Kasa ta danne almajirai 11 sun mutu a Kaduna
Published: 4th, June 2025 GMT
Wasu almajirai su 11 sun rasa rayukansu bayan kasa ta danne su a kauyen ’Yardoka da ke karamar hukumar Kubau ta jihar Kaduna.
Bayanai sun nuna almajiran sun rasu ne lokacin da suke tsaka da hakar kasa domin taya malaminsu buga bulon kasa da zai yi gini da shi.
Lamarin ya faru ne wajen misalign karfe 1:45 na ranar Litinin.
Almajiran dai da aka bayyana rasuwar tasu sun hada da Muntari Abdulkadir da Aliyu Abba da Ali Umar da Mubarak Haruna da Usain Isa da Yusuf Shafiu da Mujitafa Jibril da Yusha’u Saidu da Aliyu Abdu da Hamisu Mohammed da kuma Ali Abdulmumini, dukkansu ’yan shekaru 10 zuwa 15 ne.
Wasu daga cikinsu dai ’yan garin da lamarin ya faru ne, yayin da wasu daga ciki suka fito daga makwabtan garin a yankin Damau.
Kazalika, an samu nasarar ceto wasu mutum bakwai da raunuka a jikinsu, inda aka garzaya da su asibitin garin inda yanzu haka suke can suna samun kulawar ma’aikatan lafiya.
Rundunar ’Yan Sanda ta jihar Kaduna ta tabbatar da faruwar lamarin ta bakin kakakinta a jihar, DSP Mansir Hassan.
Kakakin ya ce jim kadan da samun rahoton faruwar lamarin ne suka aike da jami’ansu wajen bayan sun samu kiran gaggawa.
Ya kuma ce tuni suka kaddamar da bincike domin gano musabbabin faruwar lamarin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Almajirai
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu ya bayar da umarnin binciken hare-haren Benuwe
Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya umarci jami’an tsaro da su yi bincike tare da gano waɗanda suka kai hari a Jihar Benuwe, inda aka kashe sama da mutum 100.
Harin ya faru ne a ƙauyen Yelwata da ke Ƙaramar Hukumar Guma a jihar.
Iran ta rataye mutumin da ta kama yana yi wa Isra’ila leƙen asiri KADSEMA da IOM sun fara tantance ɓarnar da ambaliya ta yi a KadunaBayan harin, matasa sun rufe hanyar Lafiya zuwa. Makurdi domin nuna ɓacin ransu.
Zanga-zangar ta ci gaba da gudana har zuwa safiyar ranar Lahadi a birnin Makurdi, babban birnin jihar.
Rundunar ‘yan sandan jihar ta yi amfani da barkonon tsohuwa domin tarwatsa masu zanga-zangar.
A daren ranar Lahadi, Shugaba Tinubu ya wallafa saƙo a a shafin sa na X, inda ya ce dole a kawo ƙarshen wannan kashe-kashe, kuma ya umarci jami’an tsaro su ɗauki mataki don kama duk masu hannu a rikicin.
Tinubu ya kuma buƙaci Gwamnan Jihar Benuwe, Hyacinth Alia, da ya jagoranci tattaunawa da yin sulhu tsakanin manoma da makiyaya domin wanzar da zaman lafiya.
Ya gargaɗi shugabannin siyasa da na al’umma da su guji furucin da ka iya haifar da tarzoma.
Ya ce lokaci ya yi da za a haɗa kai domin warware matsaloli da hanyar gaskiya, adalci da fahimta, domin a samu zaman lafiya a Jihar Benuwe.