Leadership News Hausa:
2025-06-06@07:03:36 GMT

Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

Published: 4th, June 2025 GMT

Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

A nasa bangare kuma, David Perdue ya ce, shugaba Donald Trump yana matukar girmama shugaba Xi Jinping, kuma yana da muhimmanci a ci gaba da karfafa mu’amala dake tsakanin shugabannin biyu. A matsayin jakadan kasar Amurka a kasar Sin, yana fatan yin mu’amala da bangaren Sin yadda ya kamata, bisa ka’idar girmama juna, da sauraron ra’ayoyin juna.

(Mai Fassara: Maryam Yang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu ya gana da Fubara a Legas

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya gana da gwamnan Jihar Ribas da aka dakatar, Siminalayi Fubara, a gidansa da ke Legas.

Wannan ganawar na cikin ƙoƙarin warware rikicin siyasa da ya addabi jihar.

Jami’an DSS sun kashe ’yan bindiga 45 a Neja ’Yan sanda sun sake hana hawan Sallah a Kano

Fubara, ya samu saɓani da ubangidansa na siyasa, Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, bayan hauwansa mulki.

Saɓani kan ikon mallakar kuɗin jihar da naɗin muƙamai ya janyo rarrabuwar kawuna a cikin gwamnatin jihar da kuma majalisar dokokin jihar.

A watan Maris 2025, Shugaba Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci a jihar Ribas tare da dakatar da Gwamna Fubara, mataimakiyarsa, da kuma ‘yan majalisar dokokin jihar baki ɗaya.

Ya naɗa tsohon Hafsan Soja, Vice Admiral Ibokette Ibas (mai ritaya), a matsayin kantoma da zai kula da harkokin jihar.

“Tun da rikicin ya ci gaba da faruwa, babu yadda za a yi gwamnati mai bin doka da ƙa’ida ta ci gaba,” in ji Shugaba Tinubu a wani jawabi da ya yi.

“Komai ya ta tsaya cak a jihar tun da aka fara rikicin.”

“Gwamnan… ya rushe majalisar dokoki tun ranar 13 ga wata. Disamban 2023, kuma har yanzu bai gyara ta ba,” in ji Tinubu.

“Duk ƙoƙarina na yin sulhu babu abin da ya sauya.”

Duk da cewa ba a bayyana cikakken bayani kan ganawar da suka yi ba, an ce hakan na cikin ƙoƙarin samar da zaman lafiya tsakanin ɓangarorin biyu.

Wannan ganawar ta biyo bayan wata ganawa da suka yi a Landan watanni da suka gabata.

Majalisar Tarayya ta goyi bayan matakin Tinubu, kuma ta buƙaci a kawo ƙarshen dokar ta-ɓaci cikin watanni shida tare da kafa kwamitin sulhu domin warware matsalar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho
  • Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama
  • Trump ya haramtawa ‘yan kasashen duniya 12 shiga Amurka
  • Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus
  • Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa
  • Tinubu ya gana da Fubara a Legas
  • Sin Da Masar Sun Cimma Yarjejeniyar Kafa Cibiyar Harkokin Kasuwanci Ta Sabon Birnin Masar 
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce: Alakar Iran Da Lebanon Tarihi Ce Mai Tushe Da Ta Ginu Kan Mutunta Juna
  • Kasar Sin: Amurka Ta Yi Matukar Kawo Cikas Ga Yarjejeniyar Da Aka Cimma A Tattaunawar Geneva