Alhazan Jihar Jigawa sun fara ayyukan hajji cike da kwarin gwiwa yayin da aka kaisu Mina daga birnin Makkah, inda za su wuce zuwa Dutsen Arafat domin gudanar da aikin hajjin shekarar 2025.

Aikin hajji na farawa ne daga ranar 8 zuwa 13 ga watan Dhul Hajj a duk shekara, inda ake daukar alhazai zuwa sansanin Mina sannan su wuce zuwa Arafat, zuwa Muzdalifa, sannan Jamarat (Jamratul Akbah), kafin su dawo Makkah inda za su kammala da Dawafi.

Yawancin Alhazan da suka zanta da Rediyon Najeriya sun bayyana cewa, duk da wahalhalun da ke tattare da aikin hajji, sun kuduri aniyar gudanar da hajjin lafiya kuma cikin nasara.

Wasu daga cikin Alhazan daga kananan hukumomin Jahun da Kiyawa, Hajiya Maijidda Abdulhamid da Alhaji Mohammed Abdullahi Idris sun bayyana cewa tsoron Allah da kaunarsa ke basu kwarin gwiwar jure wahalhalun aikin hajji, kasancewar Allah Ya bada tabbacin karbar dukkan addu’o’i, don haka wajibi ne su jure domin babu wani alheri da ke zuwa cikin sauki.

Wani Alhaji daga Dutse, Murtala Sani Lama, ya bayyana cewa aikin hajji yana daga cikin ginshikan Musulunci, kuma kowanne musulmi mai hali yana da hakkin gudanar da shi. Ya kara da cewa a cikin Alkur’ani an bayyana cewa duk wata bukata da Alhaji ya roka za a amsa masa.

Ya kara da cewa wannan tabbacin kadai yana isar masa da kwanciyar hankali wajen shan wahalhalun aikin hajji komai yadda suka kasance.

 

Alhazan sun bayyana ra’ayin cewa kasancewar aikin hajji kira ne daga Allah kuma su baƙinsa ne na musamman, ba wani dogon tafiya ko zafi ko yawan mutane da zai hana su gudanar da ibada.

A cewar koyarwar Musulunci, duk wanda ya gudanar da aikin hajji yadda ya kamata, Allah yana gafarta masa dukkan zunubansa kuma yana bashi sabuwar dama kamar yadda aka haifi sabon jariri.

Haka kuma, a wata hira da Rediyon Najeriya, Darakta Janar na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa, Alhaji Ahmed Umar Labbo, ya ce dukkan abubuwan da suka wajaba domin jin dadin alhazan jihar an tanade su.

“An sanya ma tantin Alhazai  na’urar sanyaya daki (air condition), tare da katifa da filo da kuma bargo ga kowane Alhaji. Kuma saboda zafin rana, mun saka firijin na ruwa tsakanin tantuna domin rage hatsarin kamuwa da matsanancin kishi.”

Labbo ya kara da cewa Alhazai za su rika samun abinci sau uku a rana tare da ruwan sha, da ‘ya’yan itatuwa da kuma lemun kwalba.

Ya shawarci Alhazai da su sanya tsoron Allah a zukatansu, yana mai cewa wannan ne mataki na farko na samun hajji mai kyau da tsari.

 

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa bayyana cewa

এছাড়াও পড়ুন:

Rikici Yana Ci Gaba Da Gudanar A Kasar Sudan Tsakanin Sojoji Da Dakarun Kai Daukin Gaggawa

Rikici tsakanin sojojin Sudan da dakarun kai daukin gaggawa na kasar yana ci gaba da habaka a wurare da dama na kasar

Kasar Sudan dai na fuskantar tabarbarewar harkokin tsaro cikin hanzari, a daidai lokacin da ake ci gaba da gwabza fada tsakanin sojoji da dakarun kai daukin gaggawa na Rapid Support Forces (RSF), a cikin sarkakkiyar yanayin jin kai da na siyasa da kuma fadadan rikici a jihohi daban-daban.

Fadace-fadace a Sudan suna ci gaba da karuwa, inda ake ci gaba da gwabza fada tsakanin sojoji da mayakan kungiyar Rapid Support Forces, inda sojojin saman Sudan suka zafafa kai hare-hare ta sama ta hanyar amfani da jiragen sama marasa matuka ciki, kuma suka yi luguden wuta kan wasu muhimman wurare na kungiyar Rapid Support Forces a jihar Kordofan ta Arewa.

Hare-haren sun fi tsanani ne a yankin Kilo Zero dake arewacin Bara da Ummu Sayala, tare da lalata motocin soji da kayayyakin aiki, baya ga hasarar dimbin dakarun kungiyar Rapid Support Forces, kamar yadda majiyoyi da dama suka tabbatar da nasarar sojojin Sudan kan ‘yan tawaye.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wani mutum ya mutu a cikin rijiya a Kano
  • Farfesa Jibril Amin Tsoho Ministan Ilim Da, Manfetur A Najeriya Rasu Yana Dan Shekara 85 A Duniya
  • Mahajjata Aikin Hajjin Bana Sun Tafi Tsayiwar Arafat A Yau Alhamis Don Fara Ginshikin Aikin Hajj
  • Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa
  • Maniyyata na hawan Arfa a kasar Saudiyya
  • ROOSC Ta Kaddamar Da Rabon Kayan Koyon Karatu A Kaduna
  • Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 
  • Rikici Yana Ci Gaba Da Gudanar A Kasar Sudan Tsakanin Sojoji Da Dakarun Kai Daukin Gaggawa
  • Wata hajiyar Najeriya daga Filato ta rasu a Makkah