Rundunar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta jaddada haramcin gudanar da hawan Durbar na shagulgulan Babbar Sallah.

Wannan sanarwar na cikin wata takarda da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya sanya wa hannu, kuma aka rabawa manema labarai a Kano.

Sanarwar ta bayyana cewa an sanya wannan doka ne bisa rahotannin sirri da ke nuna cewa wasu bata-gari da masu daukar nauyinsu na shirin amfani da hawan Durbar domin tayar da hankali da barazana ga tsaro da doka a jihar.

Rundunar ta taba sanya irin wannan haramci a lokacin bukukuwan Sallah ƙarama da suka gabata, kuma an yanke shawarar ci gaba da dokar har zuwa Sallah Babba.

Sanarwar ta ƙara da cewa rundunar ta ɗauki matakan kariya tun kafin lokaci domin tabbatar da zaman lafiya da tsaron rayuka da dukiyoyi a fadin jihar.

“An shawarci masu ibada da su kasance masu bin doka da oda tare da gudanar da bukukuwan cikin lumana. Rundunar ta fitar da wasu ƙa’idojin tsaro da suka haɗa da: hawan doki wato (Kilisa),da tseren motoci ko tuki cikin ganganci da hatsari, da mallakar bindiga ko wani makami ba bisa ka’ida ba ko nuna su a fili, da kuma ɗaukar kaya marasa amfani ko masu haɗari da ka iya jawo shakku ko firgici.

Rundunar ta shawarci iyaye da su ja kunnen ‘ya’yansu, su guji shiga cikin ayyukan bata-gari ko baragurbi.

Rundunar ta kuna sha alwashin aiwatar da doka ba tare da rangwame ba.

 

Abdullahi Jalaluddeen

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Durbar Rundunar ta

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnn Zamfara Ya Ba Ma’aikata Da ‘Yan Fansho Barka Da Sallah

Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara ya amince da biyan ma’aikatan gwamnati da ‘yan fansho da ke fadin jihar kyautar Sallah (Eid-el-Kabir) a matsayin alawus-alawus da ake yi a fadin jihar domin nuna tausayi da jajircewa wajen kyautata rayuwar ma’aikata.

 

Kwamishinan yada labarai da al’adu na jihar, Mahmud Muhammad Dantawasa ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a Gusau.

 

A cewar sanarwar, matakin na Gwamnan na da nufin rage wa ‘yan kasa matsalar kudi a lokacin bukukuwan Sallah da kuma ba su damar gudanar da bukukuwan cikin farin ciki da mutuntawa.

 

Gwamnan wanda a halin yanzu yake aikin hajji a birnin Makkah na kasar Saudiyya ya mika gaisuwar Sallah ga al’ummar Zamfara.

 

A cikin sakonsa, ya yi kira ga mazauna yankin da su yi amfani da wannan biki wajen yin tunani, addu’a, da hadin kai, tare da jaddada dabi’u na tausayi da sadaukarwa da lokacin Eid-el-Kabir.

 

“Ina matukar godiya ga Allah Madaukakin Sarki da Ya ba mu damar sake shaida wani Idi,” in ji Gwamna Lawal. “A yayin da muke bikin, ina kira gare mu da mu yi tunani a kan jigon wannan hadin kai, sadaukarwa, da kuma tausayi, mu yi wa jiharmu ta Zamfara addu’a da kuma al’ummarmu Nijeriya.”

 

Daga nan sai ya yi kira ga ‘yan kasa da su yi murna cikin aminci da bin doka da oda a duk lokacin bukukuwan Sallah, yana mai cewa zaman lafiya da tsaro su ne tushen ci gaba mai ma’ana.

 

Gwamnatin Gwamna Lawal ta ci gaba da ba da fifiko kan jin dadin ma’aikatan gwamnati da wadanda suka yi ritaya, kuma ana ganin amincewa da lamunin Sallah a matsayin wani abin da ke nuni da tsarin shugabancinsa na farko na mutanensa.

 

Ma’aikatar yada labarai da al’adu ta kuma bi sahun Gwamnan wajen taya al’ummar Musulmi da daukacin al’ummar Jihar Zamfara murnar Sallah lafiya.

 

REL/AMINU DALHATU.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mun gurfanar da mutum 29 a kotu kan zargin kashe DPO a Kano – ’Yan sanda
  • Bukukuwan sallah tare da Malta Guinness a Birnin Kano
  • Mahajjata kusan miliyan biyu na hawan Arfa a Saudiyya
  • Sallah: ’Yan sanda sun yi alƙawarin tabbatar da tsaro a Gombe
  • Sallah: Mun shirya samar da tsaro a Yobe — ’Yan Sanda
  • ’Yan sanda sun sake hana hawan Sallah a Kano
  • ‘Yansanda A Kano Sun Gargaɗi Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah
  • ‘Yansanda A Kano Sun Gargadi Sarki Sanusi Kan Yekuwar Fitowa Hawan Sallah
  • Gwamnn Zamfara Ya Ba Ma’aikata Da ‘Yan Fansho Barka Da Sallah