Aminiya:
2025-11-02@06:25:17 GMT

Kasa ta danne almajirai 11 sun mutu a Kaduna

Published: 4th, June 2025 GMT

Wasu almajirai su 11 sun rasa rayukansu bayan kasa ta danne su a kauyen ’Yardoka da ke karamar hukumar Kubau ta jihar Kaduna.

Bayanai sun nuna almajiran sun rasu ne lokacin da suke tsaka da hakar kasa domin taya malaminsu buga bulon kasa da zai yi gini da shi.

Lamarin ya faru ne wajen misalign karfe 1:45 na ranar Litinin.

’Yan sanda sun sake hana hawan Sallah a Kano Ambaliyar Mokwa: Yawan mutanen da suka salwanta ya haura 700

Almajiran dai da aka bayyana rasuwar tasu sun hada da Muntari Abdulkadir da Aliyu Abba da Ali Umar da Mubarak Haruna da Usain Isa da Yusuf Shafiu da Mujitafa Jibril da Yusha’u Saidu da Aliyu Abdu da Hamisu Mohammed da kuma Ali Abdulmumini, dukkansu ’yan shekaru 10 zuwa 15 ne.

Wasu daga cikinsu dai ’yan garin da lamarin ya faru ne, yayin da wasu daga ciki suka fito daga makwabtan garin a yankin Damau.

Kazalika, an samu nasarar ceto wasu mutum bakwai da raunuka a jikinsu, inda aka garzaya da su asibitin garin inda yanzu haka suke can suna samun kulawar ma’aikatan lafiya.

Rundunar ’Yan Sanda ta jihar Kaduna ta tabbatar da faruwar lamarin ta bakin kakakinta a jihar, DSP Mansir Hassan.

Kakakin ya ce jim kadan da samun rahoton faruwar lamarin ne suka aike da jami’ansu wajen bayan sun samu kiran gaggawa.

Ya kuma ce tuni suka kaddamar da bincike domin gano musabbabin faruwar lamarin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Almajirai

এছাড়াও পড়ুন:

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

 

Yayin ganawarsa da firaministan Thailand, Shugaba Xi Jinping ya ce a shirye kasarsa take ta karfafa hadin gwiwa da Thailand kan dabarun samun ci gaba, tare kuma da gabatar da gogewarta na samun ci gaba a sabon zamani, kuma ya yi kira da a gaggauta gina layin dogo tsakanin Sin da Thailand da bunkasa hadin gwiwa a bangaren cinikin amfanin gona da tattalin arziki mai kiyaye muhalli da kuma kirkire kirkiren fasaha. (Mai fassara: FMM)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC October 31, 2025 Daga Birnin Sin Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare October 31, 2025 Daga Birnin Sin Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An yi garkuwa da Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Kebbi
  • CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka
  • Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace
  • ’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi
  • Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 
  • Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar
  • Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan
  • Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare
  • Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi
  • An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo