Aminiya:
2025-06-13@09:40:56 GMT

Barazanar Yajin Aiki: Abuja da wasu jihohi 3 za su faɗa cikin duhu

Published: 5th, June 2025 GMT

Ma’aikatan Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Abuja (AEDC), sun yi barazanar shiga yajin aiki, wanda hakan zai iya jefa Abuja, Kogi, Nasarawa da Jihar Neja cikin duhu.

Ma’aikatan, ƙarƙashin ƙungiyoyin NUEE da SSAEAC, sun ce kamfanin ya gaza cika alƙawuran da ya ɗauka bayan sun dakatar da wani yajin aiki a watan Nuwamban 2024.

A shekara 25, na kashe tiriliyan 161 wajen inganta lafiya a Afirka – Bill Gates Direbobi sun toshe babbar hanyar Kogi sakamakon harbe abokan aikinsu

Ƙorafe-ƙorafen nasu sun haɗa da rashin biyan kuɗin fansho na tsawon watanni 16, rashin ƙarin girma, rashin kula da lafiyar ma’aikata.

Sun kuma ce an ƙi biyansu ladan aiki na shekarar 2024 duk da cewa sun taimaka wajen samar da kuɗin shiga har Naira biliyan 94 cikin watanni uku.

“Mun yarda mun dakatar da yajin aiki a watan Nuwamban 2024 saboda alƙawuran da kamfanin ya ɗauka, amma har yanzu ba a aiwatar da su ba,” in ji jagoran ƙungiyar, Opaluwa Eleojo Simeon.

“Ma’aikata suna fama da matsin lamba da rashin kulawa, har wasu na mutuwa saboda halin da suke ciki.”

Rosemary Odeh, wata shugabar ƙungiyar, ta ƙara da cewa: “Mun shirya komawa yajin aiki a kowane lokaci. Ba za mu ja da baya ba har sai mun samu adalci. Wannan gwagwarmaya ba za ta tsaya ba.”

Ƙungiyoyin sun umarci mambobinsu da su fara shiri a dukkanin yankunan AEDC.

Idan aka fara yajin aikin, al’umma a yankunan da abin ya shafa na iya fuskantar rashin wutar lantarki na tsawon lokacin yajin aikin zai shafe.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Nasarawa Wutar Lantarki Yajin aiki

এছাড়াও পড়ুন:

Ɗan Ƙasar Indiya Da Wasu 12 Sun Gurfana A Kotu Kan Satar Wa Dangote Dizal Na Naira Biliyan 4

Binciken ya nuna cewa, mutum biyu daga cikin wadanda ake zargin ma’aikatan Dangote ne kai tsaye, yayin da sauran ke aiki da kamfanonin da ke da alaka da safarar mai daga matatar Dangote zuwa wuraren ajiya na kamfanin da ke Ibese da Obajana.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NAJERIYA A YAU: Rashin Aikin Yi Da Hanyoyin Magance Su A Najeriya
  • Isra’ila ta kaddamar da hare-hare kan yankuna da dama na Iran ciki har da Tehran
  • Sojoji Sun Kashe Auta, Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda Da Wasu 13 a Jihar Zamfara
  • EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Zargi Aikata Damfara A Intanet A Kaduna
  • Rashin wutar lantarki ya durƙusar da kasuwanci a Arewa Maso Gabas
  • Hajjin 2025: Jihohi 11 sun kashe N6.2bn wajen tallafa wa Alhazai
  • Ɗan Ƙasar Indiya Da Wasu 12 Sun Gurfana A Kotu Kan Satar Wa Dangote Dizal Na Naira Biliyan 4
  • Za a dauke wa jihohin Arewa maso Gabas wutar lantarki na tsawon kwana 4
  • DAGA LARABA: Dalilan Rashin Jituwa Tsakanin Marasa Lafiya Da Jami’an Kiwon Lafiya
  • Ƙungiyar G-5 Ta Ceto Nijeriya Daga Faɗa Wa Rikici — Wike