya mutu a cikin rijiya a Kano Mahajjata kusan miliyan biyu na hawan Arfa a Saudiyya

Rahoton da hukumar tsaron sojan Najeriya suka fitar na nuna cewar, dakarun sojan rundunar ta OPHK an kaddamar da hare-haren ne a wasu wurare daban-daban na sojoji a Buratai da ke karamar hukumar Biu da kuma Mallam Fatori da ke karamar hukumar Abadam.

An bayyana cikakkun bayanan hare-haren a cikin wata sanarwa da Mukaddashin mataimakin daraktan hulda da jama’a na rundunar soji na hedikwatar Operation Hadin Kai, Kyaftin Reuben Kovangiya ya fitar ranar Alhamis, 5 ga Yuni, 2025.

Sanarwar ta ce, lamarin na farko ya faru ne da sanyin safiyar Alhamis a garin Buratai, inda ‘yan ta’addan suka yi yunkurin kutsawa inda dakarun suke daga wurare da dama.

“Sojojin, duk da haka, cikin hanzari sun yi artabu da ‘yan ta’addan da manyan bindigogi, yayin da dakarun sama da manya-manyan Jiragen yakin Tucano suka ba da tallafi ta sama ga sojojin.”

Kyaftin Kovangiya ya bayyana daga bayan an gano gawarwakin ‘yan Boko Haram dama, tare da tarin makamai da alburusai iri-iri.

Hakazalika, sojojin a Mallam Fatori sun dakile wani harin da ‘yan tada kayar bayan suka tunkaro inda suke daga bangarori daban-dabam.

Sanarwar ta kara da cewa, “Sojojin sun yi wa ‘yan Boko Haram mummunan barna lamarin da ya sa su tserewa cikin rudani.”

Bayan da ‘yan tada kayar bayan da suka ja da baya ya kai ga kashe mutane da dama, yayin da wasu suka tsere da raunukan harbin bindiga.

Abubuwan da aka kwato daga hannunsu a Mallam Fatori sun hada da: bindigogi kirar AK-47 da yawa, manyan bindigogi masu linzami (GPMGs), bindigogin roka (RPGs), da sauran kayan aikinsu na ta’addanci.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Boko Haram hare hare Operation Hadin Kai

এছাড়াও পড়ুন:

Salami: Babu Inda Ba Za Mu Iya Kai Wa Hari Ba A Fadin HKI

Kwamandan dakarun kare juyin juya halin musulunci na Iran Manjo Janar Hussain Salami ya fada a yau Alhamis cewa; Abokan gaba suna yi mana barazana da yaki, sannan ya tabbatar da cewa a shirye suke su fuskanci duk abinda zai faru.

Manjo janar Salami wanda ya gabatar da jawabi ga taron dakarun sa-kai na “Basiji a nan Tehran ya kuma kara da cewa;  Babu wani wuri komai zurfi da nisansa a HKI da ba mu tsinkayowa, idan kuwa aka ba mu umarni to za su yi nasara, mu Sanya abokin gaba ya yi nadama.

A gefe daya ministan tsaron Iran ya bayyana cewa; Duk wani hari da ake tunanin kawo wa Iran, to kuwa zai fuskanci mayar da martani mai tsanani.

Ministan tsaron na Iran Laftanar janar Azizi Nasri Zadeh ya kara da cewa;  Idan har yaki ya barke, to za a tilasta wa Amruka ficewa daga wannan yankin, kuma asarar da za ta yi sai ta rubanya wacce za ta yi wa Iran.”

Ministan tsaron na Iran ya kuma ce; Abin takaici ne yadda wasu jami’an Amurka su ka yi barazanar yiyuwar barkewar yaki, idan ba a cimma matsaya ba a tattaunawar Nukiliya, sannan ya kara da cewa: Tehran ba ta maraba da yaki, amma kuma a lokaci daya ta shirya masa.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Harin Isra’ila a kan Iran ya jefa yankin Gabas ta Tsakiya cikin zama dar-dar
  • Nijeriya Ce Ta 3 A Manyan Kasashe Masu Karfin Masana’antu 10 Na Afirka
  • Isra’ila ta kaddamar da hare-hare kan yankuna da dama na Iran ciki har da Tehran
  • Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara
  • Sojoji Sun Kashe Auta, Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda Da Wasu 13 a Jihar Zamfara
  • Salami: Babu Inda Ba Za Mu Iya Kai Wa Hari Ba A Fadin HKI
  • An kashe mutum 41 cikin mako ɗaya a Filato 
  • Ba Mu Iya “Gina” Ayaba A Amurka
  • ‘Yan Tawayen Sudan Sun Kai Hare-Hare Kan Ayarin Motocin Agaji A Kan Hanyarsu Ta Kai Agajin Jin Kai 
  • Sojoji Sun Kashe Babban Kwamandan Boko Haram A Jihar Yobe