Aminiya:
2025-09-17@23:17:19 GMT

Sojoji sun dakile hare-haren ‘Yan Boko Haram biyu a Borno

Published: 5th, June 2025 GMT

A wani hari ta kasa da na sama, rundunar sojojin Operation Hadin Kai sun dakile wasu manyan hare-haren ta’addanci guda biyu a ranar Alhamis a Jihar Borno.

Dakarun sun kashe da dama daga cikin maharan tare da kwato tarin makamai da alburusai.

Wani mutum ya mutu a cikin rijiya a Kano Mahajjata kusan miliyan biyu na hawan Arfa a Saudiyya

Rahoton da hukumar tsaron sojan Najeriya suka fitar na nuna cewar, dakarun sojan rundunar ta OPHK an kaddamar da hare-haren ne a wasu wurare daban-daban na sojoji a Buratai da ke karamar hukumar Biu da kuma Mallam Fatori da ke karamar hukumar Abadam.

An bayyana cikakkun bayanan hare-haren a cikin wata sanarwa da Mukaddashin mataimakin daraktan hulda da jama’a na rundunar soji na hedikwatar Operation Hadin Kai, Kyaftin Reuben Kovangiya ya fitar ranar Alhamis, 5 ga Yuni, 2025.

Sanarwar ta ce, lamarin na farko ya faru ne da sanyin safiyar Alhamis a garin Buratai, inda ‘yan ta’addan suka yi yunkurin kutsawa inda dakarun suke daga wurare da dama.

“Sojojin, duk da haka, cikin hanzari sun yi artabu da ‘yan ta’addan da manyan bindigogi, yayin da dakarun sama da manya-manyan Jiragen yakin Tucano suka ba da tallafi ta sama ga sojojin.”

Kyaftin Kovangiya ya bayyana daga bayan an gano gawarwakin ‘yan Boko Haram dama, tare da tarin makamai da alburusai iri-iri.

Hakazalika, sojojin a Mallam Fatori sun dakile wani harin da ‘yan tada kayar bayan suka tunkaro inda suke daga bangarori daban-dabam.

Sanarwar ta kara da cewa, “Sojojin sun yi wa ‘yan Boko Haram mummunan barna lamarin da ya sa su tserewa cikin rudani.”

Bayan da ‘yan tada kayar bayan da suka ja da baya ya kai ga kashe mutane da dama, yayin da wasu suka tsere da raunukan harbin bindiga.

Abubuwan da aka kwato daga hannunsu a Mallam Fatori sun hada da: bindigogi kirar AK-47 da yawa, manyan bindigogi masu linzami (GPMGs), bindigogin roka (RPGs), da sauran kayan aikinsu na ta’addanci.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Boko Haram hare hare Operation Hadin Kai

এছাড়াও পড়ুন:

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Daga ranar 14 zuwa 15 ga wata, an gudanar da sabon zagayen shawarwari kan harkokin tattalin arziki da cinikayya a tsakanin Sin da Amurka a birnin Madrid, babban birnin kasar Spaniya, inda bangarorin biyu suka yi musayar ra’ayoyi a kan harkokin cinikayya da ke janyo hankalinsu, tare da cimma daidaito ta fannin daidaita batutuwan da suka shafi Tiktok, da rage shingayen zuba jari, da sa kaimin hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya a tsakaninsu.

Taron shawarwarin ya kasance zagaye na hudu da sassan biyu suka gudanar cikin watanni biyar da suka wuce. Kwatankwacin shawarwarin da aka gudanar a baya, a karo na farko, an sanya Tiktok cikin batutuwan da aka tattauna a shawarwarin na wannan zagaye. Yadda Sin da Amurka suka cimma daidaito a kan batun, ya kuma sake shaida cewa, samun moriyar juna shi ne tushen huldar kasashen biyu ta fannin tattalin arziki da cinikayya.

Hada karfi da karfe shi ne mafita daya tilo, a yanayin da ake ciki na karancin karfin bunkasuwar tattalin arzikin duniya. Ba za a rasa samun sabanin ta fannin tattalin arziki da cinikayya a tsakanin Sin da Amurka ba, amma duk da haka, akwai mafita idan sun dinga yin shawarwari da juna. A gaba, ya kamata sassan biyu su tabbatar da daidaito da shugabannin kasashen biyu suka cimma, musamman ma ya kamata Amurka ta samar da yanayin kasuwanci mai adalci ga kamfanonin kasar Sin, ciki har da Tiktok, kuma ta yi hadin gwiwa da kasar Sin, don su kiyaye nasarorin da suka cimma a shawarwarin, don tabbatar da hada-hadar tattalin arziki da cinikayya a tsakaninsu yadda ya kamata. (Lubabatu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 
  • Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban
  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa
  • Akalla Falasdinawa 78 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila a Gaza
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba
  • Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu
  • Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato