Aminiya:
2025-06-06@01:02:38 GMT

’Yan sanda sun sake hana hawan Sallah a Kano

Published: 4th, June 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sanda ta Jihar Kano ta sake haramta duk wani nau’i na hawan Sallah a yayin bukukuwan Babbar Sallar da ke tafe.

A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar a jihar, Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar a ranar Talata, ya ce har yanzu haramcin da rundunar ta fitar na nan daram kuma za su tabbatar da an yi aiki da shi a yayin bukukuwan Babbar Sallah ta 2025.

Ya ce sun dauki matakin ne bayan wani zama da ilahirin shugabannin hukumomin tsaro a jihar suka yi, inda ya ce sun gano wani yunkuyi da aka yi wajen yin amfani da hawan wajen yi wa harkokin tsaron jihar zagon kasa, kamar yadda aka samu yayin Karamar Sallar da ta gabata.

Hatsarin kwale-kwale ya yi ajalin mutum 7 a Sakkwato Babbar Sallah: Farashin kayan miya ya yi tashin gwauron zabo

Sanarwar ta ce, “’Yan sanda suna ba mutane shawara da su bi dukkan dokokin da aka kafa a lokacin bukukuwan.

“Daga cikin dokokin shi ne su kaurace wa hawa doki ko ma kowacce irin dabba da sunan kilisa ko tseren mota ko tukin ganganci ko rike makami.

“Kazalika, an haramta amfani da makami ko kuma duk wani abu da zai iya razanar da jama’a, yayin da ake kiran al’umma da su ja kunnen ’ya’yansu su kauce wa karya doka.

“’Yan sanda da suran jami’an tsaro a shirye suke su tabbatar da an bi wannan doka tare da hukunta wadanda suka karya ta,” in ji sanarwar.

Sai dai umarnin na zuwa ne kasa da kwana biyu bayan Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II ya umarci Hakimai da su shiga cikin birnin Kano domin fara shirye-shiryen hawan Sallar.

Umarnin wanda ke kunshe a cikin wata wasika da masarautar ta aike wa Hakiman, ta umarce su da su taho tare da dawakai da mahayansu.

Wasikar dai na dauke da sa hannun Sakataren masarautar kuma Dan Makwayon Kano, Alhaji Abba Yusuf dauke da kwanan watan 30 ga watan Mayun 2025.

Idan za a iya tunawa, ko da Karamar Sallar da ta gabata, Sarkin na Kano ya gudanar da hawan duk kuwa da sanarwar ’yan sandan ta hana shi, lamarin da ya sa hedkwatarsu ta kasa ta gayyace shi, kafin daga bisani ta janye gayyatar bayan abin da ta kira sanya bakin wasu masu fada a ji.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Hawan Sallah

এছাড়াও পড়ুন:

Wani mutum ya mutu a cikin rijiya a Kano

Wani matashi dan shekara 33 mai suna Muhammad ​​Sagir ya rasa ransa bayan ya fada rijiya a unguwar Kawon Alhaji Sani da ke karamar hukumar Nasarawa a Jihar Kano.

A cewar jami’in hulda da jama’a na hukumar kashe gobara ta Jihar Kano, mataimakin jami’in kashe gobara (ACFO) Saminu Yusif Abdullahi, ya ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 12:42 na rana a ranar Laraba, 4 ga watan Yuni, 2025.

Tsohon Ministan Ilimi, Farfesa Jibril Aminu, ya rasu

Ya ce hukumar kashe gobara ta samu kiran gaggawa daga wani mai suna Sabi’u Muhammed, inda ya sanar da su lamarin.

“Nan da nan aka tattara tawagar ceto daga hedkwatar hukumar zuwa wurin.”

“Da isowar jami’an, ma’aikatan sun gano wani mutum guda mai suna Muhammad ​​Sagir mai kimanin shekaru 33, wanda ya fada cikin busasshiyar rijiya, an ceto shi a sume kuma daga bisani aka tabbatar da mutuwarsa,” in ji shi.

Daga nan ne aka mika gawar marigayin ga hakimin Kawon Arewa, Alhaji Hamisu.

Hukumar kashe gobara ta jihar ta nanata kudurinta na daukar matakan gaggawa, sannan ta bukaci mazauna yankin da su tabbatar da killace budaddun rijiyoyi da makamantansu domin hana afkuwar ibtila’i a nan gaba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Bukukuwan sallah tare da Malta Guinness a Birnin Kano
  • Wani mutum ya mutu a cikin rijiya a Kano
  • Trump Ya Umarci A Bincika Lafiyar Ƙwaƙwalwar Tsohon Shugaban Ƙasa Biden Yayin Mulkinsa
  • Sallah: Mun shirya samar da tsaro a Yobe — ’Yan Sanda
  • Rundunar ‘Yan Sanda A Kano Ta Haramta Bukukuwan Hawan Sallah A Kano
  • ‘Yansanda A Kano Sun Gargaɗi Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah
  • ‘Yansanda A Kano Sun Gargadi Sarki Sanusi Kan Yekuwar Fitowa Hawan Sallah
  • Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 
  • Gwamnn Zamfara Ya Ba Ma’aikata Da ‘Yan Fansho Barka Da Sallah