Medvedev : babu makawa Rasha za ta mayar da martani mai zafi ga hare-haren kyiv
Published: 4th, June 2025 GMT
Rasha ta ce hare-haren Ukraine a kan yankunanta, musamman na baya-bayan nan zasu fuskanci martani mai zafi.
Da yake sanar da hakan Mataimakin shugaban kwamitin sulhu na Tarayyar Rasha Dmitry Medvedev ya ce, sojojin kasar za su ci gaba da kai farmakin har sai an kawar da makiya gaba daya.
Ya kuma kara da cewa babu makawa Rasha za ta mayar da martani kan ayyukan zagon kasa da sojojin Ukraine suka yi.
A cewarsa, za a ci gaba da kai hare-hare ba tare da kakkautawa ba, kuma wadanda ke da alhakin wadannan ayyuka.
Hukumar tsaro ta Ukraine dai ta ce an kai wa wata gada mai muhimmanci hari da ta hada Rasha da yankin Crimea da bamabamai.
Ta ce an jera bamabaman ne masu nauyin kilogiram 1,100 a cikin ruwa na tsawon watanni kuma aka tashe su daga nesa jiya Talata.
Gadar da ake kiran ta Kerch, Rasha ce ta gina ta bayan ta mamaye yankin na Crimea a 2014 daga hannun Ukraine.
Karo na biyu kenan ana kai wa gadar hari tun bayan barkewar yaki tsakaninsu a 2022.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
DSS ta kama Ɗan Bello a Kano
Hukumar Tsaro ta DSS ta saki matashin nan mai barkwanci, Bello Habib Galadanci, jim kaɗan bayan sun kama shi a Jihar Kano.
Jami’an DSS sun kama Dan Bello ne a Filin Jirgin Sama na Malam Aminu Kano kuma wasu majiyoyi na zargin daga Abuja jami’an suke.
Aminiya ta gano saukar matashin da ke zaune a ƙasar China a Najeriya ke da wuya jami’an DSS suka yi awon gaba da shi.
Sai dai kuma rahotanni da muka samu daga bisani sun nuna cewa jami’an tsaron sun sake shi, bayan ya yi ’yan mintoci a hannunsu.
Kawo yanzu dai babu bayani daga hukumomin tsaro ko Ɗan Bello game da dalilin tsarewar da aka yi masa da kuma abin da ya wakana tsakaninsu.
Ɗan Bello dai ya yi ƙaurin suna wajen yin bidiyon barkwanci kan matsalolin shugabanci da cin hanci a Najeriya.
A baya-bayan nan sakonni da ya wallafa kan matsalar fanshon ’yan sanda da ta matsalar albashin malaman jami’a sun ɗauki hankali matuƙa.
Karin bayani na tafe.