Kasa ta danne almajirai 11 sun mutu a Kaduna
Published: 4th, June 2025 GMT
Wasu almajirai su 11 sun rasa rayukansu bayan kasa ta danne su a kauyen ’Yardoka da ke karamar hukumar Kubau ta jihar Kaduna.
Bayanai sun nuna almajiran sun rasu ne lokacin da suke tsaka da hakar kasa domin taya malaminsu buga bulon kasa da zai yi gini da shi.
Lamarin ya faru ne wajen misalign karfe 1:45 na ranar Litinin.
Almajiran dai da aka bayyana rasuwar tasu sun hada da Muntari Abdulkadir da Aliyu Abba da Ali Umar da Mubarak Haruna da Usain Isa da Yusuf Shafiu da Mujitafa Jibril da Yusha’u Saidu da Aliyu Abdu da Hamisu Mohammed da kuma Ali Abdulmumini, dukkansu ’yan shekaru 10 zuwa 15 ne.
Wasu daga cikinsu dai ’yan garin da lamarin ya faru ne, yayin da wasu daga ciki suka fito daga makwabtan garin a yankin Damau.
Kazalika, an samu nasarar ceto wasu mutum bakwai da raunuka a jikinsu, inda aka garzaya da su asibitin garin inda yanzu haka suke can suna samun kulawar ma’aikatan lafiya.
Rundunar ’Yan Sanda ta jihar Kaduna ta tabbatar da faruwar lamarin ta bakin kakakinta a jihar, DSP Mansir Hassan.
Kakakin ya ce jim kadan da samun rahoton faruwar lamarin ne suka aike da jami’ansu wajen bayan sun samu kiran gaggawa.
Ya kuma ce tuni suka kaddamar da bincike domin gano musabbabin faruwar lamarin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Almajirai
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu ya gana da Fubara a Legas
Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya gana da gwamnan Jihar Ribas da aka dakatar, Siminalayi Fubara, a gidansa da ke Legas.
Wannan ganawar na cikin ƙoƙarin warware rikicin siyasa da ya addabi jihar.
Jami’an DSS sun kashe ’yan bindiga 45 a Neja ’Yan sanda sun sake hana hawan Sallah a KanoFubara, ya samu saɓani da ubangidansa na siyasa, Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, bayan hauwansa mulki.
Saɓani kan ikon mallakar kuɗin jihar da naɗin muƙamai ya janyo rarrabuwar kawuna a cikin gwamnatin jihar da kuma majalisar dokokin jihar.
A watan Maris 2025, Shugaba Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci a jihar Ribas tare da dakatar da Gwamna Fubara, mataimakiyarsa, da kuma ‘yan majalisar dokokin jihar baki ɗaya.
Ya naɗa tsohon Hafsan Soja, Vice Admiral Ibokette Ibas (mai ritaya), a matsayin kantoma da zai kula da harkokin jihar.
“Tun da rikicin ya ci gaba da faruwa, babu yadda za a yi gwamnati mai bin doka da ƙa’ida ta ci gaba,” in ji Shugaba Tinubu a wani jawabi da ya yi.
“Komai ya ta tsaya cak a jihar tun da aka fara rikicin.”
“Gwamnan… ya rushe majalisar dokoki tun ranar 13 ga wata. Disamban 2023, kuma har yanzu bai gyara ta ba,” in ji Tinubu.
“Duk ƙoƙarina na yin sulhu babu abin da ya sauya.”
Duk da cewa ba a bayyana cikakken bayani kan ganawar da suka yi ba, an ce hakan na cikin ƙoƙarin samar da zaman lafiya tsakanin ɓangarorin biyu.
Wannan ganawar ta biyo bayan wata ganawa da suka yi a Landan watanni da suka gabata.
Majalisar Tarayya ta goyi bayan matakin Tinubu, kuma ta buƙaci a kawo ƙarshen dokar ta-ɓaci cikin watanni shida tare da kafa kwamitin sulhu domin warware matsalar.