Aminiya:
2025-07-04@20:17:09 GMT

Barazanar Yajin Aiki: Abuja da wasu jihohi 3 za su faɗa cikin duhu

Published: 5th, June 2025 GMT

Ma’aikatan Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Abuja (AEDC), sun yi barazanar shiga yajin aiki, wanda hakan zai iya jefa Abuja, Kogi, Nasarawa da Jihar Neja cikin duhu.

Ma’aikatan, ƙarƙashin ƙungiyoyin NUEE da SSAEAC, sun ce kamfanin ya gaza cika alƙawuran da ya ɗauka bayan sun dakatar da wani yajin aiki a watan Nuwamban 2024.

A shekara 25, na kashe tiriliyan 161 wajen inganta lafiya a Afirka – Bill Gates Direbobi sun toshe babbar hanyar Kogi sakamakon harbe abokan aikinsu

Ƙorafe-ƙorafen nasu sun haɗa da rashin biyan kuɗin fansho na tsawon watanni 16, rashin ƙarin girma, rashin kula da lafiyar ma’aikata.

Sun kuma ce an ƙi biyansu ladan aiki na shekarar 2024 duk da cewa sun taimaka wajen samar da kuɗin shiga har Naira biliyan 94 cikin watanni uku.

“Mun yarda mun dakatar da yajin aiki a watan Nuwamban 2024 saboda alƙawuran da kamfanin ya ɗauka, amma har yanzu ba a aiwatar da su ba,” in ji jagoran ƙungiyar, Opaluwa Eleojo Simeon.

“Ma’aikata suna fama da matsin lamba da rashin kulawa, har wasu na mutuwa saboda halin da suke ciki.”

Rosemary Odeh, wata shugabar ƙungiyar, ta ƙara da cewa: “Mun shirya komawa yajin aiki a kowane lokaci. Ba za mu ja da baya ba har sai mun samu adalci. Wannan gwagwarmaya ba za ta tsaya ba.”

Ƙungiyoyin sun umarci mambobinsu da su fara shiri a dukkanin yankunan AEDC.

Idan aka fara yajin aikin, al’umma a yankunan da abin ya shafa na iya fuskantar rashin wutar lantarki na tsawon lokacin yajin aikin zai shafe.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Nasarawa Wutar Lantarki Yajin aiki

এছাড়াও পড়ুন:

Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump

“Ba za su samu tayin da ya fi wannan ba abu zai ƙara muni idan suka ƙi.”

Har yanzu babu martani daga jami’an Isra’ila kan iƙirarin Trump ba.

Tattaunawar neman tsagaita wuta ta tsaya cak tun watanni da suka gabata saboda rashin jituwa kan matakin da za a ɗauka bayan an daina faɗa.

Isra’ila tana son ta ci gaba da samun damar kai farmaki idan ta ga dama, amma Hamas tana so a daina faɗa gaba ɗaya.

Ana sa ran Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, zai kai ziyara fadar White House a mako mai zuwa.

Trump ya ce zai yi magana da Netanyahu domin ganin an kawo ƙarshen yaƙin.

A farkon shekarar nan, wani ƙoƙari na tsagaita wuta ya rushe a watan Maris bayan Isra’ila ta kai wani farmaki ba tare da sanarwa ba a Gaza wanda rahotanni suka ce ya hallaka fiye da mutane 300.

Daga baya Netanyahu ya kare farmakin, inda ya bayyana cewa Hamas ta ƙi sakin fursunon Isra’ila da ke hannunta.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja
  • Jalali: Mun  Hana Fitowar Sanadarorin Nukiliya Ta Hanyar Aiki Da Ka’idojin Tsaro
  • Ambaliya da iska sun rushe gidaje 171 a watanni biyu a Gombe – SEMA
  • Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 1,191, Sun Ceto 543 Cikin Watanni Uku
  • Buhari ba ya cikin mawuyacin hali — Bashir Ahmad
  • ’Yansanda Sun Ceto Ɗan Ghana, Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 3
  • Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar
  • Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5
  • Me Ya Sa JKS Mai Tsawon Tarihin Sama Da Shekaru 100 Ta Dore A Kan Mulki
  • Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump