Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-11-03@02:59:53 GMT

ROOSC Ta Kaddamar Da Rabon Kayan Koyon Karatu A Kaduna

Published: 4th, June 2025 GMT

ROOSC Ta Kaddamar Da Rabon Kayan Koyon Karatu A Kaduna

ROOSC Ta Kaddamar Da Rabon Kayan Koyon Karatu a Karamar Hukumar Kaduna Sout

Shirin Dawo da Yara Makaranta na Gwamnatin Jihar Kaduna Mai suna ROOSC ya kaddamar da rabon kayan koyon karatu ga dalibai a Karamar Hukumar Kaduna ta Kudu, Jihar Kaduna.

An gudanar da bikin kaddamarwar ne a Makarantar Firamare ta LEA da ke Unguwar Mu’azu, inda manyan masu ruwa da tsaki kan harkar ilimi, musamman shugabannin addini da na al’umma, suka halarta.

Da yake jawabi a wajen taron, Ko’odinetan ROOSC a Jihar Kaduna, Mr. Ezra Angai, ya bayyana cewa wannan shiri hadin gwiwa ne tsakanin Gwamnatin Jihar Kaduna da abokan ci gaba da kuma kungiyoyin aiwatar da shirin, domin inganta samun ilimi mai nagarta ga yaran da ba sa zuwa makaranta.

Ya bayyana cewa, ana aiwatar da shirin ne karkashin kulawar Ma’aikatar Ilimi ta jihar tare da hadin gwiwar kungiyoyin Save the Children da UNICEF.

“An samu kudade daga bashin sauki da tallafin da Bankin Raya Kasashen Musulmi (Islamic Development Bank) ya bayar domin aiwatar da wannan shiri,” in ji shi.

Mr. Angai ya ce, Gwamnatin Jihar Kaduna ta samu bashin sauki da tallafi domin magance matsalar yawaitar yaran da ba sa zuwa makaranta a fadin jihar.

Ya kara da cewa, shirin zai gina sabbin makarantu guda 102 tare da gyara wasu 170 da ke aiki a yanzu, inda ake sa ran samun kimanin yara 200,000 da ba sa zuwa makaranta a kan gaba a cikin shekara hudu a fadin kananan hukumomi 23 na jihar.

Shi ma da yake jawabi, Jagoran Save the Children a jihar, Malam Tanko Mohammed Langaya, ya bayyana cewa shirin ROOSC yana da kudurin raba kayan koyon karatu da koyarwa sama da 500,000 ga dalibai a makarantu a matsayin wani muhimmin bangare na aiwatar da shirin.

“Wadannan kayan karatu ba wai na kari ba ne kawai, su ne tushen ilimi mai nagarta. Tabbatar da cewa kowane yaro yana da kayan karatu masu dacewa da shekarunsa da al’adarsa da kuma masu jan hankali, muhimmin mataki ne wajen samar da ingantaccen daidaito da ilimi ga kowa da kowa a Jihar Kaduna.”

Ko’odinetan shirin daga Save the Children, Mr. Emmanuel Mbursa, ya jaddada muhimmancin raba kayan karatu guda 100,000, yana mai cewa hakan babbar nasara ce a kokarin dawo da yaran da suka daina zuwa makaranta cikin tsarin ilimin gargajiya.

Ya kuma bayyana bukatar samun goyon bayan al’umma domin dorewar shirin.

A nasa jawabin, Daraktan Tsare-tsare a Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Kaduna, Mista Salisu Bala, ya ce shirin na ROOSC yana da nufin bai wa yara ‘yan shekaru 6 zuwa 11 da matasa ‘yan shekaru 12 zuwa 18 da ke wajen makaranta damar samun ilimin firamare mai inganci.

Tun da farko, Shugaban Kwamitin Gudanar da Makarantun Firamare SBMC na Kaduna South, Alhaji Usman Sani, wanda kuma shi ne Hakimin Badikko, ya jaddada rawar da ilimi ke takawa wajen magance matsalolin rashin tsaro da matsin tattalin arziki a kasar.

Ya bukaci iyaye da shugabannin al’umma da su tabbatar cewa dukkan yara masu shekaru na zuwa makaranta suna halartar makaranta, yana mai bayyana damuwa kan rashin isasshen samun ilimin yara kanana a wasu yankunan jihar.

Alhaji Usman Sani ya yabawa Gwamna Uba Sani bisa kudurinsa na samar da ilimi ga kowa da kowa, yana mai cewa shirin ROOSC wata babbar hanya ce ta tabbatar da ingantacciyar makoma ga yaran Jihar Kaduna.

A halin yanzu, kananan hukumomi tara aka riga aka zaba domin rabon kayan koyon karatu. Sun hada da: Kaduna South, Igabi, Kaduna North, Sabon Gari, Soba da Lere.

Sauran sune: Kachia da Jema’a da kuma Kauru.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Rabo zuwa makaranta Jihar Kaduna

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar

Daga Usman Muhammad Zaria 

 

Majalisar Zartarwa ta Jihar Jigawa ta amince da bayar da rancen kudi ga hukumar gidaje ta jihar domin gina gidaje 52 a Dutse.

A cikin wata sanarwa da kwamishinan yada labarai na jihar, Alhaji Sagir Musa Ahmed ya fitar, ya bayyana cewa gidajen za su kunshi masu dakuna uku da kuma dakuna biyu kowanne.

Ya ce aikin zai kasance a gaban tsohuwar unguwar majalisar dokoki, kusa da hanyar wucewa ta Jami’ar Tarayya da je Dutse, a matsayin wani shiri na asusun gina gidaje karkashin ma’aikatar gidaje, ci gaban birane da tsare-tsaren yankuna, ta hannun hukumar gidaje ta jihar.

Alhaji Sagir ya bayyana cewa, wannan mataki na nuna kudirin gwamnati wajen magance matsalar gidaje a babban birnin jihar, kara habaka ci gaban birane, tare da samar da ayyukan yi ga matasan jihar.

Ya ce an tsara wannan asusu  ne domin tabbatar da dorewa, ta yadda za a ci gaba da zuba jari a ayyukan samar da gidaje masu araha a fadin jihar.

Haka kuma ya kara da cewa, gwamnatin jihar tana da kudirin ci gaba da inganta rayuwar al’ummarta, ta hanyar ayyuka masu amfani da jama’a, da ke inganta walwala, karfafa tattalin arziki, da tallafa wa matasa.

Kwamishinan ya kuma bayyana cewa, majalisar ta amince da bayar da kwangilar gyara da inganta gidan baki guda biyu (Malam Adamu Chiroma House da kuma Senator Francis Ella House) da ke cikin G9 Quarters a Dutse, da kudin sama da naira miliyan 219.7.

Ya ce aikin zai haɗa da cikakken gyara da inganta gine-ginen, gyaran hanyoyin ruwa da kuma girka tankokin  ruwa ga kowanne daga cikin gidajen biyu.

Ya ce hakan na da nufin tabbatar da wadataccen ruwan sha mai dorewa a  wuraren.

Alhaji Sagir Musa Ahmed ya kara da cewa, amincewar da aka yi da wannan kwangila na nuna jajircewar gwamnatin jihar wajen kula da dukiyar jama’a da kuma tabbatar da cewa gine-ginen gwamnati suna cikin yanayi mai kyau da nagarta.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gidauniyar IRM Da KADCHMA, Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna
  • Araqchi: Da Hadin Bakin Amurka, Gwamnatin Isra’ila ta kaddamar Da Hari Kan Kasar Iran
  • Hamas ta musanta zargin Amurka na cewa tana sace kayan agaji a Gaza
  • Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
  • Sanata Sunday Marshall Katung Ya Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi
  • Shugabannin Kudancin Kaduna za su karrama Janar  Christopher Musa