A wani cigaba makamancin haka, dakarun Mallam Fatori suma sun daƙile wani yunƙurin hari daga ‘yan ta’adda da suka zo ta wurare daban-daban.

Ya ce bayan sa’o’i na musayar wuta, dakarun sun bi ‘yan ta’addan da suka tsere, inda suka hallaka da dama, wasu kuma suka gudu da raunukan harbin bindiga. An kuma kwato muggan makamai da dama kamar bindigogi AK-47, da bindigar kakkaɓo jirgi (RPG), da sauran kayayyakin yaƙi.

Yanzu haka Sojojin na ci gaba da sintiri a yankin, tare da goyon bayan jiragen sama da na leƙen asiri.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Boko Haram ISWAP

এছাড়াও পড়ুন:

Guardian: Isra’ila Tana Kai Wa Makarantun Dake Dauke Da ‘Yan Gudun Hijira a gaza Hari, Tana Sane Da Hakan

Jaridar Guardian ta ta kasar Birtaniya ta bada labarin cewa, Hare-haren da sojojin HKI su ka kai kan wata makaranta, inda yan gudun hijira Falasdinawa suke samun mafaka da gangan suka yi shi, suna sane, kuma a halin yanzu suna Shirin kai wa wasu makarantun guda 4 hare-hare nan gaba.

Jaridar ta kara da cewa: Isra’ila ta ayyana wasu Karin makarantu wadanda Falasdinawa suke samun mafaka a cikinsu domin kai musu hare-hare a nan gaba. A lokacinda HKI ta kasa ganin mayakan Hamas a fili sojojinta sun koma kan kissan Falasdinawa fararen hula, wadanda suke samun mafaka a makarantu.

A cikin watanni da suka gabata sojojin mamayar sun kai hare-hare akan wasu gine-ginen 6 wadanda suka kasance makarantu ne, wadanda Falasdinawa maza da mata da yara suka maidasu wuraren fakewa daga hare-haren sojojin HKI, suka kai mutane 120 ga shahada.

A ranar Litinin da ta gabata ce, sojojin mamayar suka kai wani harin a kan makarantar “A’ishiyya” wacce ta zama sansanin ‘yan gudun  hijira a garin Deir-Balah’ na tsakiyar Gaza. Suka kuma kai falasdinawa da dama ga shahada.

Amma suka bada sanarwan cewa, ‘yan ta’adda ne suke fakewa a cikin makarantar, ba tare da sun gabatar da wata shaida ta tabbatar da hakan ba.

 A bisa wani rahoton na MDD ta fitar, ta ce kaso 95% na makarantun Gaza, sun lalace, a yayin da wasu kimani  400 su ka rushe gaba daya saboda hare-haren sojojin yahudawan.  A ranar 26 ga watan Mayu da ya shude ne, sojojin HKI suka kai hare-harei a kan makarantar “Fahmi-Jarjawi” da take cike da ‘yan gudun hijira wanda shi ma ya yi sanadiyyar shahadar Faladinawa da dama.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
  • Ministan Tsaro Ya Yi Gargadin Sake Dawowar Boko Haram Na Barazana Ga Nijeriya
  • ‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 
  • Sojoji sun dakile hare-haren ‘Yan Boko Haram biyu a Borno
  • Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 
  • An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja
  • Jami’an DSS sun kashe ’yan bindiga 45 a Neja
  • DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja
  • Guardian: Isra’ila Tana Kai Wa Makarantun Dake Dauke Da ‘Yan Gudun Hijira a gaza Hari, Tana Sane Da Hakan