Shugaban kasar Iran ya jaddada cewa: Amurka da haramtacciyar kasar Isra’ila suna da mugun nufi kan Iran da kasashen musulmi

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya jaddada cewa: Amurka da haramtacciyar kasar Isra’ila na da mugun nufi kan Iran da kasashen musulmi.

A yayin wani jawabi da ta gabatar a wajen juyayin tunawa da rasuwar Imam Khumaini {r.

a}, Pezeshkian ya ce: Haramtacciyar kasar Isra’ila ba za ta iya aikata wani aiki hauka da wauta ba, idan kasashen musulmi suka hada kansu.

Pezeshkian ya kara da cewa: Wadanda ke da’awar kare hakkin bil’adama suna kare “haramtacciyar kasar Isra’ila” mai laifi, kuma suna ci gaba da adawa da shirin makamashin nukiliyar Iran na zaman lafiya.

Ya ci gaba da cewa: “Babu mutum mai ‘yanci da zai yarda da zalunci da girman kai, kuma Iran ba zata yarda da shi ba.”

Pezeshkian ya bayyana cewa: “Za su dakile duk wani makirce-makircen abokan gaba kuma ba za su taba yin watsi da ‘yancinsu na nukiliya da na kimiyya ba.”

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Isra ila Pezeshkian ya

এছাড়াও পড়ুন:

Nukiliya : Iran za ta bayar da amsa ga shawarar Amurka cikin kwanaki masu zuwa

Ministan harkokin wajen kasar Abbas Araghchi ya sanar da cewa, nan da kwanaki masu zuwa Iran za ta mayar da amsa kan shawarar da Amurka ta gabatar kan shirin nukiliyar kasar na zaman lafiya.

A cewarsa, shawara da Amurka ta gabatar tana bukatar zurfafa bincike.

M. Araghchi, ya bayyana hakan ne ziyarar da yake a birnin Beirut, na kasar Lebanon inda ya jaddada cewa, amsar da Iran za ta mayar zata kasance bisa tsarin Jamhuriyar Musulunci ta Iran da manufofinmu da kuma kare muradun al’ummar Iran.

Ya nanata cewa inganta makamashin Uranium tamkar “jan layi” ne ga Iran, yana mai cewa Tehran ba ta bukatar neman izini daga kowa don ci gaba da ayyukanta da suka dace da shari’a kuma halaliyarta.

Ya ce inganta sinadarin Uranium ya zama abin alfahari ga al’ummar Iran kuma wannan nasara ta ilimi ta samo asali ne daga kokari da basirar masana kimiyyar Iran, kuma ba abu ne mai sauki da za a yi watsi da ita.

Araghchi ya kuma tunatar da cewa, Iran ta ta sha wahala sosai fiye sakamakon shekaru 20 na takunkumin tattalin arziki mai tsanani da Amurka ta kakaba, da kuma kisan wasu masana kimiyyar nukiliyarta tun farkon shekarun 2010, wanda jami’an gwamnatin Isra’ila suka shirya.

Ministan harkokin wajen na Iran ya kara da cewa sama da Iraniyawa miliyan daya ne ke bukatar magunguna da cibiyar bincike ta Tehran ta samar, don haka ci gaba da sarrafa sinadarin Uranium a Iran ya zama wajibi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Kasar Iran Ya Tattauna Ta Wayar Tarko Da Tokwaransa Na Masar Da Saudiya
  • Shugaban Kasar Rasha Vladimir Putin Zia Kawo Ziyara Tehran Nan Kusa
  • Qolibuf: Kungiyar BRICS Dama Ci Ta Kauda Danniyar Amurka A Kan Kudaden Kasashen Duniya
  • Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Ben Gurion Na Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Ben Gurium Na Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Nukiliya : Iran za ta bayar da amsa ga shawarar Amurka cikin kwanaki masu zuwa
  • Iran ta bukaci hadin kan al’ummar Lebanon wajen warware matsalolin kasar
  • Tsohon Jami’in Gwamnatin Biden Na Amurka Ya Tabbatar Da Cewa Isra’ila Ta Tafka Laifukan Yaki
  • Iran Ta Yi Watsi Da Da’awar Kungiyar Hadin Kan Kasashen Larabawa Na Da’awar Mallakar Wasu Yankunan Iran