Rundunar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta jaddada haramcin gudanar da hawan Durbar na shagulgulan Babbar Sallah.

Wannan sanarwar na cikin wata takarda da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya sanya wa hannu, kuma aka rabawa manema labarai a Kano.

Sanarwar ta bayyana cewa an sanya wannan doka ne bisa rahotannin sirri da ke nuna cewa wasu bata-gari da masu daukar nauyinsu na shirin amfani da hawan Durbar domin tayar da hankali da barazana ga tsaro da doka a jihar.

Rundunar ta taba sanya irin wannan haramci a lokacin bukukuwan Sallah ƙarama da suka gabata, kuma an yanke shawarar ci gaba da dokar har zuwa Sallah Babba.

Sanarwar ta ƙara da cewa rundunar ta ɗauki matakan kariya tun kafin lokaci domin tabbatar da zaman lafiya da tsaron rayuka da dukiyoyi a fadin jihar.

“An shawarci masu ibada da su kasance masu bin doka da oda tare da gudanar da bukukuwan cikin lumana. Rundunar ta fitar da wasu ƙa’idojin tsaro da suka haɗa da: hawan doki wato (Kilisa),da tseren motoci ko tuki cikin ganganci da hatsari, da mallakar bindiga ko wani makami ba bisa ka’ida ba ko nuna su a fili, da kuma ɗaukar kaya marasa amfani ko masu haɗari da ka iya jawo shakku ko firgici.

Rundunar ta shawarci iyaye da su ja kunnen ‘ya’yansu, su guji shiga cikin ayyukan bata-gari ko baragurbi.

Rundunar ta kuna sha alwashin aiwatar da doka ba tare da rangwame ba.

 

Abdullahi Jalaluddeen

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Durbar Rundunar ta

এছাড়াও পড়ুন:

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

“Bayan karbar mukaminsa na sabon kwamandan hukumar NSCDC na jihar Kano, kwamared Bala Bodinga ya umurci jami’ansa da su sadaukar da kansu ga muhimmin aiki na tabbatar da amincin muhimman kadarori da ababen more rayuwa na kasa.

 

“Kwamandan jihar ya ba da umarnin cewa, ba dare ba rana, cikin sa’o’i 24, dole jami’an hukumar su rika yin sintiri da sanya ido domin dakile ayyukan barayi da masu aikata laifuka a lunguna da sako na jihar,” inji shi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwara ETF Ya Dauki Nauyin Karatun Fitattun Dalibai A Matakin Sakandare
  • Tinubu ya janye dokar ta-ɓaci da ya sanya a Ribas
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi
  • NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • Makaman ‘Drons’ Na Yemen Sun Fada Kan Wurare Masu Muhimmanci A  HKI
  • Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”
  • ’Yan sanda sun sasanta rikicin asibitin AKTH da KEDCO