Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-07-23@22:46:40 GMT

ROOSC Ta Kaddamar Da Rabon Kayan Koyon Karatu A Kaduna

Published: 4th, June 2025 GMT

ROOSC Ta Kaddamar Da Rabon Kayan Koyon Karatu A Kaduna

ROOSC Ta Kaddamar Da Rabon Kayan Koyon Karatu a Karamar Hukumar Kaduna Sout

Shirin Dawo da Yara Makaranta na Gwamnatin Jihar Kaduna Mai suna ROOSC ya kaddamar da rabon kayan koyon karatu ga dalibai a Karamar Hukumar Kaduna ta Kudu, Jihar Kaduna.

An gudanar da bikin kaddamarwar ne a Makarantar Firamare ta LEA da ke Unguwar Mu’azu, inda manyan masu ruwa da tsaki kan harkar ilimi, musamman shugabannin addini da na al’umma, suka halarta.

Da yake jawabi a wajen taron, Ko’odinetan ROOSC a Jihar Kaduna, Mr. Ezra Angai, ya bayyana cewa wannan shiri hadin gwiwa ne tsakanin Gwamnatin Jihar Kaduna da abokan ci gaba da kuma kungiyoyin aiwatar da shirin, domin inganta samun ilimi mai nagarta ga yaran da ba sa zuwa makaranta.

Ya bayyana cewa, ana aiwatar da shirin ne karkashin kulawar Ma’aikatar Ilimi ta jihar tare da hadin gwiwar kungiyoyin Save the Children da UNICEF.

“An samu kudade daga bashin sauki da tallafin da Bankin Raya Kasashen Musulmi (Islamic Development Bank) ya bayar domin aiwatar da wannan shiri,” in ji shi.

Mr. Angai ya ce, Gwamnatin Jihar Kaduna ta samu bashin sauki da tallafi domin magance matsalar yawaitar yaran da ba sa zuwa makaranta a fadin jihar.

Ya kara da cewa, shirin zai gina sabbin makarantu guda 102 tare da gyara wasu 170 da ke aiki a yanzu, inda ake sa ran samun kimanin yara 200,000 da ba sa zuwa makaranta a kan gaba a cikin shekara hudu a fadin kananan hukumomi 23 na jihar.

Shi ma da yake jawabi, Jagoran Save the Children a jihar, Malam Tanko Mohammed Langaya, ya bayyana cewa shirin ROOSC yana da kudurin raba kayan koyon karatu da koyarwa sama da 500,000 ga dalibai a makarantu a matsayin wani muhimmin bangare na aiwatar da shirin.

“Wadannan kayan karatu ba wai na kari ba ne kawai, su ne tushen ilimi mai nagarta. Tabbatar da cewa kowane yaro yana da kayan karatu masu dacewa da shekarunsa da al’adarsa da kuma masu jan hankali, muhimmin mataki ne wajen samar da ingantaccen daidaito da ilimi ga kowa da kowa a Jihar Kaduna.”

Ko’odinetan shirin daga Save the Children, Mr. Emmanuel Mbursa, ya jaddada muhimmancin raba kayan karatu guda 100,000, yana mai cewa hakan babbar nasara ce a kokarin dawo da yaran da suka daina zuwa makaranta cikin tsarin ilimin gargajiya.

Ya kuma bayyana bukatar samun goyon bayan al’umma domin dorewar shirin.

A nasa jawabin, Daraktan Tsare-tsare a Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Kaduna, Mista Salisu Bala, ya ce shirin na ROOSC yana da nufin bai wa yara ‘yan shekaru 6 zuwa 11 da matasa ‘yan shekaru 12 zuwa 18 da ke wajen makaranta damar samun ilimin firamare mai inganci.

Tun da farko, Shugaban Kwamitin Gudanar da Makarantun Firamare SBMC na Kaduna South, Alhaji Usman Sani, wanda kuma shi ne Hakimin Badikko, ya jaddada rawar da ilimi ke takawa wajen magance matsalolin rashin tsaro da matsin tattalin arziki a kasar.

Ya bukaci iyaye da shugabannin al’umma da su tabbatar cewa dukkan yara masu shekaru na zuwa makaranta suna halartar makaranta, yana mai bayyana damuwa kan rashin isasshen samun ilimin yara kanana a wasu yankunan jihar.

Alhaji Usman Sani ya yabawa Gwamna Uba Sani bisa kudurinsa na samar da ilimi ga kowa da kowa, yana mai cewa shirin ROOSC wata babbar hanya ce ta tabbatar da ingantacciyar makoma ga yaran Jihar Kaduna.

A halin yanzu, kananan hukumomi tara aka riga aka zaba domin rabon kayan koyon karatu. Sun hada da: Kaduna South, Igabi, Kaduna North, Sabon Gari, Soba da Lere.

Sauran sune: Kachia da Jema’a da kuma Kauru.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Rabo zuwa makaranta Jihar Kaduna

এছাড়াও পড়ুন:

PSC Ta Amince Da Ɗaga Darajar Jami’an ‘Yan Sanda 12 Daga Matakin CP Zuwa AIG, Da Sauransu

– Emmanuel Adegbola Aina – AIG na wucin gadi, sashen leƙen asiri

– Omolara Ibidun Oloruntola

– Hassan Abdu Yababet – CP, Kwalejin ‘Yan Sanda Jos

– Bretet Emmanuel Simon – CP Jihar Taraba

– Enyinnaya Inonachi Adiogu – CP, FCID, Gombe

– Aminu Baba Raji – CP, FCID Alagbon

– Mohammed Mu’azu Usman – CP, Tashoshin Gabas, P/Harcourt

– Festus Chinedu Oko – AIG na wucin gadi, sashen DLS, Hedkwatar

– Ronke Nurat Okunade – CP, SFU FCID Annex, Lagos

Kazalika, PSC ta amince da:

– Ɗaga darajar DCP 16 zuwa CP

– Ɗaga darajar ACP 27* zuwa DCP

– Ɗaga CSP 145 zuwa ACP, ciki har da likitoci, ma’aikatan lafiya, injiniyoyi na jiragen sama, da limamai

– Ɗaga SP 29 (na musamman na sashen kimiyyar sadarwa da aikace-aikace da AFIS) zuwa CSP

– Ɗaga DSP 38 zuwa SP

Wani ACP ɗaya bai samu damar halarta ba, don haka ba a ɗaga darajarsa ba.

Sabbin CP 16 sun haɗa da:

– Uduak Otu Ita

– Sheikh Mohammed Danko

– Charles Ezekwesiri Dike

– Nnana Oji Ama (FCID Intelligence)

– Gabriel Onyilo Eliagwu

– Abiola Reuben Olutunde

– Yakubu Useni Dankaro

– Michael Adegoroye Falade

– Aina Adesola

– Umar Ahmed Chuso

– Emefile Tony Osifo

– Innocent Ilogbunam Anagbado

– Musa Mohammed Sani

– Victor Avwerosuo Erivwode (DC SEB, FCID)

– Omoikhudu Philip

– Sylvester Edogbanya

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Kaddamar Da Bikin BIRTV2025 A Beijing
  •  Fiye Da  Kungiyoyin 100 A Duniya Sun Yi Gargadi Akan Halin Yunwa Da HKi Ta Jefa Mutanen Gaza A Ciki
  • NEDC ta raba wa mutanen da ambaliya ta shafa kayan gini a Yobe
  • UNICEF Ya Bukaci Jihar Kano Ta Bai Wa Yara Muhimmanci A Kasafin Kudi
  • Makarantun Kano Za Su Fara Hutun Ƙarshen Zango A Ranar Juma’a – Gwamnati
  • DAGA LARABA: Abubuwan da ya kamata yara su yi yayin hutun makaranta
  • Har Yanzu Yaƙi Da Ta’addanci Ne Babban Muradin Gwamnatina — Tinubu
  • PSC Ta Amince Da Ɗaga Darajar Jami’an ‘Yan Sanda 12 Daga Matakin CP Zuwa AIG, Da Sauransu
  • Manoma A Kaduna Sun Yabawa Irin Masara Na TELA Saboda Juriyarshi Ga Kwari
  • An kaddamar Da Wani Shiri Na Ba ‘Yan Mata 200,000 Tallafin Audugar Mata A Kano