Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ya Jaddada Hakkin Iran Na Tace Sinadarin Uranium
Published: 4th, June 2025 GMT
Jagoran juyin juya halin Musulunci ya bayyana cewa: Inganta sinadarin Uranium shi ne mabuɗin batun nukiliya, don haka Iran ba zata taba yin watsi da shi ba
A jawabin da ya gabatar a safiyar yau Laraba, a daidai lokacin da ake cika shekaru 36 da wafatin jagoran juyin juya halin Musulunci Imam Khumaini (Allah ya jikansa), Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei, a matsayin martani ga shawarar Amurka, ya jaddada cewa inganta sinadarin Uranium shi ne mabudin batun nukiliya, kuma ba za su taba yin watsi da shi ba.
A wajen wannan juyayi, bayan karatun kur’ani mai tsarki da yabon Ahlul-baiti (a.s) jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya gabatar da jawabinsa inda ya ce: Kafin ya ce komai, yana mika jinjinarsa ga ruhin Imam mai girma da kuma rokon Allah Madaukakin Sarki da ya daukaka darajarsa.
Jagoran ya kara da cewa: Gobe ne ranar Arafah, kuma mabudin Sallah, don haka yana nasiha ga matasa da yin sallah, su bayyana bukatunsu da manufofinsu ga Allah Madaukakin Sarki, tare da neman taimakonsa.
Ayatullah Khamenei ya ci gaba da cewa: Tsarin siyasarsu wanda alhamdulillahi ya samu ci gaba da karfafa shi ne sakamakon juyin juya hali mai girma, kuma jagoransu mutum ne mai girma wanda har yanzu ake jin kasancewarsa a duniya sama da shekaru talatin bayan wafatinsa, kuma har yanzu tasirin juyin juya halinsa a bayyane yake ga al’ummar duniya, kuma irin koma bayan da Amurka take da samu a duniya yana da nasaba da samuwarsa da kuma kiyayya da juyin juya halinsa.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Jagoran juyin juya halin Musulunci
এছাড়াও পড়ুন:
Jami’an Tsaron A Nan Iran Sun Kama Yan Kungiyar ISIS Kafin Su Aiwatar Da Hare-Hare
Jami’an Yansanda masu kula da ayyukan ta’addanci da kuma hana aukuwarsu a nan Iran sun sami nasarar kama wasu yan kungiyar ISIS 13 a duk fadin kasar daga ciki har da shugabansu.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Brigadier General Saeed Montazer al-Mahdi kakakin rundunar FARAJA mai kula da fada da yan ta’adda yana fadar haka. Ya kuma kara da cewa yan ta’addan su 13 daga cikin har da shugabansu, sun kuduri anniyar kai hare-hare a cikin Jama’a su kuma kashe mutane a wasu tarurrukan da aka gudanar a kasar nan.
Labarin ya kara da cewa an kama yan ta’addan na ISIS a biranen Tehran, Qum, Esfahan da kuma Albus. Kuma an kama tare da su kayakin aiki wadanda suka hada da damarar boma bomai na kunan bakin waje da kuma jakunan da ake ratayawa a baya cike da abubuwan Facewa. Kakakin rundunar FARAJA y ace suna dauke da karin bayani nan gaba.