Aminiya:
2025-11-02@19:46:01 GMT

’Yan sanda sun sake hana hawan Sallah a Kano

Published: 4th, June 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sanda ta Jihar Kano ta sake haramta duk wani nau’i na hawan Sallah a yayin bukukuwan Babbar Sallar da ke tafe.

A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar a jihar, Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar a ranar Talata, ya ce har yanzu haramcin da rundunar ta fitar na nan daram kuma za su tabbatar da an yi aiki da shi a yayin bukukuwan Babbar Sallah ta 2025.

Ya ce sun dauki matakin ne bayan wani zama da ilahirin shugabannin hukumomin tsaro a jihar suka yi, inda ya ce sun gano wani yunkuyi da aka yi wajen yin amfani da hawan wajen yi wa harkokin tsaron jihar zagon kasa, kamar yadda aka samu yayin Karamar Sallar da ta gabata.

Hatsarin kwale-kwale ya yi ajalin mutum 7 a Sakkwato Babbar Sallah: Farashin kayan miya ya yi tashin gwauron zabo

Sanarwar ta ce, “’Yan sanda suna ba mutane shawara da su bi dukkan dokokin da aka kafa a lokacin bukukuwan.

“Daga cikin dokokin shi ne su kaurace wa hawa doki ko ma kowacce irin dabba da sunan kilisa ko tseren mota ko tukin ganganci ko rike makami.

“Kazalika, an haramta amfani da makami ko kuma duk wani abu da zai iya razanar da jama’a, yayin da ake kiran al’umma da su ja kunnen ’ya’yansu su kauce wa karya doka.

“’Yan sanda da suran jami’an tsaro a shirye suke su tabbatar da an bi wannan doka tare da hukunta wadanda suka karya ta,” in ji sanarwar.

Sai dai umarnin na zuwa ne kasa da kwana biyu bayan Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II ya umarci Hakimai da su shiga cikin birnin Kano domin fara shirye-shiryen hawan Sallar.

Umarnin wanda ke kunshe a cikin wata wasika da masarautar ta aike wa Hakiman, ta umarce su da su taho tare da dawakai da mahayansu.

Wasikar dai na dauke da sa hannun Sakataren masarautar kuma Dan Makwayon Kano, Alhaji Abba Yusuf dauke da kwanan watan 30 ga watan Mayun 2025.

Idan za a iya tunawa, ko da Karamar Sallar da ta gabata, Sarkin na Kano ya gudanar da hawan duk kuwa da sanarwar ’yan sandan ta hana shi, lamarin da ya sa hedkwatarsu ta kasa ta gayyace shi, kafin daga bisani ta janye gayyatar bayan abin da ta kira sanya bakin wasu masu fada a ji.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Hawan Sallah

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda

Daga Usman Muhammad Zaria

 

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta yi kira ga mazauna jihar Jigawa da su kasance masu bin doka da oda, tare da yin aiki kafada da kafada da rundunar ‘yan sanda domin tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali a fadin jihar.

Kwamishinan ‘Yan Sanda na jihar Jigawa, CP Dahiru Muhammad, ne ya bayyana haka lokacin da ya karɓi sabbin motoci 10 kirar Toyota Hilux da Gwamna Umar Namadi ya bai wa rundunar a Dutse, babban birnin jihar.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, SP Lawan Shiisu Adam, ya fitar, CP Dahiru Muhammad ya yaba da jajircewar Gwamna Umar Namadi wajen tallafa wa hukumomin tsaro domin sauke nauyin da ke kansu a jihar.

Ya bayyana cewa, wannan gudummawa ta nuna cikakken kudirin gwamnatin Gwamna Namadi na ƙara inganta harkokin tsaro da kuma tallafawa Rundunar ‘Yan Sanda ta Najeriya wajen aiwatar da aikinta na kare rayuka da dukiyoyin jama’a a fadin jihar.

Kwamishinan ya nuna cewa, waɗannan sabbin motoci 10 za su taimaka matuƙa wajen rage lokacin da ake ɗauka kafin amsa kiran gaggawa, tare da ƙara inganta aikin rundunar a fadin jihar.

Ya ƙara da cewa, za a yi amfani da motocin yadda ya kamata, tare da kula da su don tabbatar da ingantaccen  tsaro.

CP Dahiru Muhammad ya kuma sake jaddada aniyar rundunar wajen ci gaba da tabbatar da zaman lafiya, doka da oda, tare da ƙarfafa haɗin gwiwa da sauran hukumomin tsaro da masu ruwa da tsaki.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna
  • Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • ‘An Kashe Masu Zanga-zanga Akalla 500 a Tanzania’
  • Najeriya ta musanta ikirarin Trump, na cewa Kristoci na fuskantar babbar barazana a kasar
  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • Gwamnatin Tarayya Da Stellar Steel, Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Habaka Karafan Cikin Gida
  • Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa
  • An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkuku
  • Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aure